• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Matsalolin Tsaro Da Ambaliya: ‘Yan Nijeriya Sun Sayo Abinci Daga Waje Na Tiriliyan 3 – CBN

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
tallafi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Babban Bankin Nijeriya (CBN) ya bayyana cewa ‘yan Nijeriy sun kashe dalar Amurka biliyan 2.13 wajen shigo da kayan abinci daga kasashen ketare a shekarar 2023.

A cewar rahoton kiddiga na zanga-zango da CBN ya fitar, akwai bukatu da dama da kasashen waje ke da su kan Afrika duk da cewa nahiyar na matukar fifita sayo kayan abinci daga can.

  • Jami’ai Sun Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka Karkashin Dandalin FOCAC 
  • Za A Fara Rabon Takin CBN Kyauta, Sai Dai Masana Sun Ba Da Shawara

Wannan dai na zuwa ne a yayin da farashin kayayyakin abinci da ake shigo da su cikin Nijeriya ya karu zuwa babban mataki, inda ya kai har zuwa kaso 34 cikin 100 a cikin shekara guda tsakanin watan Afrilun 2023 zuwa Afrilun 2024.

Farashin kayan abinci dai ya yi tashin gwauron zabi a nahiyar Afrika sakamakon lamuran da suka shafi harkokin duniya, inda nahiyar ke kan gaba-gaba wajen shigo da kayayyaki a kasashen waje domin amfanin kai da kai.

Makuden kudaden da ake kashewa wajen sayo kayan abinci a kasashen waje na daga cikin manyan damuwowin da ke shafan tattalin arzikin Nijeriya. Kasar tana da dubban albarkatun gona, kuma akwai sa’ayin da ake ta kan yi wajen fitar da abincin gida duk a kokarin ganin an rage dogaro da shigo da kayan abinci a kasashen waje.

Labarai Masu Nasaba

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Sai dai, matsalolin da suka shafi na rashin kyan hanyoyi, matsalar tsaro, canjin yanayi su na taka rawa wajen dakile manufar da aka sanya a gaba na dogara da abincin gida.

Gwamnatin tarayya ta taba yin fatali da shigo da kayayyakin abinci na kasashen waje a wani matakin magance tsadar kayan abinci da kuma matsin rayuwa da al’umma suka shiga.

Tulin kudin da aka kashe wajen sayo kayan abincin kamar yadda masana suka ce, kai tsaye na nuni da cewa gwamnatin Nijeriya har yanzu ba ta dauki matakin magance matsalar yunwa da fatara zuwa shekarar 2030 ba, kamar yadda ke kunshe cikin shirin cimma muradin karni na majalisar dinkin duniya.

A shekarar 2023 kamar yadda kiddigar ya nuna, an kashe dala miliyan 245.7 wajen shigo da kayan abinci a watan Janairu, dala miliyan 163.6 a watan Fabrairu, dala miliyan 268.4 a watan Maris, dala miliyan 240.9 a watan Afrilu, dala miliyan 238.3 a watan Mayu da kuma dala miliyan 206.1 aka rasa wajen sayo kayan abinci a watan Yuni.

A watan Yuli na 2023 kuwa, babban bankin kasar nan ya ce an fitar da kudin da ya kai dala miliyan 58 wajen sayo kayan abinci kawai, dala miliyan 95.3 a watan Agusta, dala miliyan 119.9 a Satumba, dala miliyan 132.4 a Oktoba, dala miliyan 235.9 a Nuwamba da kuma dala miliyan 126.2 a watan Disamban bara.

A watan Afrilun 2024, rahoton hauhawar farashin kayan abinci da hukumar kidddiga ta kasa (NBS) ta fitr, ya karu daga kaso 15.92 cikin dari zuwa 40.53, sakamakon tashin farashin fulawa, garri, buredi, alkama, semolina, doya, mangyade, kifi, nama, hatta, kaji, mango, ayaba, kayan marmari na lambu, lipton na shayi, bombita, miliya, madara, da dai sauran nau’ikan kayan abinci.

Da yake tofa albarkacin baki kan wannan lamarin, shugaban kungiyar manoma a Nijeriya, Kabir Ibrahim, ya ce a halin da ake ciki duk da wannan adadin kudin da aka kashe wajen shigo da kayayyakin, ba wai an amincewa da a shigo da kowani irin kaya ba ne.

Ya ce, tabbas za a iya samun karuwar adadin a wannan shekarar sakamakon kara dogara da ake yi wajen sayo kayan abinci daga kasashen waje.

Kabir ya nuna cewa a shekarun da aka hana shigo da kayan abinci daga kasashen waje ba a kashe wadannan makuden kudaden ba, amma yanzu an dauko hanyar ci gaba da salwatar da makuden kudade domin shigo da kayan abincin kasashen waje.

Ya nuna cewa idan da za a maida hankali kan kayan abicin da ake nomawa a cikin gida, zai kawo karshen matsaloli da dama.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CBNlamunin BankiNomaYan bindiga
ShareTweetSendShare
Previous Post

Rundunar Sojojin Kasar Sin Ta Ci Gaba Da Yin Atisayen Soja a Wuraren Dake Kewayen Tsibirin Taiwan

Next Post

An Bude Taron Koli Karo Na 7 Na Raya Yanar Gizo Na Sin 

Related

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa
Labarai

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

4 hours ago
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP
Manyan Labarai

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

4 hours ago
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba
Kotu Da Ɗansanda

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

8 hours ago
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC
Manyan Labarai

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

8 hours ago
Abin Da Ya Sa ‘Yan Nijeriya Ba Su Mori Dimokuradiyya Ba Har Yanzu –Jega
Labarai

Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega

11 hours ago
‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote
Labarai

‘Yan Kasuwa Na Kalubalantar Rage Faranshin Man Dangote

12 hours ago
Next Post
An Bude Taron Koli Karo Na 7 Na Raya Yanar Gizo Na Sin 

An Bude Taron Koli Karo Na 7 Na Raya Yanar Gizo Na Sin 

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

Gwamna Ademola Adeleke Ya Ƙaryata Jita-Jitar Sauya Sheƙa Daga PDP Zuwa APC

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.