ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

by Leadership Hausa and Sulaiman
2 years ago
Yara

Alhaji Abdullahi Yaluwa Ajiyan Yawuri, shi ne shugaban ‘yan Arewa masu mallakar gidajen Rediyo da Talabijin. A tattauanwar da ya yi da wakilinmu, ya bayyana matsayar kungiyarsu a kan yadda aka wulakanta yara kanana da sunan gurfanar da su a kan shiga zanga-zangar tsadar rayuwa watanni 6 da suka wuce. Ga dai bayanan da ya yi.

 

“Makasudin wannan labari da muka fitar shi ne bayan mun ga hotuna a Soshiyal Midiya da yara kanana, duk wanda ya dube su za ka ga tsoro da barazana a fuskokinsu, da yunwa da kuma shida ta cewa an tirsasa musu da wuya, an kuma yi amfani da tsari na yunwa, kuma babban abin tambaya ma yanzu shi ne, su wadannan da Allah ya sa aka gani kila su Allah ya yi musu gyadar dogo, to me ya samu sauran da kila Allah bai nufa su an kawo su kotun ba?

ADVERTISEMENT
  • NAHCON Za Ta Biya Alhazai Diyyar Wasu Kuɗaɗe Kan Ƙarancin Kula Da Su Lokacin Hajji
  • EFCC Ta Gurfanar Da Tsofaffin Gwamnoni Da Tsofaffin Ministoci, Bayan Kwato Kadarorin Biliyoyin Naira A Kasashen Waje

“To babu shakka wannan tsari na shugabancin rashin gaskiya da muka gani dole ya tayar wa kowa hankali ba a Arewa kawai ba a duk duniya, kuma ya nuna cewa a karkashin wannan shugabanci na Bola Ahmed Tinibu Nijeriya fa ta kama hanyar lalacewa, kuma babu yadda za a yi mu kira kanmu da kasa mai aiki da Dimukradiyya.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

“To wadannan yara an zarge su ne wasu daga cikinsu dai yan shekaru 12 wasu 13 wasu 14, an zarge su wai da yi wa Nijeriya zagon kasa, to ka dubi wadannan yaran ka ce wai su ne su kai barazanar tunbuke gwamnatin Tinubu, to ka san babau shakka akwai rashin hankali a wannan zaton.

 

‘’Kuma abin da yake bani mamaki shi ne, gwanati da ta ce tana da masaniya akan mutanen da suka assasa wannan zanga-zangar ta #EndBadGobernace# har yanzu ba a kawo su kotu ba sai wadannan yara wanda yawancin su ma idan a wajen zanga-zangar aka kama su, to sun tafi tafi ne kawai a matsayin yaro ya ji abin hanyaniya ya ruga ya gani kuma wannan a gidan kowa akwai irin su.

 

Mun yi kira ga gwamnati da ta saki wadannan yaran kuma ta tabbatar da an kiyaye lafiyarsu, kuma wadanda ba su da kafiya muna kira ga gwamnati ta fita da su kasar waje kamar yadda shugaban kasa ke fita a kai su Faransa a kai su Ingila domin a duba lafiyarsu, kuma a biya su diyya, sannan duk wani wanda ke da hannu a cikin wannan ta’asar daga Babban Sufeto Janar na ‘Yansanda zuwa mai shari’a, lauyoyin gwamnati ma, to duk wanda ke hannu a wannan Fir’aunancin, muna kira ga gwamnati ta kama su a yi wani kwamiti da za ta bicike su kuma wanda aka kama da laifi a horar da shi. mun jaddada wa gwamnati cewa, matsaloli da Nijeriya ke ciki ba ‘yan Nijeriya suka jawo shi ba, tsarin shugabancin wannan gwamnatin ne ya kawo wadannan matsaloli, kuma ‘yan Nijerita ba za su daina fitowa zanga-zanga ba domin wadanda ke shugabancin mu yanzu ba su fi mu zama ‘yan Nijeriya ba.

 

“Bayan haka, muna neman cewa tsare-tsare na gwamnati dake kawo mana bala’i, da jawo mana fakirci, dake sa mutane suna mutuwa a gidansu da yunwa, to muna kira ga gwamnati ta janye wadannan.

 

“Maganar tallafi akan fetur, maganar tallafi akan biyan biyan kudin wuta, maganar tallafi akan sauran abubuwa na gwamnati da wasu kasashe ke yi, ko kasashen da ke amfani da jari hujja ba su daina ba da irin wannnan tallafin ba, muna kira ga gwamnati ta janye wadannan tsare-tsare kuma a dawo mana da tsarin da muka amince domin su ne shugabannin, amma mu ake shigabanta, kuma yadda za a ce ra’ayinmu bai da wani muhimmanci akan yadda gwamnati za ta gudanar da shugabancinta, mun gaji da ba mu hakuri, “Mun gaji da gafara sa muna so mu gani a kasa, ita ce babbar magana kuma shi ne babban kiran da muka yi ga gwamnati”.

Yara
Leadership Hausa
Website |  + posts Bio
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
  • Leadership Hausa
    Batun Guguwar Kakar Yakin Neman Zabukan 2027 A Nijeriya
Yara
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna
  • Sulaiman
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

MASU ALAKA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano
Siyasa

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

April 25, 2026
Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

March 18, 2025
Nijeriya
Ra'ayoyi

Ra’ayoyin ‘Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

October 5, 2024
Next Post
Masana Na Ganin Akwai Kyakkyawar Dama A Dangantakar Sin Da Najeriya

Masana Na Ganin Akwai Kyakkyawar Dama A Dangantakar Sin Da Najeriya

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.