• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Kafa Gwamnatin Hadin Kai

by Leadership Hausa
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Bukatar Kafa Gwamnatin Hadin Kai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar 1 ga watan Maris 2023 ne Hukumar Zabe INEC ta bayyana jam’iyya mai mulki ta APC a matsayin wadanda ta lashe zaben shugaban kasa da aka yi ranar Asabar 25 ga watan Fabrairu 2023.

Tinubu, tsohon gwamnan Jihar Legas wanda ya yi wa APC takara ya samu kuri’u 8,794,726 inda ya kayar da Atiku Abubakar, tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar jam’iyyar PDP wanda ya samu kuri’u 6,984,520.

  • Dan Majalisar Da Ake Nema Ruwa A Jallo Ya Fita Yakin Neman Zabe A Bauchi
  • An Fitar Da Tsarin Yin Kwaskwarima Na JKS Da Hukumomin Gwamnati

Wanda ya zo na uku a zaben shi ne Peter Obi na jam’iyyar LP mai kuri’a 6,101,533 sai kuma Rabiu Musa Kwankwaso na jam’iyyar NNPP wanda ya zo na hudu da kuri’u 1,496,687.

A ranar da aka yi zaben shugaban kasa, ‘yan Nijeriya sun kuma zabi ‘yan majalisun kasa 469, da yawa a cikin su kuma wannan ne karo na farko na shigarsu majalisar.

Amma kuma zaben shugaban kasa, kamar dai yadda aka yi a shekarun baya, a wannan karon ma yana tattare ne da abubuwan da sukia shafi kabilanci da addini, musamman ma ganin dukkan manyan ‘yan takarar su uku sun fito ne daga manyan kabilun kasar nan.

Labarai Masu Nasaba

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

Sannan kuma wadanda suka zo na biyu da na uku duk suna ikirarin sune suka lashe zaben, suna korafin cewa an yi magudi a yayin da ake tattara sakamakon zaben. Baya ga hukuncin kotun da ke sauraren karrarikin zabe da kuma hukuncin da kotun koli za ta iya yankewa daga baya babu wata dokar da za ta iya hana a rantsar da Bola Tinubu a matsayin shugaban Nijeriya a ranar 29 ga watan Mayu 2023.

Da zarar ya dare karagar mulki, zai shiga hidimar zabo ministoci da shugabanin ma’aikatu da za su taimaka masa wajen aiwatar da alkawurran da ya yi wa al’ummar Nijeriya a lokacin da yake yakin neman zabe, shugaban kasan zai kuma iyan tabbatar da ganin wanene zai zama shugaban majalisar dadttawa da kuma ta wakilai. A kan haka ne muke ganin yana da matukar muhimmanci a ra’ayinmu na mu jawo hankalin shugaban kasa Tinubu a kan bukatar a samar da gwamnatin da dukkan bangarorin kasa za su san ana damawa su a cikin gwamnatin da kuma shugabanin majalisar kasa. A siyasance, Tinubu ya kafa harkar siyasan ce a yankin kudu maso yammacin Nijeriya. Kuma kamar yadda ne bayyana da bakinsa, ya kuduri burin zama shugaban kasa ne a dukkan tsawon rayuwarsa. Tabbas wannan burinasa ne ya sanya ya yi watsi da jam’iyyar ACN inda ya shiga hadaka da jam’iyyar APC, jam’iyyar da ke da asali daga yankin arewacin Nijeriya.

A wannan hadakar a gwamnatin da ta gabata, a ware wasu yankuna a yayin zaben shugabanin majalisar kasa, yayin da arewa ta samu shugaban kasa da shugaban majalisar dattawa, yankin kudu maso yamma suka samu mataimaki shugaban kasa da shugaban majalisar wakilai, muna kira ga zabbaben shugaban kasa da kada ya bi wannan hanyar.

Amma daga dukkan alamu, bangaren shugaban kasa basu kammala bukuwan lashe zabe ba, amma sai gashi har an fara gwagwamaryar neman shugabancin majalisan dattawa da kuma ta Wakilai.

Duk da cewa, a boye ake kamun kafar neman shugabancin majalisun biyu, amma al’umma na ganin yadda al’amurran ke tafiya, inda ake yi wa wasu ‘yan majalisar kamun kafa da yawa na amfanin da makaman da ke a hannun su wadanda suka hada da bukatar da yankunan suke cii na neman ayyukan cigaba, zamu ga wasu irin wadannan salon kamun kafar daga masu neman shugabancin majalisar kasa a nan gaba kada.

Akwai wasu tanade-tanade a cikin kundin tsarin mulkin kasa da aka tabbatar da cewa, ba a juya wa wani bangare ko jiha baya ba a harkar gudanar da kasa.  Baya ga tabbatar da shugaban kasa ya zabi Ministoci daga dukkan jihohin tarayyar kasar nan, tsarin mulki ya fayyace yadda za a kafa gwmanatin tarayya da ma na wasu ma’aikatun  gwamnati ta yadda za a tafi tare da kowa da kowa don samar da hadin kan kasa.

Da babu wannan tanadin da Tinubu yana da damar ya zabi ‘yan asalin jiharsa ta Legas su zama ministoci maimakon ya zaba daga jihohi 36 a tarayyar Nijeriya, sai dai a wuraren da ba a samu wadanda suka cancaci rike wani mukami ba daga wata jiha. Doka ta tanadi a rarraba mukamai a tsakanin shiyoyyin siyasa shida na kasar nan don kowa ya san ana damawa da shi. Don haka a kwai bukatar a yi takatsantsan wajen ganin kowacce bangare na kasa ya samu wakilci a dukkan bangarorin gudanar da mukin kasar nan gaba daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin Hadin KaiINECLegasTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dan Majalisar Da Ake Nema Ruwa A Jallo Ya Fita Yakin Neman Zabe A Bauchi

Next Post

Shugaba Xi Jinping Zai Kai Ziyarar Aiki Kasar Rasha

Related

UTME
Manyan Labarai

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

7 hours ago
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu
Manyan Labarai

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

13 hours ago
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Bunƙasa, Amma Farashin Kayayyaki Na Ci Gaba Da Tashi – Bankin Duniya

18 hours ago
Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte
Manyan Labarai

Sojoji 20 Sun Ɓace Bayan Harin Da ISWAP Suka Kai Marte

22 hours ago
Ko Kanawa Za Su Yafe Wa Ganduje?
Manyan Labarai

Kotu Ta Ce Za A Ci Gaba Da Shari’ar Ganduje Kan Zargin Aikata Rashawa A Kano

23 hours ago
Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar
Manyan Labarai

Gwamnan Zamfara Ya Raba Katin ATM Ga Mutane 400,000 Da Suka Ci Gajiyar Shirin ‘Cash Transfer’ A Jihar

2 days ago
Next Post
Shugaba Xi Jinping Zai Kai Ziyarar Aiki Kasar Rasha

Shugaba Xi Jinping Zai Kai Ziyarar Aiki Kasar Rasha

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.