• English
  • Business News
Friday, July 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Biyan Basukan Waje Ya Ƙaru Zuwa Dala Biliyan 2.78 – Rahoton CBN

by Khalid Idris Doya
10 months ago
in Labarai
0
Biyan Basukan Waje Ya Ƙaru Zuwa Dala Biliyan 2.78 – Rahoton CBN
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Biyan basukan Nijeriya a farkon watanni bakwai na wannan shekarar ya karu da kaso 53.63 ko dala miliyan 971.47 zuwa dala biliyan 2.78, wanda ya karu kan dala biliyan 1.81 da aka samu a daidai irin wannan lokacin a shekarar 2023.

Wannan bayanin na kunshe ne ta cikin rahoton biyan kudaden kasa da kasa na mako-mako da aka wallafa a shafin yanar gizo ta Babban Bankin Nijeriya (CBN).

  • Matsalolin Tsaro Da Ambaliya: ‘Yan Nijeriya Sun Sayo Abinci Daga Waje Na Tiriliyan 3 – CBN
  • Emefiele Ya Yi Amfani Da Wakili Wajen Karbar kwangila Daga CBN – Shaida 

Bayanan na CBN ya nuna cewa biyan basukan waje ya karu a watan Mayu da dala miliyan 854.36, yayin da na watan Janairu ya biyo baya da dala miliyan 560.51, sai kuma watan Yuli mai dala miliyan 542.

Biyan basukan waje na sauran watanni da suka hada da Febrairu, Maris, da Afrilu sun tsaya kasa da dala miliyan 300, inda kuma aka samu wata mafi karancin biya wato watan Yunin 2024 da aka biya dala miliyan 50.82.

A cewar ofishin kula da basuka (DMO), bashin da ke makale kan Nijeriya ya kai naira tiriliyan 121.6 zuwa karshen zangon farko na wannan shekarar.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

Rahoton DMO na cewa, “Bashin da ake bin Nijeriya ya kai tiriliyan 121.67 (dala biliyan 91.46) zuwa ranar 31 ga watan Maris din 2024. Idan aka kwatanta da na ranar 31 watan Disamban 2023, da ya kai tiriliyan 97.34 (Dala biliyan 108.23). Adadin kudin basukan waje sun kai tiriliyan 65.65 (Dala biliyan 46.29), yayin da kuma basukan cikin gida suka kai naira tiriliyan 56.02 (Dala biliyan 42.12).”

Da yake tofa albarkacin bakinsa kan batun karin kudin basukan, daraktan bincike da tsare-tsare a Chapel Hill Denham, Tajudeen Ibrahim, ya misalta yawan karuwan basukan da faduwar darajar naira da ya janyo basukan suka kai har haka.

“Akwai tasirin hulda da kudin kasashen waje wajen biyan basuka, na biyu kuma shi ne ya danganta da yanayin lokacin da ka je neman rancen shi ma yana kara tasiri, Nijeriya ta kara ciwo bashi a ciki da waje. Baya ga hakan, akwai zancen faduwar darajar naira, duk sun yi tasiri a wannan bangaren,” ya shaida.

Tunin dai masana suka yi ta gargadin yawan ciwo basuka na kara jefa kasar nan cikin damuwa da yanayi marar tabbas.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BashiCBN
ShareTweetSendShare
Previous Post

Marubuta Na Taimakawa Wajen Bunkasa Rayuwar Al’umma -Miyetti

Next Post

Bayan Shekaru 8 Da Kullewa, Gwamnan Kano Ya Buɗe Makarantar Koyon Tuƙin Mota A Kano

Related

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

16 minutes ago
An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa
Manyan Labarai

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

33 minutes ago
Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 
Labarai

Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

51 minutes ago
Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista
Labarai

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

3 hours ago
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa
Manyan Labarai

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

5 hours ago
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…
Manyan Labarai

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

6 hours ago
Next Post
Bayan Shekaru 8 Da Kullewa, Gwamnan Kano Ya Buɗe Makarantar Koyon Tuƙin Mota A Kano

Bayan Shekaru 8 Da Kullewa, Gwamnan Kano Ya Buɗe Makarantar Koyon Tuƙin Mota A Kano

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga Tare Da Kwato Makamai A Jihar Filato

‘Yan Bindiga Sun Kai Wa ‘Yansanda Hari Tare Da Kashe Wani Mutum Da Raunata Wani A Nasarawa

July 11, 2025
Goron Sallah

GORON JUMA’A

July 11, 2025
An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

An Koka Kan Yadda Tsafi Da Jariran Da Aka Haifa Da Tsagaggen Lebe Ke Karuwa

July 11, 2025
Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

Bafarawa Ya Kaddamar Da Kungiyar Hada Kan Arewa Da Samar Da Zaman lafiya A Kaduna 

July 11, 2025
Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

Hadarin Da Ke Kunshe Da Jin Bangare Daya Na Labari

July 11, 2025
NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

NPA Ta Yi Wa Ma’aikatanta 1,500 Karin Girma

July 11, 2025
Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

Shirin Sabunta Fata Na Tinubu Yana Samar da Damarmakin Cigaba — Minista

July 11, 2025
NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

NPA Ta Tarbi Babban Jirgin ‘Ruwa MB Ocean Dragon’ Don Bunkasa Ayyukanta

July 11, 2025
Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

Rikicin Masarautar Kano Ya Kara Zafafa

July 11, 2025
Yunkurin Magance Matsalar Tsaro Da Rigingimu A Arewa…

Akwai Bukatar Hada Kai Da Aiki Tare Tsakanin Hukumomin Tsaro

July 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.