• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bikin Ranar Majalisar Dinkin Duniya: Muna Fuskantar Kalubalen Da Ba A Taba Ganin Irinsa Ba – Schmale

Ya Nemi Kasashe Su Kara Sadaukarwa Domin Zaman Lafiyar Duniya

byyahuzajere
2 years ago
majalisa

Babban Jami’in Majalisar Ɗinkin Duniya a Nijeriya, Mista Matthias Schmale, ya bayyana cewa kudirin da ya sa aka kafa Maja;lisar Dinkin Duniya na fuskantar kalubalen da ba a taba ganin irinsa ba saboda yadda yaki ke ci gaba da gudana a sassan duniya.

Ya bayyana haka ne lokacin da yake jawabi game da ranar Majalisar Dinkin Duniya, wanda ake gudanarwa kowace shekara don tunawa da muhimmiyar ranar da Yarjejeniyar Kafa Majalisar Dinkin Duniya ta fara aiki, 24 ga Oktoba,1945.

A jawabin nasa wanda Jami’ar yada labarai bangaren Hausa na Ofishin Bayar da Bayanai na MDD da ke Abuja, Maryam Rabi’u ta raba wa manema labarai a yau Talata, babban jami’in ya yi tsokaci a kan ka’idoji da ayyukan Majalisar Dinkin Duniya da kuma kalubalen da duniya ke fuskanta a yau.

Mr. Schmale ya fara ne da tabo batun yadda aka bude taron Yarjejeniyar Kafa Majalisar Dinkin Duniya, wanda ya jaddada cewa babban kudirin kafa hukumar shi ne “ceto al’ummar duniya daga bala’in yaki.”

A bikin na bana, ya bayyana cewa, wannan kudiri na fuskantar kalubalen da ba a taba ganin irinsa ba, inda tashe-tashen hankula suka shafi miliyoyin mutane a wurare kamar Ukraine, Falasdinu, Isra’ila, Sudan da Myanmar, da kuma korar shugaban Nijar da aka yi a kwanan baya.

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

  • Nijeriya Ta Yi Nasara A Kotun Ingila Kan Rikicinta Da Kamfanin P&ID
  • An Kwato Bindiga AK47 Guda 150 A Minna Bayan Artabu

Babban Jami’in ya bukaci kasashen kungiyar su sake jaddada sadaukarwarsu da girmama Yarjejeniyar ta Majalisar Dinkin Duniya, da kuma sabunta kokarinsu na inganta zaman lafiya, yana mai bayyana cewa, wannan shi ne muhimmin sakon Babban Sakataren MDD Antonio Guterres a bana.

Ya kuma yaba wa ma’aikatan Majalisar Dinkin Duniya a Nijeriya, wadanda suke aiki ba tare da gajiya ba, a lokuta da dama a cikin mawuyacin hali, domin cika burin Majalisar Dinkin Duniya na samar da zaman lafiya da wadata ga kowa da kowa.

Ya kuma tuna tare da bayyana alhini kan ma’aikatan Majalisar Dinkin Duniya guda 23 da suka rasa rayukansu a harin ta’addancin da aka kai a ofishin MDD da ke Abuja a shekarar 2011 da kuma abokan aikinsu da ke ci gaba da sadaukarwa a yanayi na tashe-tashen hankula.

Mr. Schmale ya kuma bayyana kudira MDD kan cimma ajandar 2030 da kuma manufofin ci gaban zamani masu dorewa (SDGs), tare da jaddada ka’idar kowa ya bayar da gudunmawa a dama da shi ba tare da barin kowa a baya ba. Ya yi alkawarin mayar da hankali wajen magance matsalolin da suka shafi yara da ba su zuwa makaranta, rashin abinci mai gina jiki, cin zarafin mata da ‘yan mata, da bukatun al’umma masu rauni da suka hada da tsofaffi, nakasassu, da ‘yan gudun hijira.

Har ila yau, ya yi kira ga shugabannin gwamnati da su hanzarta aiwatar da ajandar 2030 sannan ya yi magana game da dimbin damar da Nijeriya ke da ita ta bunkasa da ciyar da kanta gaba, yana mai jaddada bukatar mayar da hankali wajen aiwatar da lamarin bilhakki.

Taken bikin ranar Majalisar Dinkin Duniya na bana, “Hadin gwiwar Majalisar Dinkin Duniya tare da Nijeriya don Cimma Tsarin SDGs,” ya mayar da hankali ne a kan bayyana mahimmancin haɗin gwiwa da sauke nauyin da ke wuyar juna.

Babban Jami’in ya jaddada kokarin da majalisar ke yi na kara samun kayan aiki don magance matsalolin kiwon lafiya kamar cuta mai karya garkuwar jiki (AIDS), da tarin fuka, da zazzabin cizon sauro, da kuma tallafa wa samar da zaman lafiya, magance rikice-rikice, da inganta hanyoyin sa ido ga rundunar ‘yan sandan Nijeriya.

Bugu da kari, ya amince da ayyukan jin kai a jihohin Borno, Adamawa, da Yobe, inda aka bayar da agajin gaggawa ga marasa galihu miliyan 3.6 a farkon rabin shekarar nan.

Mr. Schmale ya kuma tunatar da kowa da kowa cewa dole ne dukkanin ayyukan ci gaba su kasance daga tushe a cikin mutunta hakkin Dan’adam, bayar da shawarar ‘yancin fadin albarkacin baki, da kuma dakile kalaman batanci da kiyayya.

Mr Schmale ya kammala jawabinsa da neman hadin kai da hadin gwiwa tsakanin gwamnati, kungiyoyin fararen hula, bangarori masu zaman kansu, da kafafen yada labarai wajen tabbatar da akidu da ganin kimar Majalisar Dinkin Duniya don ci gaban mutanen duniya da samun wadata, da zaman lafiya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Next Post
Kasar Sin Ta Harba Sabon Tauraron Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

Kasar Sin Ta Harba Sabon Tauraron Dan Adam Da Ake Iya Sarrafawa Daga Nesa

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version