• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Birtaniya: An Yi Wa Malamar Jinya Daurin Rai Da Rai Bisa Laifin Kashe Jarirai

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Labarai
0
Birtaniya: An Yi Wa Malamar Jinya Daurin Rai Da Rai Bisa Laifin Kashe Jarirai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

An yanke hukuncin daurin rai-da-rai ga wata ma’aikaciyar jinyar jarirai, Lucy Letby, wadda ita ce ta fi yi wa kananan yara kisan dauki dai-dai a tarihin baya-bayan nan na Birtaniya.

An yanke mata hukunci ne bayan samun ta da laifin kashe jarirai bakwai, da kuma yunkurin kashe karin shida a wani asibitin yara da ke Countess of Chester.

  • Ingila Ta Rage Haraji Kan Kayayyakin Nijeriya 3,000

Da gangan, Lucy Letby ta rika yi wa jarirai allura da sauran iska a cikin sirinji, kuma ta rika yi wa wasu dura da karfi, sannan ta bai wa jarirai biyu guba da sinadarin insulin.

Bayan yanke mata wannan hukunci, Lucy Letby ba ta nuna wata alamar nadama ba.

A yazu dai Letby za ta shafe tsawon gaba dayan rayuwarta a tsare, inda ta zama mace ta hudu a Birtaniya da aka taba yankewa irin wannan hukunci, wanda shi ne mafi tsanani da ake yankewa mai laifi.

Labarai Masu Nasaba

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

Alkalin kotun Mai shari’a Goss, ya bayyana laifin da Lucy ta aikata a matsayin “babban abin kyama”.

Ya ce “ta aikata abin da ya saba da tunanin dan’adam mai cikakken hankali, da ya san kimar lura da jarirai, kuma babbar cin amanar wadanda suka yarda da aikin ma’aikatan lafiya ne”.

Alkalin ya bayyana ta a matsayin mara tausayi, wadda ke sanya damuwarta cikin aikinta.

Lauyan da ke kare ta, Ben Myers KC, ya ce “Tun bayan fara shari’ar Lucy ta ki musanta aikata laifin da ake zargin ta da aikatawa, dangane haka ba shi da wani mataki da zai dauka da zai iya kai wa ga rage tsawon hukuncin da aka yanke mata”.

Harabar kotun ta cika makil da iyayen yaran da ma’aikaciyar jinyar ta halaka wa jarirai, har ma wasu sun yi sharbar hawaye a lokacin da alkalin yake karanta hukuncin da ya yanke wa mai laifin.

An ga wasu daga cikin masu sauraron karar rai a bace lokacin da suka saurari bayanan alkalin.

Wata uwa da ita ma, ta rasa danta ta ce “akwai takaici a ce akwai mutumin da zai iya aikata irin wannan mummunar aika-aika”.

Ita ma wata mahaifiya da aka kashe jaririnta cike da bakin ciki, ta sanar da kotun cewa, “ Game da mutuwar danta, tana ganin lamarin kamar a cikin wani fim din ban tsoro”.

Haka zalika, wata uwa da ke rungume da zomon wasa na yara, ta sanar da kotun cewa “Abin da Lucy Letby ta aikata, mugunta ce da kuma babban abin kunya ne sakaci a matsayinta na malamar jinya da aka bai wa amana”.

Su ma iyayen wata jaririya da aka bayyana sunanta da Baby G, wadda ita ce bakwaini mafi kankanta a cikin dukkan jariran, wacce nauyinta bai fi giram 535, sun fada wa kotun cewa: “Allah ya raya ta” amma sai “ta fada hannun shaidanu”.

Kimanin mutum 70 ne aka taba yankewa irin wannan hukunci na daurin rai-da-rai, inda ake ci gaba da duba lafiyar kwakwalwar hudu a asibiti. Idan aka yanke irin wannan hukunci, ba a taba sauya shi ba, sai dai bisa wasu dalilai na ba sabon ba.

Sauran matan da aka taba yankewa irin wannan hukunci sakamakon yi wa mutane kisan dauki dai-dai, akwai Rose West da Joanna Dennehy, sai kuma Myra Hindley, wadda tun a wancan lokacin ta riga mu gidan gaskiya.

Jagoran jam’iyyar adawa ta Labour, Keir Starmer, ya yi kira ga gwamnati ta tilasta wa masu laifin da ake yanke wa hukunci su rika fuskantar wadanda aka aikata wa laifi, ganin Letby ta ki bayyana a gaban kotu lokacin da aka yanke mata hukunci.

Ya ce “Ina son ganin an dauki mataki cikin gaggawa a wannan shari’a, saboda iyayen wadanda lamarin ya shafa sun shiga mummunar damuwa.

“Muna neman a samar da sauyi a doka wanda zai tilasta wa masu laifi, su saurari hukuncin da ake yanke musu”, in ji shi.

Shi ma Firaministan Birtaniya, Rishi Sunak, ya ce gazawa ce da kuma tsoro a ce wadanda aka yanke wa hukunci a cikin kotu, su ki fuskantar iyalan da suka aikata wa laifi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Birtaniya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Al’adu Nagari Ke Rainon Sinawa 

Next Post

Nijeriya Na Asarar Gangar Danyen Mai 400,000 A Kullum – NSA

Related

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42
Labarai

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

54 minutes ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

3 hours ago
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi
Labarai

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

5 hours ago
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

8 hours ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

9 hours ago
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 
Labarai

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

9 hours ago
Next Post
Nijeriya Na Asarar Gangar Danyen Mai 400,000 A Kullum – NSA

Nijeriya Na Asarar Gangar Danyen Mai 400,000 A Kullum – NSA

LABARAI MASU NASABA

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

An Kaddamar Da Yankin Gwajin Aikin Gona Da Sin Ta Gina A Zimbabwe

May 15, 2025
HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

HOTO: Ofishin Tsohon Shugaban Kasa Shagari Bayan Shekara 42

May 15, 2025
Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

Shawarwarin Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakanin Sin Da Amurka Sun Haifar Da Managarcin Sakamako

May 15, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.