• English
  • Business News
Wednesday, September 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Kaddamar Da Hanyar Nguru-Gashua-Bayamari A Yobe

by Muhammad Maitela
3 years ago
in Kananan Labarai
0
Buhari Ya Kaddamar Da Hanyar Nguru-Gashua-Bayamari A Yobe
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa, Muhammadu Buhari, ya kaddamar da bude sabuwar hanyar da gwamnatin tarayya ta kammala wadda ta tashi daga Nguru zuwa Gashua ta wuce Baymari tare da mikata a hannun gwamnatin jihar Yobe a ranar Lahadi.

Da yake jawabi a madadin shugaban Buhari a wajen taron bude hanyar, Ministan Wutar Lantarki, Abubakar D. Aliyu, ya bayyana aikin hanyar a matsayin daya daga cikin muhimman ayyukan da gwamnatin tarayya ta gudanar a fadin kasar nan domin bunkasa harkokin sufuri da tattalin arziki a kasa.

  • Uwa Ta Yi Shahada Bayan Karya Dan Bindiga Da Tabarya Wajen Kare Danta
  • An Tabbatar Da Yusuf Baba-Ahmed A Matsayin Mataimakin Peter Obi

Ya ce, “Kamar yadda zaku shaida, zamu mika wannan hanya mai tazarar kilomita sama da 55, wadda ta sada garuruwan Nguru-Gashua- Bayamari a jihar Yobe zuwa jihohin Jigawa da Borno.”

“Har wala yau kuma, hanya ce mai matuqar muhimmanci wadda za ta bunqasa harkokin noma da kasuwanci a wannan yankin.”

A nashi vangaren, Minista a Ma’aikatar Ayyuka da Gidaje ta Nijeriya, Babatunde Fashola, wanda Daraktan kula da manyan hanyoyi- Mr Celestine Shuwusu ya wakilta ya bayyana farin-ciki dangane da yadda ma’aikatar ta fara aikin kana ta kammala tare da mika shi cikin nasara.

Labarai Masu Nasaba

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya

Bugu da qari kuma, Mista Fashola ya yaba da cikakken hadin kan ma’aikatar kuxi ta tarayya, zauren majisar dokoki ta qasa, musamman shugaban kwamitin ayyuka na majisa bisa goyon bayan da suka bayar wajen kammala aikin.

Haka zalika ya yaba wa ma’aikatansa, yan kwangila tare da yankunan da aka gudanar da aikin hanyar bisa hadin kai da goyon baya.

Da yake jawabi a bukin bude sabuwar hanyar, Gwamnan jihar Yobe, Mai Mala Buni ya bayyana kaddamar da bude hanyar a matsayin muhimmin tarihi ga al’umar jihar sabanin irin yadda cikin shekaru da yawa gwamnatocin baya suka mayar da jihar saniyar ware.

Bugu da kari gwamna Buni ya bayyana muhimmancin shimfida hanyoyi wajen bunkasa tattalin arziki da raya birane da yankunan karkara.

Kazalika, Gwamna Buni ya yaba wa gwamnatin Muhammadu Buhari dangane da namijin kokari wajen dawo da zaman lafiya mai dorewa a yankin.

A hannu guda kuma Buni ya jinjina wa sashen zartaswa dangane da amincewa da dawo wa da gwamnatin jihar Yobe Naira Biliyan 18 da ta kashe wajen gina hanyoyi mallakain gwamnatin tarayya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Uwa Ta Yi Shahada Bayan Karya Dan Bindiga Da Tabarya Wajen Kare Danta

Next Post

A Karon Farko, ‘Yan Ta’adda Sun Farmaki Tawagar Buhari

Related

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa
Kananan Labarai

Gamayyar kungiyoyin Seyi Tinubu (STSG) Na Shirin Gangamin Taronta Na Kasa

3 months ago
Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya
Kananan Labarai

Gwamnati Ta Ware Wata 14 Don Kammala Aikin Hanyar Abuja Zuwa Zariya

5 months ago
Ƙarin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arziƙin Duniya
Kananan Labarai

Ƙarin Harajin Amurka Zai Illata Tattalin Arziƙin Duniya

5 months ago
Gwamnati Ta Amince Da Bai Wa Jami’o’i 11 Masu Zaman Kansu Lasisi
Kananan Labarai

Gwamnati Ta Amince Da Bai Wa Jami’o’i 11 Masu Zaman Kansu Lasisi

6 months ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Kananan Labarai

Nijeriya Za Ta Ci Gajiyar Dala Tiriliyan 7 A Tsarin Kasuwancin Musulunci Na Duniya

12 months ago
Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Aikin Sake Gina Asibitin Talata Mafara
Labarai

Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Aikin Sake Gina Asibitin Talata Mafara

12 months ago
Next Post
A Karon Farko, ‘Yan Ta’adda Sun Farmaki Tawagar Buhari

A Karon Farko, ‘Yan Ta’adda Sun Farmaki Tawagar Buhari

LABARAI MASU NASABA

Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 

Kungiyar Kare Shirye-shiryen Tinubu Ta Nemi A Dakatar Da Shugaban Kamfanin NNPCL 

September 3, 2025
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

September 3, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Ba Abin Da Zai Hana Tinubu Sake Lashe Zaɓe A 2027 – Jigon APC

September 3, 2025
Ya Kamata El-Rufai Ya Yi Bayani Kan Zargin Gwamnati Na Biyan ‘Yan Bindiga KuÉ—aÉ—e – Datti

Ya Kamata El-Rufai Ya Yi Bayani Kan Zargin Gwamnati Na Biyan ‘Yan Bindiga KuÉ—aÉ—e – Datti

September 3, 2025
Mauludi: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar Juma’a A Matsayin Hutu

Mauludi: Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Ranar Juma’a A Matsayin Hutu

September 3, 2025
Shugaba Xi Ya Yi Kira Da A Rungumi Daidaito Da Adalci

Shugaba Xi Ya Yi Kira Da A Rungumi Daidaito Da Adalci

September 3, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Ci Yankuna Da Dama A Katsina

Jihohi 18 A Arewa Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Satumba – NiHSA

September 3, 2025
Xi Jinping Ya Duba Faretin Rundunonin Sojoji Da Kayayyakin Soja, Shugabannin Kasashe 26 Su Ma Sun Halarci Bikin

Xi Jinping Ya Duba Faretin Rundunonin Sojoji Da Kayayyakin Soja, Shugabannin Kasashe 26 Su Ma Sun Halarci Bikin

September 3, 2025
Xi Jinping: Tuna Tarihi Da Martaba ’Yan Mazan Jiya Martaba Zaman Lafiya Da Gina Makoma Mai Kyau 

Xi Jinping: Tuna Tarihi Da Martaba ’Yan Mazan Jiya Martaba Zaman Lafiya Da Gina Makoma Mai Kyau 

September 3, 2025
NAFDAC Ta Gano Wasu Jabun Allurai A Kasuwanni, Ta Gargaɗi Jama’a Kan Amfani Da Su

NAFDAC Ta Gano Wasu Jabun Allurai A Kasuwanni, Ta Gargaɗi Jama’a Kan Amfani Da Su

September 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.