ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Buhari Ya Sha Alwashin Karin Goyon Baya Ga Dakarun Soji A Kokarinsu Na Yaki Da Ta’addanci

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Buhari

Shugaban kasa Muhammadu Buhari a ranar Alhamis a Jaji da ke jihar Kaduna ya jinjina tare da irin sadaukarwa gami da nasarorin da dakarun sojin kasar nan suke samu wajen kare kasar nan da kuma jajircewarsu.

Da yake jawabi a wajen yaye dalibai 247 na manyan kwas 44 ta Kwalejin horar da jami’an soji da ke Jaji, shugaba ta cikin sanarwar da hadiminsa Garba Shehu ya fitar, Buhari ya sha alwashin cewa, gwamnatinsa za ta cigaba da samar wa dakarun Sojoji abubuwan da suke bukata na goyon baya wajen cigaba da yakar ‘yan ta’adda da ta’addanci.

  • Na Yi Takaicin Zama Ministan Matasa Da Wasanni A Gwamnatin Buhari —Solomon Dalung

‘‘Sojojin Nijeriya su na aiki tukuru da kwarewa da gogewar da suke da su wajen shafe barazanar tsaro da kare kasar nan.

ADVERTISEMENT

“Kokarin sojojin kasa na yaki da ‘yan Boko Haram, ‘yan bindiga, masu garkuwa da mutane, da sauran matsalolin tsaro abun jinjina da yabawa ne. Tababs sojojin mu na kokari.

“Wannan Gwamnatin za ta ci gaba da samar da dukkanin abubuwan da Sojoji ke bukata da goya musu baya domin cimma nasarorin da aka sanya a gaba,” ya shaida.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

Shugaban ya ce matsalolin tsaro da ake fama da shi a duniya baki daya ma na samo asali ne bisa dalilai daban-daban. Don haka ya ce akwai bukatar kara sanya tsaro a iyakokin kasar nan domin dakile aniyar ‘yan ta’adda.

Daga bisani ya taya wadanda aka yaye murna tare da jawo hankalinsu da su bada tasu gudunmawar wajen kare kasar nan a kowani lokaci.

A jawabinsa na maraba, Kwamandan Kwalejin, Air Vice Marshall (AVM) Olurotimi Tuwase, ya yi bayanin cewa sojoji 111 ne, 69 sojojin ruwa ne, 42 kuma Sojoji sama ne, da kuma wasu karin daliban da aka yaye da suka samu horo daban-daban ciki har da dalibai daga kasashen waje.

AVM Tuwase ya kara da cewa, daliban da aka yaye kan kwas din 44 sun fito daga kasashen Burkina Faso, Cameroun, Chad, The Gambia, Ghana, Liberia, Mali, Niger, Rwanda, Sierra Leone, Tanzania, Togo da Zambia.

Kwamandan ya gode wa shugaban kasa Buhari a bisa irin goyon bayan da yake basu da karfafawa musu guiwa a kowani lokaci.

A wajen taron Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya mika lambar yabo ga daliban da suka yi zarra a cikin wadanda aka yaye din.

Buhari
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Jami’an Tsaro Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 4, Sun Ceto Uwa Da Ɗanta A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

MASU ALAKA

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Labarai

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana
Labarai

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Next Post
Kasashen Yammacin Duniya Ne Suka Kirkiro Batun Tarkon Bashin Sin Kan Kasashen Afrika

Kasashen Yammacin Duniya Ne Suka Kirkiro Batun Tarkon Bashin Sin Kan Kasashen Afrika

LABARAI MASU NASABA

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 13, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026
Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

Shugaban Majalisar Bayar Da Shawara Kan Harkokin Siyasa Ta Kasar Sin Ya Yi Kira Da A Raya Dangantakar Gabobi Biyu Na Mashigin Tekun Taiwan Cikin Lumana

June 13, 2026
Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

Ghana Za Ta Kai Ƙarar Canada Kotu Kan Hana Thomas Partey Shiga Ƙasar

June 13, 2026
Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.