• English
  • Business News
Sunday, May 11, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Sha Alwashin Karin Goyon Baya Ga Dakarun Soji A Kokarinsu Na Yaki Da Ta’addanci

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Yajin Aikin ASUU: Kamata Ya Yi Buhari Ya Fara La’akari Da Rahotan Briggs —Kungiyar Iyaye
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar Alhamis a Jaji da ke jihar Kaduna ya jinjina tare da irin sadaukarwa gami da nasarorin da dakarun sojin kasar nan suke samu wajen kare kasar nan da kuma jajircewarsu.

Da yake jawabi a wajen yaye dalibai 247 na manyan kwas 44 ta Kwalejin horar da jami’an soji da ke Jaji, shugaba ta cikin sanarwar da hadiminsa Garba Shehu ya fitar, Buhari ya sha alwashin cewa, gwamnatinsa za ta cigaba da samar wa dakarun Sojoji abubuwan da suke bukata na goyon baya wajen cigaba da yakar ‘yan ta’adda da ta’addanci.

  • Na Yi Takaicin Zama Ministan Matasa Da Wasanni A Gwamnatin Buhari —Solomon Dalung

‘‘Sojojin Nijeriya su na aiki tukuru da kwarewa da gogewar da suke da su wajen shafe barazanar tsaro da kare kasar nan.

“Kokarin sojojin kasa na yaki da ‘yan Boko Haram, ‘yan bindiga, masu garkuwa da mutane, da sauran matsalolin tsaro abun jinjina da yabawa ne. Tababs sojojin mu na kokari.

“Wannan Gwamnatin za ta ci gaba da samar da dukkanin abubuwan da Sojoji ke bukata da goya musu baya domin cimma nasarorin da aka sanya a gaba,” ya shaida.

Labarai Masu Nasaba

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

Shugaban ya ce matsalolin tsaro da ake fama da shi a duniya baki daya ma na samo asali ne bisa dalilai daban-daban. Don haka ya ce akwai bukatar kara sanya tsaro a iyakokin kasar nan domin dakile aniyar ‘yan ta’adda.

Daga bisani ya taya wadanda aka yaye murna tare da jawo hankalinsu da su bada tasu gudunmawar wajen kare kasar nan a kowani lokaci.

A jawabinsa na maraba, Kwamandan Kwalejin, Air Vice Marshall (AVM) Olurotimi Tuwase, ya yi bayanin cewa sojoji 111 ne, 69 sojojin ruwa ne, 42 kuma Sojoji sama ne, da kuma wasu karin daliban da aka yaye da suka samu horo daban-daban ciki har da dalibai daga kasashen waje.

AVM Tuwase ya kara da cewa, daliban da aka yaye kan kwas din 44 sun fito daga kasashen Burkina Faso, Cameroun, Chad, The Gambia, Ghana, Liberia, Mali, Niger, Rwanda, Sierra Leone, Tanzania, Togo da Zambia.

Kwamandan ya gode wa shugaban kasa Buhari a bisa irin goyon bayan da yake basu da karfafawa musu guiwa a kowani lokaci.

A wajen taron Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya mika lambar yabo ga daliban da suka yi zarra a cikin wadanda aka yaye din.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Karya Fure Take Ba Ta ’Ya’ya

Next Post

Kasashen Yammacin Duniya Ne Suka Kirkiro Batun Tarkon Bashin Sin Kan Kasashen Afrika

Related

Labarai

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

11 hours ago
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)
Labarai

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

12 hours ago
Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu
Labarai

Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

14 hours ago
Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama
Labarai

Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

15 hours ago
Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don YaÆ™i Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Zulum Ya Haramta Sayar Da Fetur A Bama Don YaÆ™i Da Ta’addanci

17 hours ago
Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2
Labarai

Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2

18 hours ago
Next Post
Kasashen Yammacin Duniya Ne Suka Kirkiro Batun Tarkon Bashin Sin Kan Kasashen Afrika

Kasashen Yammacin Duniya Ne Suka Kirkiro Batun Tarkon Bashin Sin Kan Kasashen Afrika

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

Tawagar Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Farko Ta Sin Ta Dawo Daga Abyei Cikin Nasara

May 10, 2025
An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

An Fara Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Matakin Koli Tsakanin Sin Da Amurka A Geneva

May 10, 2025
Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

Sharhi: Sin Da Rasha Suna Sauke Nauyin Dake Wuyansu

May 10, 2025

Kungiyar Malaman Jami’o’i Ta Ba Dalibai 164 Tallafin Karatu

May 10, 2025
Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)

May 10, 2025
Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

Sin Ta Nemi Indiya Da Pakistan Su Muhimmanta Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali

May 10, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow

May 10, 2025
Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

Ra’ayin Al’umma Game Da Iyaye Masu Furta Muggan Kalamai A Kan ‘Ya’yansu

May 10, 2025
Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

Wayar Salula Na Dab Da Kai Mu Wutar Jahannama

May 10, 2025
Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

Martanin Kwankwaso Ga Kawu Sumaila Da Sauran Masu Ficewa Daga NNPP

May 10, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.