• English
  • Business News
Sunday, October 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

by Leadership Hausa
2 months ago
Cibiyoyi

Samar da Cibiyoyin gudanar da bincike a daukacin fadin duniya, domin samar da ci gaba, na da matukar mahimmanci.

Hakan ne ya sanya kasashen ke ware dimbin kudaden a kai akai ga irin wadannan Cibiyoyin domin a ci gaba da gudanar da yin binciken.

  • EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
  • Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sai dai, abin dubi a nan shi ne, ba wai kawai zuba kudaden domin gudanar da binciken ne ke da matsala ba, amma yadda za a tattala kudaden domin gudanar da binciken shi ne, babban abin da ya wajaba a mayar da hankali akai.

An ruwaito cewa, a kwanan baya, Gwamnatin Tarayya ta amince da a fitar da Naira biliyan 4.2 domin a gudanar da ayyukan yin bincike guda 158.

Wannan binciken, za a gudanar da shi ne, a karkashin Gidauniyar dake tallafawa makarantun dake gaba da sakandare watoTETFund.

LABARAI MASU NASABA

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Za a zuba kudin a aikin gudanar da binciken na kasa wato NRF na shekarar 2024.

Kazalika, a cikin sanawar da Gidauniyar ta fitar, ta nuna cewa, Gwamnatin ta kuma amince da a bayar da wasu kwangiloli na kafa guraren gudanar da binciken fasahar zamani da kuma guraren gudanar da kasuwanci guda 18.

Gwamantin ta amince da kafa su ne, biyo bayan shawarin da Gidauniyar ta bayar na a kafa su, shiyoyi shida na kasar nan, a karkashin daukin na 2024.

Daga cikin ayyukan da za a yi sun hada da bunkasa rukunin kananan gidaje a yankunan da ke a kasar, habaka samar da takin zamani mai inganci da bunkasa shirin magance Ciyawa a gonakai da bai wa Masara da aka shuka kariya daga harbin cutuka da sauransu.

Sai dai, damuwar wannan Jaridar shi ne, akasarin wadannan binciken ka kawai karewa da wallafa su ne, a Mujallun Makarantu, ba tare da wanzar da binciken, a zahirance ba, musamman domin amfanin ‘yan Nijeriya.

Bugu da kari, bayanan kwana-kwanan na Bankin Duniya sun nuna cewa, ba a wanzar da binciken a aikace, saboda sauye-sayen da ake samu a kasar.

Wannan matsalar za a iya cewa, na faruwa ne, saboda gibin da ake samu a tsakanin gudanar da bincike da tsari da kuma rashin wanzarwa.

A cewar sanarwar, Nijeriya na fuskanar kalubale a wajen wanzar bincike da kuma batun da ya shafi ci gaba, musamman wajen fadada alfanunun da wadannan batutuwan suke da shi, ga habaka tattalin arzikin kasar.

Matukar ba a gudanar da bincike, za a ci gaba da kasance wa a gidan jiya a kasar.

A cewar Hukumar Kula da Kididdiga ta Kasa NBS, a faro gudanar da yin bincike na hadaka ne kan kimmiyar 1970, wato a lokacin da aka kafa Cibiyar Binciken kimiyya da Fasha ta NCST.

Amma bayan Cibiyar ta NCST ta shafe shekaru shida da kafuwa, an ta samun korafe-korafe, kan banbancin batun bunkasa tattalin arzikin kasa.

Daga baya, a 1973, daukacin sassan gudanar da bincike da ke a ma’aikataun Gwamnati, sun koma a matsayin Cibiyoyi masu cin gashin kansu.

Kasar nan na da sama da Cibiyon gudanar da bincike guda 66 wadanda akasarinsu, Gwamnatin Tarayya ce ta kafa su take kuma samar masu da kudade.

Wasu daga cikin wadannan Cibiyoyin na gudanar da kanannan bincike ne, a fannoni kamarsu, Noma da samar da magunguna da sauransu.

Misali, Cibiyar Bincike kan Harkokin Lafiya NIMR, Cibiyar Binciken Magunguna da ci gabansu ta Najeriya, NIPRD, Cibiyar Nazarin Itacen Man Fuskar NIFOR, Cibiyar Ilimin Kimiyya da Bincike ta Kasa NISER.

Wadannan Ciboyoyin ciki har da na Jami’oin kasar da kuma sauran sassan gudanar da bincike da ke a karkashin hukomin Gwamnati, maufarsu shi ne, su kara bunkasa fannin ilomin Boko da habaka dabari tare da kuma yin amfani da sakamakon bincken da aka gudanar domin samar da mafita.

Gidauniyar da ke bayar da tallafin kiwon lafiya ta Grandbille Medical And Laser, ta bayyana cewa, fannin kiwon lafiya na kasar nan na fama da dimbin manyan kalubale ciki har da cutukan da ke harbin bil Adama da sauran cutukan da ba a iya yada su.

Manyan cutukan su ne, zazzabin cizon Sauro, Kanjamau, Tarin Fuka, Amai da Gudawa, mutuwar Jarirai, cutar Daji da sauransu, wadanda kuma suke ci gaba da yaduwa a kasar.

Koda yake dai, Nijeriya na samar da kayan gwajin cutar ta Kanjamau tare da yunkurin samar da magungunan da ke rage radadin cutar, amma abin takaicin, masu gudanar da bincike ba su iya yin wani abin azo a gani ba, a binciken na su.

Akasarin, ana danganta matsalar gudanar da binciken na rashin samar da wadattaun kudade, wanda hakan ya sanya, ba a samun wani sakamako.

Bangaren samar da magungunan gargajiya, fanni ne, na kasuwanci da ke kunshe da miliyoyin dala a daukacin fadin duniya, wanda aka kiyasata cewa, hada-hadar kasuwancin fannin, ta kai ta sama da dala biliyan 100.

Ya kamata a ce, wannan fannin ya janyo hankulan masu gudanar da bincike da ke a kasar, amma muna ganin cewa, hakan na faruwa ne, saboda rashin hada karfi da karfe, a tsakanin Cibiyoyin gudanar da bincike da kuma masana’antar ta sarrafa magungunan na gargajiya da ke a kasar.

Ra’ayin wannan Jaridar shi ne, masu gudanar da bincike na bayar da gagarumar gudunmawa wajen kara bunkasa tattalin aziki da inganta kiwon lafiya da rage yin dogaro kan kayan kimiyar zamani, da ake shigowa da su cikin kasar.

A nan, zamu iya cewa, ya zama wajbi masu gudanar da bincike a kasar nan da su amfani da basirarsu domin a ciyar da Nijeriya gaba a fanin bincike, musamman domin a samar da makoma mai kyau, domin amfanin daukacin ‘yan kasar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji
Manyan Labarai

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI
Manyan Labarai

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka
Kiwon Lafiya

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025
Next Post
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

LABARAI MASU NASABA

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

An Yi Liyafar Murnar Kebe Ranar Tunawa Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan

October 25, 2025

Nafisa Abdullahi Aminu: Yarinyar Da Ta Ɗaukaka Darajar Nijeriya A Idon Duniya

October 25, 2025
Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

Sin Da Amurka Sun Fara Tattaunawa Kan Tattalin arziki Da Cinikayya A Kuala Lumpur

October 25, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Banki Na Shekarar 2025 Bankin Providus

October 25, 2025
Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

Firaministan Sin Ya Isa Singapore Don Ziyarar Aiki

October 25, 2025
Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

Gwarzuwar Hukumar Da Ta Kawo Sauyi A Kula Da Muhalli A 2025 Hukumar NASENI

October 25, 2025
An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

An Gudanar Da Taron Cika Shekaru 80 Da Kawo Karshen Mulkin Mallakar Japan A Yankin Taiwan Da Dawo Da Shi Kasar Sin A Beijing

October 25, 2025

Daɓid Adeyemi

October 25, 2025
Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

Wakilin Sin: Shawarar GGI Ta Nuna Yadda Za A Jagoranci Bunkasa Makomar MDD

October 25, 2025
Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

Gwarzuwar Ma’aikaciyar Jinya Ta Shekarar 2025: Misis Mabel Ijeoma Duaka

October 25, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.