• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Biyan Basukan Waje Ya Ƙaru Zuwa Dala Biliyan 2.78 – Rahoton CBN

by Khalid Idris Doya
10 months ago
in Labarai
0
Biyan Basukan Waje Ya Ƙaru Zuwa Dala Biliyan 2.78 – Rahoton CBN
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Biyan basukan Nijeriya a farkon watanni bakwai na wannan shekarar ya karu da kaso 53.63 ko dala miliyan 971.47 zuwa dala biliyan 2.78, wanda ya karu kan dala biliyan 1.81 da aka samu a daidai irin wannan lokacin a shekarar 2023.

Wannan bayanin na kunshe ne ta cikin rahoton biyan kudaden kasa da kasa na mako-mako da aka wallafa a shafin yanar gizo ta Babban Bankin Nijeriya (CBN).

  • Matsalolin Tsaro Da Ambaliya: ‘Yan Nijeriya Sun Sayo Abinci Daga Waje Na Tiriliyan 3 – CBN
  • Emefiele Ya Yi Amfani Da Wakili Wajen Karbar kwangila Daga CBN – Shaida 

Bayanan na CBN ya nuna cewa biyan basukan waje ya karu a watan Mayu da dala miliyan 854.36, yayin da na watan Janairu ya biyo baya da dala miliyan 560.51, sai kuma watan Yuli mai dala miliyan 542.

Biyan basukan waje na sauran watanni da suka hada da Febrairu, Maris, da Afrilu sun tsaya kasa da dala miliyan 300, inda kuma aka samu wata mafi karancin biya wato watan Yunin 2024 da aka biya dala miliyan 50.82.

A cewar ofishin kula da basuka (DMO), bashin da ke makale kan Nijeriya ya kai naira tiriliyan 121.6 zuwa karshen zangon farko na wannan shekarar.

Labarai Masu Nasaba

Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

Rahoton DMO na cewa, “Bashin da ake bin Nijeriya ya kai tiriliyan 121.67 (dala biliyan 91.46) zuwa ranar 31 ga watan Maris din 2024. Idan aka kwatanta da na ranar 31 watan Disamban 2023, da ya kai tiriliyan 97.34 (Dala biliyan 108.23). Adadin kudin basukan waje sun kai tiriliyan 65.65 (Dala biliyan 46.29), yayin da kuma basukan cikin gida suka kai naira tiriliyan 56.02 (Dala biliyan 42.12).”

Da yake tofa albarkacin bakinsa kan batun karin kudin basukan, daraktan bincike da tsare-tsare a Chapel Hill Denham, Tajudeen Ibrahim, ya misalta yawan karuwan basukan da faduwar darajar naira da ya janyo basukan suka kai har haka.

“Akwai tasirin hulda da kudin kasashen waje wajen biyan basuka, na biyu kuma shi ne ya danganta da yanayin lokacin da ka je neman rancen shi ma yana kara tasiri, Nijeriya ta kara ciwo bashi a ciki da waje. Baya ga hakan, akwai zancen faduwar darajar naira, duk sun yi tasiri a wannan bangaren,” ya shaida.

Tunin dai masana suka yi ta gargadin yawan ciwo basuka na kara jefa kasar nan cikin damuwa da yanayi marar tabbas.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BashiCBN
ShareTweetSendShare
Previous Post

Marubuta Na Taimakawa Wajen Bunkasa Rayuwar Al’umma -Miyetti

Next Post

Bayan Shekaru 8 Da Kullewa, Gwamnan Kano Ya Buɗe Makarantar Koyon Tuƙin Mota A Kano

Related

Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang
Manyan Labarai

Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

3 hours ago
David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC
Manyan Labarai

David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

6 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutum 6 A Ƙauyukan Filato, Sun Jikkata Wasu
Labarai

Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato

7 hours ago
An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa
Labarai

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

15 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

16 hours ago
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma
Labarai

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

17 hours ago
Next Post
Bayan Shekaru 8 Da Kullewa, Gwamnan Kano Ya Buɗe Makarantar Koyon Tuƙin Mota A Kano

Bayan Shekaru 8 Da Kullewa, Gwamnan Kano Ya Buɗe Makarantar Koyon Tuƙin Mota A Kano

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea

Arsenal Ta Sayi Kepa Daga Chelsea

July 2, 2025
Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

Ba Zan Bar Jam’iyyar PDP Ba – Gwamna Muftwang

July 2, 2025
David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

David Mark Da Aregbesola Sun Zama Shugaba Da Sakataren Jam’iyyar ADC

July 2, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sake Kashe Mutum 6 A Ƙauyukan Filato, Sun Jikkata Wasu

Rikicin Gonar Gado Ya Yi Ajalin Mutum Ɗaya, An Ƙone Gidaje A Filato

July 2, 2025
An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.