• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Binciken CGTN: Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kasa Da Kasa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Amurka Kan Iran

by CGTN Hausa and Sulaiman
4 months ago
Amurka

Matakin kasar Amurka na amfani da jiragen yakinta samfurin “B-2 Spirit stealth”, wajen jefa bama-bamai kan cibiyoyin sarrafa sinadaran nukiliyar kasar Iran, karkashin shirin da aka yiwa lakabi da “Midnight Hammer”, ya kara ta’azzara halin da ake ciki a yankin Gabas ta Tsakiya. 

Bayan da a fakaice Amurka ta nuna goyon bayanta ga hare-haren Isra’ila, sai kuma ta shiga kaddamar da hare-hare kai tsaye. Game da hakan, kuri’ar jin ra’ayin jama’a da kafar CGTN ta kasar Sin ta shirya, ta fayyace yadda akasarin masu bayyana ra’ayoyi suka soki lamirin Amurka bisa hare-haren da ta aiwatar kan Iran, tare da sukar manufar kasar ta diflomasiyyar waje mai lakabin “Amurka gaban komai”, wadda a cewarsu ta haifar da mummunar ta’asa marar iyaka a Gabas ta Tsakiya.

  • Sin Na Fatan Kwamitin Sulhun MDD Zai Goyi Bayan Kuduri Game Da Halin Da Iran Ke Ciki
  • Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano

Sakamakon jin ra’ayin jama’ar ya nuna cewa, kaso 91 bisa dari na masu bayyana mahangarsu, na ganin yayin da sassan kasa da kasa ke tsaka da kiraye-kirayen sassauta rikicin Isra’ila da Iran, matakin Amurka ya zamo tamkar watsawa wuta fetur, da jefa rikicin cikin wani yanayi da ka iya gagara a warware shi. A daya bangaren kuma, kaso 90 na masu bayyana ra’ayoyin na ganin hare-haren da Amurka ta kai kan cibiyoyin sarrafa sinadaran nukiliyar kasar Iran, sun yi matukar cin karo da dokokin MDD, da ka’idojin cudanyar kasashen duniya, kana ya keta ’yancin kasar Iran, da tsaro da ikon kare yankunanta.

Kazalika, kaso 77 bisa dari sun jaddada cewa, sarkakiyar yankin Gabas ta Tsakiya, ba za ta iya ba da damar wanzar da zaman lafiya mai dorewa a shiyyar da karfin soji ba, kana za a iya warware batun nukiliyar Iran, da tashe-tashen hankula tsakanin Isra’ila da falasdinawa ne kadai ta hanyoyin siyasa, da tattaunawa da hawa teburin shawarwari.

An gudanar da kuri’un jin ra’ayin ne ta dandalolin CGTN na Turanci, da Sifaniyanci, da Faransanci, da Larabci, da harshen Rasha, inda mutane 10,472 dake kasashen ketare suka bayyana ra’ayoyinsu cikin sa’o’i 12. (Saminu Alhassan)

LABARAI MASU NASABA

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya
Daga Birnin Sin

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103
Daga Birnin Sin

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Next Post
Karin Kudin Mai: Hakika An Ci Amanarmu, In Ji ‘Yan Kwadago

NNPC Ya Ƙara Kuɗin Fetur, Duba Sabon Farashin

LABARAI MASU NASABA

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

Sauya Sheƙa: APC Za Ta Lashe Kashi 95% Na Ƙuri’un Kaduna A 2027 – Gwamna Sani

October 19, 2025
Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?

Ko Kin San… Maganin Sanyi Na Mata (Infection)?

October 19, 2025
JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

JTF Ta Kama Wani Da Ake Zargin Mai Safarar Miyagun Ƙwayoyi Ne Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kogi

October 19, 2025
Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

Abin Da Nijeriya Ke Bukata Kafin Samun Damar Zuwa Gasar Kofin Duniya

October 19, 2025
Yadda Ake Alkaki

Yadda Ake Alkaki

October 19, 2025
Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (1)

Kar Ki Yi Kuskuren Da Za Ki Yi Da Na Sani A Kai (2)

October 19, 2025
An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

An Sanya Hannu Kan Yarjejiyar Zaman Lafiya A Gaza

October 19, 2025
Nijar

Gwamnatin Nijar Ta Yaye Tsofaffin Mayaka 369 Da Aka Bai Wa Horon Sauya Tunani

October 19, 2025
Yadda Zargin Takardar Karatun Bogi Ta Tilasta Wa Minista Nnaji Murabus

‘Yan Siyasa 11 Da Suka Faɗa Dambarwar Takardar Shaidar Karatu Ta Bogi

October 19, 2025
gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.