ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bikin Baje Kolin CIIE: Kasashen Afirka Kar Ku Yarda A Bar Ku A Baya

by Abdulrazaq Yahuza
3 years ago
CIIE

Bikin baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin na duniya (CIIE) ya nuna kudurin kasar Sin na hada kan duniya domin cin gajiyar juna ta fuskar tattalin arziki har ma da zamantakewa.

A karon farko da na samu labarin bikin, na yi tunanin akwai yiwuwar za a bar ’yan kasuwarmu na Afirka da dama a baya wurin shiga a dama da su, saboda rashin karfin jari irin na takwarorinsu na sauran duniya.

  • Xi Zai Gana Da Biden Tare Da Halartar Taron Shugabannin Tattalin Arzikin APEC
  • Sin Na Taka Rawar Gani Wajen Tabbatar Da Zaman Lafiya A Gabas Ta Tsakiya

Amma bisa bayanan da na ji daga cibiyar baje kolin, a ziyararmu ta aiki a 2018 a Shanghai, shugabannin shiryawa sun ce, baje kolin na CIIE ya tsara taimakawa kasashe masu rauni wajen ba su matsugunai domin baje kolinsu ba tare da biyan kudi ba har ma da wani tallafi da zai taimaka wa kayayyakinsu su samu damar shiga kasuwar kasar Sin.

ADVERTISEMENT

Wannan tsari ya haifar da da mai ido, domin ko a bana, daga kasar Zimbabwe kawai, fiye da kamfanoni da kungiyoyi 15 da suka kware a fannin fasahar zane, da sarrafa kayayyakin fata, da harkokin sadarwa, da kuma sayar da ma’adanai, suke halartar bikin baje kolin.

Haka nan daga Nijeriya da Afirka ta Kudu da sauran kasashe duk suna can ana damawa da su a bikin baje kolin na bana karo na 6 a birnin Shanghai.

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Baje kolin na CIIE, karin dama ce ga Nijeriya ta samun cinikin kayan da take fitarwa zuwa Sin kamar su kwarar manja, ridi, ‘ya’yan itace, hatsi har ma da waken soya wanda cinikayyarsu sun kai Dalar Amurka miliyan 140.88 a shekarar 2021, bisa bayanan cibiyar cinikayya ta COMTRADE ta Majalisar Dinkin Duniya.

Shugaban Tsangayar Aikin Gona da Raya Karkara ta ARMTI da ke Nijeriya, Dr. Olufemi Oladunni, ya bayyana cewa, “akwai damammaki da yawa da manoman Nijeriya za su ci gajiya a kasuwanni na kasashen duniya bisa cudanya da ‘yan kasuwa na waje, manoman za su samu dabarun inganta noma, da yadda za su rika sarrafa amfanin gona bayan girbi da kuma fitarwa waje.”
Har ila yau, manajan daraktar kamfanin sarrafa kayan fata na Samuneti dake Zimbabwe, Tsitsi Chirova, ta ce baje kolin CIIE fage ne da suke samun damar fadada hadin gwiwa da kara fahimtar ire-iren kayayyakin da za su rika sarrafawa. “Daga shigar da muka yi a baya, mun sami damar habaka tallace-tallacenmu, da kuma samun shawarwari daga abokan cinikinmu don habaka abubuwan da muke samarwa. Don haka idan muka halarci bikin baje kolin na kasar Sin, na yi imani hakan zai tallata kamfaninmu da gaske, kuma bayan mun dawo gida, mun yi imanin za mu samu karin kwastomomi,” in ji ta.

Shi ma wani mai sassaka dake birnin Harare, Richard Mudinzva, da ya sha alwashin halartar bikin karo na 6, ya ce, akwai abokan ciniki da yawa a kasuwar kasar Sin dake sha’awar kayayyakin Afirka. Alkaluman da ofishin jakadancin kasar Sin dake Zimbabwe ya fitar sun nuna cewa, cinikayyar bangarorin biyu ta karu da kashi 39.4 bisa dari, zuwa dala biliyan 2.43 daga Janairu zuwa Satumbar 2023, wanda ya zarce adadin cinikin da aka samu a shekarar 2022.

Kasar Guinea-Bissau, mafi noman kashu a duniya, ta ci gajiyar bikin baje kolin a bara, yayin da aka ware mata matsugunin kamfanoninta suka baje kolinsu na kashu. Kamar yadda jakadan kasar a Sin, Antonio Serifo Embalo ya bayyana, sakamakon halartar bikin baje kolin na bara, ’yan kasuwa da dama sun nuna muradinsu a kan bangaren kashu na kasar. Wasu ma tuni har sun tsara yadda za su zuba jari a kasar.
A nashi bangaren, mataimakin shugaban Afirka ta Kudu, Paul Mashatile, ya yaba wa kasar Sin bisa yadda take kara bude kofofinta na kasuwanci musamman ga kasashen Afirka. Yana mai cewar, bikin baje kolin ya kara fadada dama ga kamfanoni na duniya wajen bunkasa hulda da abokan ciniki.

Sama da kamfanoni 1,500 daga kasashen dake cikin shawarar “ziri daya da hanya daya” ke baje kolin hajojinsu a bikin karo na shida.

Ana sa rai, cinikayyar shigo da kaya na kasar Sin su zarce dala tiriliyan 17 nan da shekara 5 masu zuwa, don haka nake cewa, kasashen Afirka kar ku yarda a bar ku a baya wajen cin gajiyar hakan.

CIIE
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Taj

Bankin TAJ Ya Sake Lashe Kyautar Gwarzon Bankin Musulunci Na Bana

LABARAI MASU NASABA

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.