• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Sha Alwashin Karin Goyon Baya Ga Dakarun Soji A Kokarinsu Na Yaki Da Ta’addanci

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Yajin Aikin ASUU: Kamata Ya Yi Buhari Ya Fara La’akari Da Rahotan Briggs —Kungiyar Iyaye
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar Alhamis a Jaji da ke jihar Kaduna ya jinjina tare da irin sadaukarwa gami da nasarorin da dakarun sojin kasar nan suke samu wajen kare kasar nan da kuma jajircewarsu.

Da yake jawabi a wajen yaye dalibai 247 na manyan kwas 44 ta Kwalejin horar da jami’an soji da ke Jaji, shugaba ta cikin sanarwar da hadiminsa Garba Shehu ya fitar, Buhari ya sha alwashin cewa, gwamnatinsa za ta cigaba da samar wa dakarun Sojoji abubuwan da suke bukata na goyon baya wajen cigaba da yakar ‘yan ta’adda da ta’addanci.

  • Na Yi Takaicin Zama Ministan Matasa Da Wasanni A Gwamnatin Buhari —Solomon Dalung

‘‘Sojojin Nijeriya su na aiki tukuru da kwarewa da gogewar da suke da su wajen shafe barazanar tsaro da kare kasar nan.

“Kokarin sojojin kasa na yaki da ‘yan Boko Haram, ‘yan bindiga, masu garkuwa da mutane, da sauran matsalolin tsaro abun jinjina da yabawa ne. Tababs sojojin mu na kokari.

“Wannan Gwamnatin za ta ci gaba da samar da dukkanin abubuwan da Sojoji ke bukata da goya musu baya domin cimma nasarorin da aka sanya a gaba,” ya shaida.

Labarai Masu Nasaba

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Shugaban ya ce matsalolin tsaro da ake fama da shi a duniya baki daya ma na samo asali ne bisa dalilai daban-daban. Don haka ya ce akwai bukatar kara sanya tsaro a iyakokin kasar nan domin dakile aniyar ‘yan ta’adda.

Daga bisani ya taya wadanda aka yaye murna tare da jawo hankalinsu da su bada tasu gudunmawar wajen kare kasar nan a kowani lokaci.

A jawabinsa na maraba, Kwamandan Kwalejin, Air Vice Marshall (AVM) Olurotimi Tuwase, ya yi bayanin cewa sojoji 111 ne, 69 sojojin ruwa ne, 42 kuma Sojoji sama ne, da kuma wasu karin daliban da aka yaye da suka samu horo daban-daban ciki har da dalibai daga kasashen waje.

AVM Tuwase ya kara da cewa, daliban da aka yaye kan kwas din 44 sun fito daga kasashen Burkina Faso, Cameroun, Chad, The Gambia, Ghana, Liberia, Mali, Niger, Rwanda, Sierra Leone, Tanzania, Togo da Zambia.

Kwamandan ya gode wa shugaban kasa Buhari a bisa irin goyon bayan da yake basu da karfafawa musu guiwa a kowani lokaci.

A wajen taron Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya mika lambar yabo ga daliban da suka yi zarra a cikin wadanda aka yaye din.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Karya Fure Take Ba Ta ’Ya’ya

Next Post

Kasashen Yammacin Duniya Ne Suka Kirkiro Batun Tarkon Bashin Sin Kan Kasashen Afrika

Related

Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye
Labarai

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

49 minutes ago
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis
Manyan Labarai

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

2 hours ago
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku
Manyan Labarai

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

3 hours ago
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja
Labarai

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

5 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

6 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

15 hours ago
Next Post
Kasashen Yammacin Duniya Ne Suka Kirkiro Batun Tarkon Bashin Sin Kan Kasashen Afrika

Kasashen Yammacin Duniya Ne Suka Kirkiro Batun Tarkon Bashin Sin Kan Kasashen Afrika

LABARAI MASU NASABA

Yadda Muka Zama Bayin ‘Yan Bindiga -Mazaunin Wani Kauye

’Yan Bindiga Sun Sako Ma’aurata A Katsina Bayan Karɓar N50m A Matsayin Kuɗin Fansa

September 18, 2025
Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

Yadda Ribas Ta Yi Cikar Ƙwari Yayin Da Gwamna Fubara Ya Koma Ofis

September 18, 2025
Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

September 18, 2025
’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

’Yansanda Sun Kama Mutane 9 Kan Yin Ƙaryar Sace Su A Jihar Neja

September 18, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Cafke Babban Kwamandan IPOB

September 18, 2025
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

September 17, 2025
Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

Yawan Kadarorin Kamfanoni Mallakar Gwamnatin Sin Ya Wuce Yuan Triliyan 90 a Lokacin Shirin Raya Kasa Na 14 Na Shekaru 5 

September 17, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

Gwamnatin Tarayya Ta Dawo Da Karatun Tarihi A Makarantu

September 17, 2025
Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

Yakin Haraji Da Cinikayya Ba Zai Gurgunta Fifikon Da Sin Ke Da Shi A Fannin Raya Masana’antun Sarrafa Hajoji Da Kasar Ta Gina A Tsawon Lokaci Ba

September 17, 2025
Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

Manyan Ma’aikatan FIRS 4 Sun Rasu Sakamakon Gobarar Da Ta Tashi A Ginin Afriland A Legas 

September 17, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.