• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bikin Baje Kolin Cinikayya Ta Zama Dandalin Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Bikin Baje Kolin Cinikayya Ta Zama Dandalin Karfafa Hadin Gwiwar Sin Da Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sakamakon kudirin da kasar Sin da Afirka suke da shi na yin aiki tare domin cin gajiyar juna da kuma hobbasar da Sin ke yi na tabbatar da al’umma mai kyakkyawar makoma ta bai daya a duniya, a wannan makon ne aka bude bikin baje kolin tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Afirka karo na uku, daga ranar 29 ga watan Yuni zuwa ranar 2 ga watan Yuli a birnin Changsha na lardin Hunan da ke tsakiyar kasar Sin. 

Baje kolin wanda aka fara a shekarar 2019, ya kasance wani muhimmin dandali na inganta hadin gwiwar kasuwanci da tattalin arziki tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka. Shekaru 14 ke nan a jere, kasar Sin tana zama babbar abokiyar kasuwanci a Afirka, bayan da ta doke Amurka a wannan fannin a shekarar 2009. Kawancen cinikayya da tattalin arzikin ba wai kawai ya zurfafa ba ne, har ma ya kara samun tagomashi tare da cin gajiyar abin a tsakanin Sin da Afirka.

  • Sin Ta Yi Kira Da A Samar Da Yanayin Shawo Kan Rikicin Ukraine Baki Daya

Adadin cinikayya a tsakanin Sin da Afirka ya kai Dala biliyan 282 a shekarar 2022, inda ya ninka wanda yake tsakanin Amurka da Afirka a shekarar har sau hudu. A cikin shekaru 10 da suka wuce, kasar Sin ta kasance kan gaba a matsayin kasar da ta fi zuba jari a Nahiyar Afirka, inda ta kara habaka tattalin arzikin nahiyar da kashi 20 cikin dari. A cikin rubu’in farko na shekarar 2023, sabon jarin da kasar Sin ta zuba kai-tsaye a Afirka ya bunkasa da kashi 24 bisa dari a shekarar da ta gabata, inda ya kai na Dala biliyan 1.38.

Hadin gwiwar kasuwanci da tattalin arziki yana daya daga cikin hanyoyi mafi dacewa na kawar da talauci da rashin ci gaba. Dangane da hakan, tun bayan kafuwar dandalin tattaunawar hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka (FOCAC) a shekarar 2000, shugabannin Sin da Afirka, suke ba da fifiko wajen daidaita tattalin arzikin duniya a matsayin wata manuniya ko babbar alama ta hadin gwiwarsu. Haka nan an shigar da tsarin cikin shirye-shirye da manufofi daban-daban ciki har da na Ziri Daya Da Hanya Daya (BRI).

Manufar bude kofar kasuwanci ta kasar Sin ta shawo kan yadda kayayyakin Afirka ke tabarbarewa a kasuwannin kasar. Kasar Kenya ta zama kasa ta farko a nahiyar Afirka da ta fitar da danyen kayan marmari na avocado zuwa kasuwannin kasar Sin. A cikin watanni uku, tsakanin Maris da Mayun 2023, ta fitar da kayan marmarin zuwa kasar Sin da ya kai na Dala miliyan 64.38, wanda ya amfanar da dubban kananan manoma. A yau, kasashe 21 na Afirka suna cin moriyar yafe musu biyan haraji na kashi 98 bisa dari na kayayyakin da suke fitarwa zuwa kasuwannin kasar Sin.

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Akwai abubuwa masu yawa da ke kara habaka hadin gwiwar kasuwanci tsakanin Sin da Afirka. Alakar da Sin ke yi da kasashen Afirka, na mayar da hankali ne da ba da fifiko kan hadin gwiwar tattalin arziki da gudanar da harkokin kasuwanci. Wannan ya sha bamban sosai da tsarin da Amurka ta dauka na hulda da nahiyar da ke katsalandan gare su da sunan “dimokuradiyya,” “sha’anin mulki,” da “`yancin Dan adam.”

Har ila yau, huldar kasuwanci da ke tsakanin kasar Sin da Afirka ta ginu ne bisa la’akari da abubuwa na bukatu da samar da wadata kawai. Hakazalika, masu zuba jari na kasar Sin suna kallon Afirka a matsayin wurin samun damammaki. A daya bangare kuma, kasashen yammacin duniya da masu zuba jarinsu su kan yi wa Afirka kallon wani yanki na yi wa kawunansu garkuwar tsaro sannan akwai karancin harkokin tattalin arziki. Misali jarin da Washington ta zuba kai tsaye a Afirka ya ragu daga Dala biliyan 69 a shekarar 2014 zuwa Dala biliyan 47.5 a shekarar 2020.

Sakamakon kudurorin taron ministoci karo na 8 na FOCAC a shekarar 2021, Sin da Afirka suna da damar amfani da bikin baje kolin, da zurfafa hadin gwiwa a fannonin da suka fi ba da fifiko kamar kiwon lafiya, rage fatara, aikin gona da samar da abinci, inganta kasuwanci, zuba jari, kirkire-kirkire na zamani da bunkasa kyawon muhalli.

Bikin baje kolin na Changsha na zuwa ne a wani muhimmin lokaci ga Sin da Afirka. Shi ya sa bangarorin biyu ke aiki tukuru domin kawar da tasirin da annobar COVID-19 ta yi. Afirka na aiwatar da kyakkyawan tsarin ciniki cikin ‘yanci na nahiyar (AfCFTA) wanda ya hada hada-hadar kasuwanci na mutane biliyan 1.4 tare da jimillar kudin kayayyakin cikin gida(GDP) da ya haura Dala triliyan 3.7.

A lokaci guda kuma, kasar Sin tana kara sa kaimi wajen bunkasa tattalin arzikin duniya ta hanyar habaka hada-hadar kayayyaki, karfafa jari, fasahohi da ka’idojin gudanarwa mafi dacewa. Matukar babu kakkarfan kawancen kasar Sin, yunkurin Afirka na bunkasa masana’antu zai iya zama a mafarki kawai. Hakazalika, Afirka ba tana bai wa kasar Sin damar kasuwancin kayan masana’antunta ne ba kawai, har ma da sararin zuba jari mai dorewa tare da dimbin albarkatun kasa da ake bukata domin sarrafawa a masana’antu na zamani.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Sakkwato Ta Fara Biyan Alawus Din Masu Bukata Ta Musamman

Next Post

Ban Yi Nadamar Rusau A Kano Ba -Gwamnan Kano

Related

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

8 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

9 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

11 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

12 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

19 hours ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

21 hours ago
Next Post
Ban Yi Nadamar Rusau A Kano Ba -Gwamnan Kano

Ban Yi Nadamar Rusau A Kano Ba -Gwamnan Kano

LABARAI MASU NASABA

An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.