Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta kama mutane shida tare da rufe wasu shaguna a kasuwar Sabon Gari da ke Kano, saboda sayar da man da ake koɗar da fata ba bisa ƙa’ida ba.
Shugaban hukumar na Jihar Kano, Kasim Ibrahim, ya shaida wa manema labarai a ranar Talata cewa an ɗauki wannan mataki ne bayan samun ƙorafe-ƙorafe daga jama’a ta kafafen sada zumunta, tare da umarnin kai-tsaye daga shugabar hukumar ta ƙasa.
- Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?
- Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato
“Bayan samun ƙorafe-ƙorafe daga mutane ta kafafen sada zumunta, muka fara bincike a ɓoye tare da sayen kayan a asirce domin duba sahihancinsu,” in ji Ibrahim.
Ya bayyana cewa binciken ya gano wasu mutane guda shida da ke da hannu wajen rabawa da amfani da waɗannan mayuka ba tare da izini ba.
“Waɗannan kayayyaki sun kasance kamar kayan gyaran fata a wuraren kwalliya, amma suna ɗauke da sinadarai masu haɗari waɗanda ba a amince da su ba,” in ji shi.
Haɗin gwiwar NAFDAC da sashen bincike da aiwatar da dokokinta ne ya kai ga kama waɗanda ake zargi tare da rufe shagunan da suka shafa, da ɗaukar samfurin mayukan domin gwaji a ɗakin bincike.
Haka kuma, an rufe wasu kamfanonin da ke kwaikwayon kayayyakin da aka yi wa rijista ko suke karya ƙa’idodin NAFDAC, har sai an kammala bincike.
Ibrahim ya roƙi jama’a da su kasance masu lura da duk wani abu da ya saɓa wa doka kuma su riƙa sanar da hukumar nan take.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp