ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bikin Kafuwar Daular Saudiyya Shekara 93: Abubuwan Da Suka Kamata A Sani

by Sulaiman
2 years ago
Saudiyya

Ofishin Jakadancin Kasar Saudiyya da ke Abuja ya gudanar da bikin cikar ranar kasa ta Saudiyya karo 93 a gidan Ambasadanta da ke Abuja, wanda ya samu halartar jami’an gwamnati da shugabannin ofisoshin diflomasiyya da kungiyoyin kasa da kasa da kuma ‘yan kasuwa da sauran manyan mutane.

A nasa jawabin, Jakadan kasar Saudiyya a Nijeriya H.E. Faisal bin Ebraheem Alghamdi ya bayyana cewa, Masarautar tana bikin cika shekaru 93 na hadin kan sassan Masarautar Sarki Abdulaziz bin Abdulrahman Al Saud (Allah Ya jikansa) a karkashin wata kungiya mai karfi wacce aka kafa ta bisa akidar Musulunci wacce daidaito, adalci da amana suka tabbata acikinta.

  • Gwamnatin Kaduna Ta Nemi Saudiyya Ta Zuba Jari A Jiharta
  • Saudiyya Ta Kebe Wa Nijeriya Kujeru 95,000 A Aikin Hajji Na 2024

Alghamdi ya kuma bayyana cewa, akwai kyakkyawar alaka a tsakanin Masarautar da Nijeriya mai cike da tarihi wacce ta ke ta ci gaba da bunkasa tun lokacin da aka kulla huldar jakadanci tsakanin kasashen biyu a shekarar 1961. Ya kuma yi fatan alheri da nasara ga mai girma shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu.

ADVERTISEMENT

Yayin da yake tsokaci kan kyakkyawar alakar da ke tsakanin kasashen biyu, jakadan ya ce, sama da mahajjata ‘yan Nijeriya 200,000 da masu zuwa karamin aikin hajji (Umara) da maziyarta sun ziyarci Masarautar a shekarar da ta gabata, kuma Masarautar ta baiwa daliban Nijeriya tallafin karatu sama da 200 don yin karatu a jami’o’in kasar daban-daban. Ya kara da cewa, yawan cinikin da ke tsakanin kasashen biyu ya haura dala miliyan 600.

Saudiyya

LABARAI MASU NASABA

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

Akan taimakon jin kai ga al’ummar Nijeriya. Jakadan Masarautar ya bayyana cewa, Sarki Salman bin Abdulaziz Al Saud (Allah Ya kare shi) ya ba da umarnin aiwatar da taimakon sa-kai na Nur-Saudi a Nijeriya, wanda aka fara aiwatarwa mataki-mataki; An aiwatar da matakin farko wanda aka nufi yakar makanta da musabbabanta, sannan kuma ta yi wasu ayyukan tiyata musamman a bangaren mafitsara da raba tagwayen da aka haifa a Jone.

Jakadan ya taya iyayen tagwayen murna da aka yi nasarar raba su a watan Mayun da ya gabata, a aikin tiyata mai lamba 56 da masarautar ta yi wajen raba wasu tagwaye daga sassan duniya.

Saudiyya
A karshe, jakadan ya mika godiya ga kasashen duniya da abokan arziki daga ciki har da tarayyar Nijeriya bisa goyon bayan da ta baiwa Saudiyya na karbar bakuncin bikin baje kolin duniya na 2030 a birnin Riyadh, wanda ya zo daidai da ranar da Saudiyya ta ke shirin kaddamar da kudirinta na shekarar 2030.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?
Nazari

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC
Manyan Labarai

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
Next Post
Bayan Shekaru 9, Har Yanzu Yana Tuna Ni

Bayan Shekaru 9, Har Yanzu Yana Tuna Ni

LABARAI MASU NASABA

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025
Kwankwaso

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Gina Sabbin Ginshikan Samar Da Ci Gaban Kasa Masu Inganci

November 15, 2025
Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

Duk Niyyar Da Mutum Ya Shigo Da Ita Kannywood Ita Za Ta Bi Shi —HAUWA KUJAMA

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.