Tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya taya Shugaba Bola Tinubu murna yayin da gwamnatin sa ke cika shekaru biyu a mulki, tare da jan hankalin ‘yan Nijeriya da su takaita tsammaninsu daga gwamnati, yana mai cewa, “gyare-gyare ba sa yin tasiri cikin dare daya.”
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Garba Shehu, ya fitar, Buhari ya bukaci a ci gaba da goyon bayan gwamnatin APC, yana mai gargadi cewa kada a bar matsin lamba na siyasar cikin gida ya hana aiwatar da sauye-sauyen da ake bukata.
- Tinubu Ya Yi Ƙoƙari, Gyaran Nijeriya Aikin Kowa Da Kowa Ne – Buhari
- Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Amso Bashin $21.5bn Da ₦757.9bn
Sanarwar mai taken “Tinubu Ya Samu Yabon Buhari da Shawararsa a bikin cika shekaru biyu” ta bayyana cewa matsalolin da suka hada da talauci da hauhawar farashin kaya—wadanda suka fi shafar talakawa — gwamnati kadai ba za ta iya magance su ba.
Tun daga hawansa mulki a ranar 29 ga Mayu, 2023, gwamnatin Tinubu ta kawo manyan sauye-sauye ciki har da:
- Kawo karshen tallafin man fetur,
- Daidaita dokar musayar kuɗi (liberalisation of Naira),
- Biyan bashin COVID-19 na dala biliyan $3.4 gaba ɗaya,
Sai dai hakan ya janyo matsanancin hauhawar farashi da tsadar rayuwa a cikin gida.
A ranar 23 ga Mayu, 2025, jam’iyyar APC ta bayyana Tinubu a hukumance a matsayin dan takararta guda daya tilo don zaben 2027, duk da fuskantar sauyin ‘yan siyasa daga jam’iyyu daban-daban.
Buhari ya jinjina wa kokarin Tinubu wajen rage talauci da hauhawar farashin kayayyaki, yana mai kira ga fannoni masu zaman kansu da daukacin ‘yan ƙasa da su ba da gudunmawarsu.
Ya kammala da cewa: “Ina taya Shugaba Tinubu murnar cikar shekaru biyu a ofishi. Allah ya ci gaba da ba ka hikima da tausayi wajen jagoranci. Mu kuma mu rage tsammaninmu daga gwamnati.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp