• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

by Ra'ayinmu
2 months ago
Nijeriya

Bisa wasu alƙaluma da Ƙungiyar Ƙasa da Ƙasa da ke aikin jin ƙai wato Red Cross ta fitar a kwanan baya, sun nuna cewa, aƙalla ƴan Nijeriya dubu 23,659 ne suka ɓace, waɗanda kuma har yau, ƴanuwansu ba su sake jin ɗuriyarsu ba. Wannan lamari ke ci gaba da jefa rayuwar ƴanuwa aƙalla dubu 13,595 a cikin fargaba.

A saboda hakan, ake ganin ya zama wajibi matakan gwamnati uku na ƙasar su gaggauta ɗaukar matakan gaggawa domin a lalubo mafita. Red Cross ta fitar da waɗannan alƙaluman ne a yayin zagayowar ranar ɓacewar mutane ta duniya da aka gudanar a baya-bayan nan. Ƙungiyar ta yi nuni da cewa, batun ya fi ƙarfin alƙaluma, domin irin halin damuwa da iyaye mata da ƴaƴansu ke shiga musamman sakamakon hare-haren ƴan ta’adda.

  • ‘Yansanda Sun Ceto Wani Dan Shekara 25 Da Aka Sace A Jihar Kebbi
  • An Cafke Mutum Hudu Bayan ‘Yan Fashi 20 Sun Afka Wasu Gidaje A Bauchi

Kazalika, tafiye-tafiyen ƴan cinari a ciki da wajen ƙasar na ƙara haifar da ɓacewar mutane wanda hakan ya janyo mutuwarsu, ƴanuwansu kuma ba su sake jin ɗuriyarsu ba. Idan da gawar aka gani, hakan na sauƙaƙa wa iyali maimakon a ce sun ɓace gaba ɗaya. Batun kuma ba wai kawai ya tsaya kan waɗanda suka rasa ƴanuwansu ba, hatta al’umma gaba ɗaya na shiga cikin tsoro mai yuwa su fuskanci irin wannan matsala.

Matakan da gwamnati ke ɗauka kan lamarin sun yi ƙaranci. Ko da yake hukumomin tsaro na fitar da sanarwar ceto wasu daga cikin mutanen da suka ɓace, yawan ɓacewar mutane ya sa ya zama wajibi a ɗauki tsare-tsaren da za su magance wannan matsala. Har yanzu babu wani ingantaccen tsari na ƙasa da aka samar domin magance matsalar, balle a ware kuɗaɗe don tallafa wa ƴan uwa da lamarin ya shafa.

Ƴanuwan da ke kai rahoton ɓacewar mutanensu kuma suna fuskantar ɓata lokaci saboda tsararan tsare-tsare, abin da ke hana su samar da bayanan da suka kamata. Sai dai ƙungiyoyi kamar ICRC sun samar da tsarin zamani kan lamarin, wanda ya ba su damar gano wasu da suka ɓace tare da miƙa su ga iyalansu, har ma da tattara sabbin sunaye 451 na waɗanda suka ɓace. Amma bai kamata a bar irin waɗannan ƙungiyoyi kaɗai da nauyin ba, domin abu ne da gwamnati itama ta kamata ta ɗauki nauyi.

LABARAI MASU NASABA

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Ya kamata a kafa hukumar musamman da za ta kula da gano mutane da suka ɓace tare da bata ƙarfi don gudanar da bincike. Kaso 68 cikin 100 na masu neman ƴaƴan da suka ɓace iyaye mata ne, amma da dama suna dawowa hannu rabbana saboda rashin tsari daga mahukunta. A jihar Yobe kaɗai, yara 2,500 ne aka ce sun ɓace, mafi yawan su a Gujba, abin da ya nuna gazawar gwamnati wajen kare rayuka a Arewa maso Gabas.

Yakuma zama wajibi a samar da tsare-tsaren gwamnati da za su kare haƙƙin ƴanuwa waɗanda suka rasa nasu, musamman a jihohin da ake fama da tashe-tashen hankula. Waɗannan tsare-tsaren za su yi aiki kaf shoulder da al’ummomin yankuna, sarakunan gargajiya, malaman addini da ƙungiyoyin sa kai.

Haka kuma dole al’umma su tsaya tsayin daka wajen bai wa iyalan waɗanda suka ɓace kariya daga nuna masu ƙyama tare da taimaka musu da tallafin da suke matuƙar buƙata.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nijeriya
Manyan Labarai

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Next Post
Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025
Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.