ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ra’ayoyin ‘Yan Nijeriya A Kan Zagayowar Ranar Samun ‘Yancin Kai

by Abubakar Abba and Sulaiman
2 years ago
Nijeriya

A ranar Talata 1 ga watan Oktoba Nijeriya ta yi bikin cika shekara 64 da samun mulkin kai daga Turawa. Wasu ‘yan Nijeriya sun bayyana yadda suke ji da kuma fatan da suke da shi a kan wannan biki. Yayin da wasu ke cewa Nijeriya ta cikia burin a daidai wannan lokaci wasu kuma na ganin samsam Nijeriya bata yi abin azo a gani ba musamman in aka lura da wasu kasashe tsasrarrakin kasar nan, wadanda muka samu ‘yancin kai a kusan lokaci daya amma sun yi mana wajen ci gaba da bunkasar tattalin arziki ga dai yadda suka bayyana ra’ayoyin na su.

 

Alh. Adamu Muhammed Makarfi: Mai fashin baki a al’amuran yau da kullum. A nawa ra’ayin, koda ma gwamnatin ta bayyana cewa, ba za ta gudanar da shagulgulan bikin zagayowar ranar ta samun ‘yancin kan Nijeriya ba, koma za ta yi dai, akasarin ‘yan kasar musamman talakawa da bas u iya ciyar da iyalansu sau uku a rana, babu wani da zai damu da wani maganar zagoyowar ranar.

ADVERTISEMENT
  • Wakilin Sin Ya Bukaci Sassan Somaliya Da Su Kara Azamar Warware Sabani Ta Hanyar Tattaunawa
  • Habasha Ta Jinjinawa Masu Zuba Jari Na Kasar Sin

Tun daga badi zuwa yau, da gwamnatin ta hau karagar mulkin kasar, babu wani abu da sauya na ci gaba, illama ma dai, sai kara jefa akasarin ‘yan kasar da gwamnatin ta yi a cikin ukubar rayuwa, musamman ta hanyar cire tallafin man fetur da ta yi.

 

LABARAI MASU NASABA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

Irin wadannan tsauraran tsare-tsaren da gwamnatin ta zo da su, sun kara tagyyar rayuwar talakawan kasar.

 

Hajiya Aisha Abubakar :Shugabar gidauniyar Zulifata da ke a jihar Kaduna da ke sasanta ma’aurata da kwatowa kananan yara hakkinsu, ta ce, a kullum kwannan duniya a gidauniyra mu, muna karbar korafe korafe iri-iri daga gun mata kan yadda mazajensu ke gaza ciyar da iyalansu, duk wannan zan iya cewa, ya samu asali ne daga irin tsararan tsare-tsaren da gwamnatin ta zo da su, musamman kara farashin man feutr da kuma cire tallafin mai.

 

Ta ce, karain abun takaici shi ne, yadda wasu magindantan ke bin dare, suna shiga cikin gonakai domin satar kayan amfanin gona da manoma suka girbe domin su ciyar da iyalansu.

 

Yau ko da magidanci dan kasuwa ne, ko da yaje kasuwar, babu wani gwabbaban ciniki da zai yi da zai iya kula da rayuwar iyalansa.

 

Malam Zakari Adamu: Shi kuwa wani malami a kwaleji kimiyya da fasaha ta tarayya da ke a Jihar Kaduna Malam Zakari Adamu ya ce, a nasa ra’ayin har yanzu gwamnatin da lamau ba ta dauki hanyar samarwa da ‘yan kasar sauki ba domin kuwa, a kullum tunaninta, kara karkata yake a kan jefa ‘yan kasar a cikin kunci ta hanyar fito da tsare-tsare, ba tare da daukar kwararran matakan da za su samarwa da ‘yan Nijeriya sauki ba.

 

Ya zama wajibi, gwamnatin ta sani cewa, zabar ta aka yi kuma ba mulkin karfa-karfa ya dace ta rinka yiwa ‘yan kasar ba, musamman talakawa.

 

Malam Babbangida Yola; tabbas shekara 64 a cikin shekarun kasa ba abin wasa ba ne. Nijeriya ta fuskanci gwagwamarwa mai karfi a cikin wadannan shekarun. Tun daga yakin basasa da gano man fetur da bunkasar tattalin arziki a fannoni da dama. Dole a yaba da wadannan ci gaba, amma kuma in aka lura irin ci gaba da aka samu wasu kasashen da muka samu ‘yancin kai a daidai lokaci daya, sai muce abin bai kai yadda ake bukata ba. Matsalar a Nijeriya shi ne yadda shugabanin suna kasa tsayuwa su yi aiki yadda ya kamata da kuma yadda shugabannin bas a son ci gaba da ayyukan da wadanda sduka gaba suka fara na ci gaba.

Yanci
Abubakar Abba
+ posts Bio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    “Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”
Yanci
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma
  • Sulaiman
    Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani
  • Sulaiman
    Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana
  • Sulaiman
    Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

MASU ALAKA

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano
Siyasa

Gwarzo Na Shirin Sake Fitowa Domin Kawo Sabbin Salon Siyasa A Kano

April 25, 2026
Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 
Ra'ayoyi

Madallah Da Hutu Ga ‘Yan Sakandire Domin Azumi 

March 18, 2025
Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri
Ra'ayoyi

Ya Kamata A Biya Yaran Da Aka Gurfanar Saboda Zanga-Zanga Cikakkiyar Diyya – Ajiyan Yawuri

November 10, 2024
Next Post
Gwamna Dauda Ya Kammala Biyan Bashin Ma’aikata Fiye Da Naira Biliyan 9

Gwamna Dauda Ya Kammala Biyan Bashin Ma'aikata Fiye Da Naira Biliyan 9

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026
Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

Me Ya Sa Ake Ganin Afrika Na Da Damar Taka Rawa A Tsarin Tattalin Arzikin Duniya?

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.