• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

by Leadership Hausa
1 month ago
in Manyan Labarai
0
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Samar da Cibiyoyin gudanar da bincike a daukacin fadin duniya, domin samar da ci gaba, na da matukar mahimmanci.

Hakan ne ya sanya kasashen ke ware dimbin kudaden a kai akai ga irin wadannan Cibiyoyin domin a ci gaba da gudanar da yin binciken.

  • EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
  • Sin Ta Maida Martani Ga Yiwuwar Daukar Matakin Sojan Amurka A Kan Venezuela

Sai dai, abin dubi a nan shi ne, ba wai kawai zuba kudaden domin gudanar da binciken ne ke da matsala ba, amma yadda za a tattala kudaden domin gudanar da binciken shi ne, babban abin da ya wajaba a mayar da hankali akai.

An ruwaito cewa, a kwanan baya, Gwamnatin Tarayya ta amince da a fitar da Naira biliyan 4.2 domin a gudanar da ayyukan yin bincike guda 158.

Wannan binciken, za a gudanar da shi ne, a karkashin Gidauniyar dake tallafawa makarantun dake gaba da sakandare watoTETFund.

Labarai Masu Nasaba

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Za a zuba kudin a aikin gudanar da binciken na kasa wato NRF na shekarar 2024.

Kazalika, a cikin sanawar da Gidauniyar ta fitar, ta nuna cewa, Gwamnatin ta kuma amince da a bayar da wasu kwangiloli na kafa guraren gudanar da binciken fasahar zamani da kuma guraren gudanar da kasuwanci guda 18.

Gwamantin ta amince da kafa su ne, biyo bayan shawarin da Gidauniyar ta bayar na a kafa su, shiyoyi shida na kasar nan, a karkashin daukin na 2024.

Daga cikin ayyukan da za a yi sun hada da bunkasa rukunin kananan gidaje a yankunan da ke a kasar, habaka samar da takin zamani mai inganci da bunkasa shirin magance Ciyawa a gonakai da bai wa Masara da aka shuka kariya daga harbin cutuka da sauransu.

Sai dai, damuwar wannan Jaridar shi ne, akasarin wadannan binciken ka kawai karewa da wallafa su ne, a Mujallun Makarantu, ba tare da wanzar da binciken, a zahirance ba, musamman domin amfanin ‘yan Nijeriya.

Bugu da kari, bayanan kwana-kwanan na Bankin Duniya sun nuna cewa, ba a wanzar da binciken a aikace, saboda sauye-sayen da ake samu a kasar.

Wannan matsalar za a iya cewa, na faruwa ne, saboda gibin da ake samu a tsakanin gudanar da bincike da tsari da kuma rashin wanzarwa.

A cewar sanarwar, Nijeriya na fuskanar kalubale a wajen wanzar bincike da kuma batun da ya shafi ci gaba, musamman wajen fadada alfanunun da wadannan batutuwan suke da shi, ga habaka tattalin arzikin kasar.

Matukar ba a gudanar da bincike, za a ci gaba da kasance wa a gidan jiya a kasar.

A cewar Hukumar Kula da Kididdiga ta Kasa NBS, a faro gudanar da yin bincike na hadaka ne kan kimmiyar 1970, wato a lokacin da aka kafa Cibiyar Binciken kimiyya da Fasha ta NCST.

Amma bayan Cibiyar ta NCST ta shafe shekaru shida da kafuwa, an ta samun korafe-korafe, kan banbancin batun bunkasa tattalin arzikin kasa.

Daga baya, a 1973, daukacin sassan gudanar da bincike da ke a ma’aikataun Gwamnati, sun koma a matsayin Cibiyoyi masu cin gashin kansu.

Kasar nan na da sama da Cibiyon gudanar da bincike guda 66 wadanda akasarinsu, Gwamnatin Tarayya ce ta kafa su take kuma samar masu da kudade.

Wasu daga cikin wadannan Cibiyoyin na gudanar da kanannan bincike ne, a fannoni kamarsu, Noma da samar da magunguna da sauransu.

Misali, Cibiyar Bincike kan Harkokin Lafiya NIMR, Cibiyar Binciken Magunguna da ci gabansu ta Najeriya, NIPRD, Cibiyar Nazarin Itacen Man Fuskar NIFOR, Cibiyar Ilimin Kimiyya da Bincike ta Kasa NISER.

Wadannan Ciboyoyin ciki har da na Jami’oin kasar da kuma sauran sassan gudanar da bincike da ke a karkashin hukomin Gwamnati, maufarsu shi ne, su kara bunkasa fannin ilomin Boko da habaka dabari tare da kuma yin amfani da sakamakon bincken da aka gudanar domin samar da mafita.

Gidauniyar da ke bayar da tallafin kiwon lafiya ta Grandbille Medical And Laser, ta bayyana cewa, fannin kiwon lafiya na kasar nan na fama da dimbin manyan kalubale ciki har da cutukan da ke harbin bil Adama da sauran cutukan da ba a iya yada su.

Manyan cutukan su ne, zazzabin cizon Sauro, Kanjamau, Tarin Fuka, Amai da Gudawa, mutuwar Jarirai, cutar Daji da sauransu, wadanda kuma suke ci gaba da yaduwa a kasar.

Koda yake dai, Nijeriya na samar da kayan gwajin cutar ta Kanjamau tare da yunkurin samar da magungunan da ke rage radadin cutar, amma abin takaicin, masu gudanar da bincike ba su iya yin wani abin azo a gani ba, a binciken na su.

Akasarin, ana danganta matsalar gudanar da binciken na rashin samar da wadattaun kudade, wanda hakan ya sanya, ba a samun wani sakamako.

Bangaren samar da magungunan gargajiya, fanni ne, na kasuwanci da ke kunshe da miliyoyin dala a daukacin fadin duniya, wanda aka kiyasata cewa, hada-hadar kasuwancin fannin, ta kai ta sama da dala biliyan 100.

Ya kamata a ce, wannan fannin ya janyo hankulan masu gudanar da bincike da ke a kasar, amma muna ganin cewa, hakan na faruwa ne, saboda rashin hada karfi da karfe, a tsakanin Cibiyoyin gudanar da bincike da kuma masana’antar ta sarrafa magungunan na gargajiya da ke a kasar.

Ra’ayin wannan Jaridar shi ne, masu gudanar da bincike na bayar da gagarumar gudunmawa wajen kara bunkasa tattalin aziki da inganta kiwon lafiya da rage yin dogaro kan kayan kimiyar zamani, da ake shigowa da su cikin kasar.

A nan, zamu iya cewa, ya zama wajbi masu gudanar da bincike a kasar nan da su amfani da basirarsu domin a ciyar da Nijeriya gaba a fanin bincike, musamman domin a samar da makoma mai kyau, domin amfanin daukacin ‘yan kasar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Cibiyoyi
ShareTweetSendShare
Previous Post

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

Next Post

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Related

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto
Manyan Labarai

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

3 hours ago
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

15 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

17 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

2 days ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

2 days ago
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja
Manyan Labarai

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

2 days ago
Next Post
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

Rundunar ‘Yansanda Ta Kama Wanda Ake Zargi Da Haɗa-baki Kan Sace Mai Anguwa A Kano

October 5, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.