• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano

by yahuzajere
1 year ago
Gwam

Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamanatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano

Assalamu alaikum warahmatullah wabarakatuhu!

Cikin girmamawa gare ku shugabanni da Jami’o’in Lafiya na ƙasata baki ɗaya.

Na ɗauki alƙalamina ne domin na kiraye ku a kan wani ganganci da kan tafi da rayukan al’umma da na ga hukumar haraji ta Nijeriya (FIRS) ta yi a wani asibiti mai zaman kansa a birnin Kano, wato ‘Best Choice Specialist Hospital’ da ke unguwar Gadon Ƙaya kan shataletalen Tal’udu.

Wasu daga cikin marasa lafiya da wasu iyaye sun kawo wa jaridar Alfijir labarai ƙorafi a kan yadda jami’an hukumar tattara harajin suka zo tare da jam’ian tsaro da bindigogi suna musu barazana a kan sai dole sun tashi sun fita daga cikin asibitin bayan bala’in da suke ciki na rashin lafiya, ga shi kuma sun yi yawo wurare da dama a Kano sun rasa inda za a iya samun gadon kwanciya musamman a ɓangaren larurar da ta shafi yara da jarirai sai nan ɗin!

LABARAI MASU NASABA

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

  • Gwamnan Kano Ya Ɗauki Nauyin Ɗawainiyar Marayu 95 Har Zuwa Jami’a

 

Babban abin takaicin ma shi ne wasu daga cikin likitoci da ke Kano da ma wasu jahohin sun tsunduma yajin aiki a kan haƙƙoƙinsu, maimakon hukumar ta yi aiki da hankali wajen taimaka wa al’umma domin jin-ƙan su, a’a sai ƙoƙari take wajen ƙara nakasa rayuwar waɗannan marasa lafiyar da ke asibitin ko kuma ma hallaka su!

Matsalar haraji da ke tsakaninku da asibiti matsala ce da ta shafe ku, ba abin da ya shafi waɗanda suka zo neman lafiya asibitin ba ne.

Don haka muke kira ga shugabanni na wannan ƙasa tamu mai albarka, da hukumar kare haƙƙin bil’adama kan wannan cin zarafin da aka yi wa al’umma da a kawo musu ɗauki cikin gaggawa.

Ku kuma hukumar tattara haraji, ku dubi Allah ku canja hanyar da za ku bi wajen neman haƙƙinku, don inda haƙƙinku ya ƙare nan fa na wasu ya fara.

Idan da ƴaƴanku ne ke zuwa asibitin ba na talakawa ba, da ai ba za ku yi hakan ba!

Kukan Kurciya Jawabi Ne!

Daga
MUSA BESTSELLER, EDITAN JARIDAR ALFIJIR LABARAI
Mai Biyayya A Gare ku

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

March 18, 2025
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

November 10, 2024
Nijeriya
Ra'ayoyi

Ra’ayoyin ‘Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

October 5, 2024
Next Post
Ka Da Mu Yanke Kauna Da Nijeriya – Jonathan

Ka Da Mu Yanke Kauna Da Nijeriya - Jonathan

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.