• English
  • Business News
Wednesday, August 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Birtaniya Ta Haramta Daukar Likitoci ‘Yan Nijeriya Aiki

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Birtaniya Ta Haramta Daukar Likitoci ‘Yan Nijeriya Aiki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin Britaniya ta sanar da haramtawa hukumar kula da al’amuran ma’aikatan lafiya da masu ba da kulawa a kasar daukar likitoci da ma’aikatan lafiya aiki daga Nijeriya.

Gwamnatin ta sanar da wannan matakin ne a cikin wani kundin tsarin aikin lafiya da masu ayyukan jinkai cikin wani sako da ta wallafa a shafinta na Intanet.

  • An Kama ‘Yansanda Biyar Da Dan Kasuwa A Filato
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin: Kasar Sin Ba Ita Ce Tushen Saka Wa Kasashen Afirka Tarkon Bashi Ba

A yanzu, Nijeriya ta shiga cikin jerin kasashen da suke fama da rashin wadatattun ma’aikatan lafiya a bisa bayyanan WHO.

A watan Maris ne WHO ta fitar da sunayen kasashe 55 da suke fama da kalubalen wadatattun ma’aikatan lafiya ciki, har da Nijeriya.

Sabo da haka, ya kamata a bai wa kasashen Birtaniya, Nijeriya da sauran kasashen da aka ayyana fifiko wajen inganta bai wa ma’aikatan lafiya horo da kuma al’amuran da suka danganci ba da taimako ta yadda za a hana daukan ma’aikatan lafiya a kasashen waje.

Labarai Masu Nasaba

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

Sakon da kundin ya kunsa shi ne “bisa tsarin dokar WHO” kuma kamar yadda karara dokar ta bayyana cewa za a yi wa dokar tsarin aikin kwaskwarima bayan duk shekaru 10, ya kamata a bai wa wadannan kasashen fifiko wajen bai wa ma’aikatan lafiyarsu horon aiki domin su dada samun kwarewar aiki kana a dakatar da daukan su aiki a kasashen waje.

Cibiyoyin lafiya da kuma cibiyoyin da ke bai wa al’umma kulawa, cibiyoyin daukar ma’aikata da sauran masu alaka da daukar ma’aikatan lafiya masu hadin giwa su kiyaye daukar ma’aikatan lafiya daga wadannan kasashe har sai idan an samu tattaunawa ta fahimta tsakanin gwamnatocin kasashen.

WHO ta rubuta sunayen kasashen da ke da bukatar tallafin da kariyar da jan alli. Har idan an cimma jarjejeniya tsakanin kasar da ta haramta cibiyoyin daukar ma’aikata, ana sanya kasar cikin wannan rukunin kasashen.

Dokar ta kuma ce, har idan ba a rubuta sunan kasar da jan alli ba to yana kasancewa a rukunin masu koren alli. Kasashen da aka yi wa haramcin daukar ma’aikata sune Kenya da Nepal kawai.

Idan za a iya tunawa, wani kudirin dokar haramta bai wa likitoci ‘yan Nijeriya da suka samu horon aikinsu a kasar takadar shaidar kwarewar aiki har sai sun kwashe mafi karancin shekaru biyar suna aiki a kasar, ya yi masarar samun karatu na biyu a majalisar wakilan kasar a ranar Alhamis din da ya gabata.

Manufar dokar ita ce rage yawan likitocin da suke neman barin kasar su fita aiki a kasashen waje kana a inganta ayyukan lafiya a Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AikiBirtaniyaLikitocin NijeriyaWHO
ShareTweetSendShare
Previous Post

Muna Ci Gaba Da Buga Sabbin Kudi Yanzu -CBN

Next Post

Rashin Tsaro: Buhari Ya Gyara Nijeriya Fiye Da Yadda Ya Same Ta, In Ji Adesina

Related

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya
Manyan Labarai

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

28 minutes ago
Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

7 hours ago
Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82
Manyan Labarai

Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

8 hours ago
Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

17 hours ago
Remi Tinubu Ta Bada Gudunmawar Naira Biliyan 1 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwan Neja Ta Shafa
Manyan Labarai

Remi Tinubu Ta Bada Gudunmawar Naira Biliyan 1 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwan Neja Ta Shafa

24 hours ago
Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32
Manyan Labarai

Shugaban ‘Yan Bindiga A Zamfara, Bello Turji, Ya Ajiye Makamai, Ya Saki Mutane 32

1 day ago
Next Post
Rashin Tsaro: Buhari Ya Gyara Nijeriya Fiye Da Yadda Ya Same Ta, In Ji Adesina

Rashin Tsaro: Buhari Ya Gyara Nijeriya Fiye Da Yadda Ya Same Ta, In Ji Adesina

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Nafisa, Rukayya, Hadiza Murnar Samun Nasarar Zama Gwanaye A Gasar Turanci Ta Duniya

August 6, 2025
Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

Sin Ta Samar Da Yuan Biliyan Daya Domin Ayyukan Jin Kai Sakamakon Ibtila’in Ambaliyar Ruwa

August 6, 2025
Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

Uwargidar Gwamnan Katsina Ta Nemi A Taimaka Wa Mata Wajen Yaƙi Da Ciwon Nono Da Na Mahaifa

August 6, 2025
Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

Bello Turji Bai Yi Sulhu Da Kowa Ba – Guyawa Isa

August 6, 2025
Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

Sojoji Sun Kama Mai Yi Wa Boko Haram Safarar Man Fetur A Borno

August 6, 2025
Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

Matar Marigayi MKO Abiola, Ta Rasu Tana Da Shekaru 82

August 6, 2025
Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

Remi Tinubu Ta Bai Wa Waɗanda Ambaliya Ta Shafa A Neja Tallafin N1bn

August 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

Gwamnatin Tarayya Za Ta Farfaɗo Da Noman Dabino – Shettima

August 6, 2025
Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

Kwamishinan Sufuri Ya Yi Murabus Kan Belin Wani Da Ake Zargi Da Laifin Safarar Kwaya A Kano

August 6, 2025
Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

Hare-haren Boko Haram Da ‘Yan Bindiga Ya Ragu A Cikin Shekaru Biyu – Ribadu

August 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.