• English
  • Business News
Tuesday, August 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Kafa Gwamnatin Hadin Kai

by Leadership Hausa
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Bukatar Kafa Gwamnatin Hadin Kai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar 1 ga watan Maris 2023 ne Hukumar Zabe INEC ta bayyana jam’iyya mai mulki ta APC a matsayin wadanda ta lashe zaben shugaban kasa da aka yi ranar Asabar 25 ga watan Fabrairu 2023.

Tinubu, tsohon gwamnan Jihar Legas wanda ya yi wa APC takara ya samu kuri’u 8,794,726 inda ya kayar da Atiku Abubakar, tsohon mataimakin shugaban kasa kuma dan takarar jam’iyyar PDP wanda ya samu kuri’u 6,984,520.

  • Dan Majalisar Da Ake Nema Ruwa A Jallo Ya Fita Yakin Neman Zabe A Bauchi
  • An Fitar Da Tsarin Yin Kwaskwarima Na JKS Da Hukumomin Gwamnati

Wanda ya zo na uku a zaben shi ne Peter Obi na jam’iyyar LP mai kuri’a 6,101,533 sai kuma Rabiu Musa Kwankwaso na jam’iyyar NNPP wanda ya zo na hudu da kuri’u 1,496,687.

A ranar da aka yi zaben shugaban kasa, ‘yan Nijeriya sun kuma zabi ‘yan majalisun kasa 469, da yawa a cikin su kuma wannan ne karo na farko na shigarsu majalisar.

Amma kuma zaben shugaban kasa, kamar dai yadda aka yi a shekarun baya, a wannan karon ma yana tattare ne da abubuwan da sukia shafi kabilanci da addini, musamman ma ganin dukkan manyan ‘yan takarar su uku sun fito ne daga manyan kabilun kasar nan.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Kwangilar Hanyoyi 17 Akan Naira Biliyan 40.8

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

Sannan kuma wadanda suka zo na biyu da na uku duk suna ikirarin sune suka lashe zaben, suna korafin cewa an yi magudi a yayin da ake tattara sakamakon zaben. Baya ga hukuncin kotun da ke sauraren karrarikin zabe da kuma hukuncin da kotun koli za ta iya yankewa daga baya babu wata dokar da za ta iya hana a rantsar da Bola Tinubu a matsayin shugaban Nijeriya a ranar 29 ga watan Mayu 2023.

Da zarar ya dare karagar mulki, zai shiga hidimar zabo ministoci da shugabanin ma’aikatu da za su taimaka masa wajen aiwatar da alkawurran da ya yi wa al’ummar Nijeriya a lokacin da yake yakin neman zabe, shugaban kasan zai kuma iyan tabbatar da ganin wanene zai zama shugaban majalisar dadttawa da kuma ta wakilai. A kan haka ne muke ganin yana da matukar muhimmanci a ra’ayinmu na mu jawo hankalin shugaban kasa Tinubu a kan bukatar a samar da gwamnatin da dukkan bangarorin kasa za su san ana damawa su a cikin gwamnatin da kuma shugabanin majalisar kasa. A siyasance, Tinubu ya kafa harkar siyasan ce a yankin kudu maso yammacin Nijeriya. Kuma kamar yadda ne bayyana da bakinsa, ya kuduri burin zama shugaban kasa ne a dukkan tsawon rayuwarsa. Tabbas wannan burinasa ne ya sanya ya yi watsi da jam’iyyar ACN inda ya shiga hadaka da jam’iyyar APC, jam’iyyar da ke da asali daga yankin arewacin Nijeriya.

A wannan hadakar a gwamnatin da ta gabata, a ware wasu yankuna a yayin zaben shugabanin majalisar kasa, yayin da arewa ta samu shugaban kasa da shugaban majalisar dattawa, yankin kudu maso yamma suka samu mataimaki shugaban kasa da shugaban majalisar wakilai, muna kira ga zabbaben shugaban kasa da kada ya bi wannan hanyar.

Amma daga dukkan alamu, bangaren shugaban kasa basu kammala bukuwan lashe zabe ba, amma sai gashi har an fara gwagwamaryar neman shugabancin majalisan dattawa da kuma ta Wakilai.

Duk da cewa, a boye ake kamun kafar neman shugabancin majalisun biyu, amma al’umma na ganin yadda al’amurran ke tafiya, inda ake yi wa wasu ‘yan majalisar kamun kafa da yawa na amfanin da makaman da ke a hannun su wadanda suka hada da bukatar da yankunan suke cii na neman ayyukan cigaba, zamu ga wasu irin wadannan salon kamun kafar daga masu neman shugabancin majalisar kasa a nan gaba kada.

Akwai wasu tanade-tanade a cikin kundin tsarin mulkin kasa da aka tabbatar da cewa, ba a juya wa wani bangare ko jiha baya ba a harkar gudanar da kasa.  Baya ga tabbatar da shugaban kasa ya zabi Ministoci daga dukkan jihohin tarayyar kasar nan, tsarin mulki ya fayyace yadda za a kafa gwmanatin tarayya da ma na wasu ma’aikatun  gwamnati ta yadda za a tafi tare da kowa da kowa don samar da hadin kan kasa.

Da babu wannan tanadin da Tinubu yana da damar ya zabi ‘yan asalin jiharsa ta Legas su zama ministoci maimakon ya zaba daga jihohi 36 a tarayyar Nijeriya, sai dai a wuraren da ba a samu wadanda suka cancaci rike wani mukami ba daga wata jiha. Doka ta tanadi a rarraba mukamai a tsakanin shiyoyyin siyasa shida na kasar nan don kowa ya san ana damawa da shi. Don haka a kwai bukatar a yi takatsantsan wajen ganin kowacce bangare na kasa ya samu wakilci a dukkan bangarorin gudanar da mukin kasar nan gaba daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamnatin Hadin KaiINECLegasTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dan Majalisar Da Ake Nema Ruwa A Jallo Ya Fita Yakin Neman Zabe A Bauchi

Next Post

Shugaba Xi Jinping Zai Kai Ziyarar Aiki Kasar Rasha

Related

Kano
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Kwangilar Hanyoyi 17 Akan Naira Biliyan 40.8

4 hours ago
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

7 hours ago
An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami
Manyan Labarai

An Rufe Kwaleji A Bauchi Bayan Zanga-zangar Ɗalibai Kan Fashi Da Makami

9 hours ago
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku
Manyan Labarai

Jagora A ADC Ya Ƙaryata Zargin Atiku Ya Kankane Komai A Jam’iyyar

10 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Batun Rashin Lafiyar Tinubu

14 hours ago
Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi
Manyan Labarai

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

23 hours ago
Next Post
Shugaba Xi Jinping Zai Kai Ziyarar Aiki Kasar Rasha

Shugaba Xi Jinping Zai Kai Ziyarar Aiki Kasar Rasha

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

‘Yan Bindiga Sun Kai Hari Masallaci Sun Kashe Wani Mutum Da Jikkata Wasu Da Dama A Sokoto

August 12, 2025
Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa

August 12, 2025
Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

Gwamnatin Kano Za Ta Horar Da Tubabbun ‘Yandaba 718 Sana’o’i 

August 12, 2025
Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

Xi: Sin Da Brazil Na Iya Zama Misalin Hadin Kai Da Dogaro Da Kai Ga Kasashe Masu Tasowa

August 12, 2025
Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

Jiragen saman NAF Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 592, Sun Lalata Kayayyakin Yaki 372

August 12, 2025
Ma’aikatar Cinikayya Ta Kasar Sin Ta Yi Karin Haske Kan Batun Saka Wasu Sassa Cikin Wadanda Ta Sanyawa Takunkumin Sayar Musu Da Kayayyaki

Ma’aikatar Cinikayya Ta Kasar Sin Ta Yi Karin Haske Kan Batun Saka Wasu Sassa Cikin Wadanda Ta Sanyawa Takunkumin Sayar Musu Da Kayayyaki

August 12, 2025
Ronaldo Zai Daura Aurensa Na Farko A Rayuwa Tare Da Budurwarsa Georgina

Ronaldo Zai Daura Aurensa Na Farko A Rayuwa Tare Da Budurwarsa Georgina

August 12, 2025
Sin Ta Gabatar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakaninta Da Amurka A Stockholm

Sin Ta Gabatar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Taron Tattalin Arziki Da Cinikayya Tsakaninta Da Amurka A Stockholm

August 12, 2025
Kano

Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Kwangilar Hanyoyi 17 Akan Naira Biliyan 40.8

August 12, 2025
Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

Fasahohin AI Sun Bude Sabon Babi Na Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.