• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Kawo Karshen Mamayar Da Kamaru Ke Yi Wa Yankunan Nijeriya

by Leadership Hausa
3 weeks ago
in Manyan Labarai
0
Bukatar Kawo Karshen Mamayar Da Kamaru Ke Yi Wa Yankunan Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kwanukan baya ne, ‘yan Nijeriya suka shiga cikin fargaba, biyo bayan bayyanar kutsen da wasu gugun ‘yan ta’adda da suka fito daga kasar Kamaru suka yi, a wani jeje da ke a yankin Efiat a karamar hukuma Mbo, ta jihar Akwa Ibom.

Sai dai, a bisa yunkurin daukar matakan gaggawa, Majalisar Dattawa a ranar 18 na watan Maris, ta kafa kwamitin wucin gadi da zai gudanar da bincike kan wannan batun.

  • Manchester Ta Kai Zagayen Semi Final A Europa Bayan Doke Lyon
  • Sin Da Malaysia Za Su Samar Sabbin Shekaru 50 Masu Muhimmanci Na Dangantakar Kasashen Biyu

Majalisar ta kuma bai wa kwatin wa’adin mako biyu, da ya gabatar mata da rahoton binciken da ya gudanar kan wannan lamarin

Kazalika, Majalisar ta kuma bukaci Shugaban Kasa Bola Tinubu, da ya gaggauta daukar matakai, musamman domin a tabbatar da an bai wa sama da Rijiyon Mai da na Iskar Gas 2,560 da ke a yanin.

Kwamtin ya kunshi, mutane kamar su; Sanata Jimoh Ibrahim dan jam’iyyar APC daga Mazabar Ondo ta Kudu wanda shi ne, Shugaban kwamtin.

Labarai Masu Nasaba

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Akwai kuma Sanata Adeniyi Adegbonire dan jam’iyyar APC daga mazabar Ondo ta tsakiya, Sanata Seriake Dickson dan jami’yyar PDP, daga mazabar Bayelsa ta Gabas, Sanata Shehu Lawan Kaka, dan jam’iyyar APC, daga mazabar Borno ta tsakiya.

Sauran sun hada da; Sanata Banigo Ipaligo dan jam’iyyar PDP, daga mazabar Ribas ta Yamma, Sanata Jarigbe Jarigbe dan jami’yyar PDP, daga Koros Riba ta Arewa, Sanata Ekong Sampson dan jami’yyar PDP, daga mazabar Akwa Ibom ta Kudu, Sanata Sani Bello dan jami’yyarAPC, daga mazabar Neja ta Arewa sai kuma Sanata Aniekan Bassey, dan jam’iyyar PDP, daga mazabar Akwa Ibom.

Majalisar ta kafa wannan kwamtin ne, biyo bayan kudurin da Sanata Aniekan Bassey na mazabar Arewa da Gabas daga Akwa Ibom, ya gabatar mata wacce ta yi daidai da dokokin 41 da 51.

Bugu da kari, a cikin kudurin da Sanata Bassey ya gabatar wa da Majalisar Dattawan ya yi gargadi da cewa, kutsen na ‘yan ta’addar daga kasar Kamaru, zai iya shafar tattalin arzikin jihar ta Akwa Ibom

Sanatan ya shedawa Majalisar cewa, yankin na Efiat, da ke a karamar hukumar Mbo a Akwa Ibom, na daga cikin yankin da aka bai wa kasar Kamaru a shekarar 1913, biyo bayan yarjejeniyar Anglo-German ko kuma a hukuncin da yarjejeniyar Babban Kotun Koli ta Duniya Duniya ta yanke a watan Okutobar 2002.

A nan, muna jinjiawa Majalisar ta Dattawa bisa kafa wannan kwamtin mai mambi tara, musamman domin kwamitin ya gudanar da bincike, kan wannan batun, na zargin kutsen ‘yan ta’addar na kasar Kamaru,a wannan yankin.

Sai dai, a wannan lokacin, yana da kyau a ci gaba da tsimayin sakamakon binciken da kuma shawarwarin da kwamtitin zai gabatar wa da Majalisar ta Dattawa kan wannan batun, domin sanin mataki na gaba da za a dauka.

Batu na maganar rikicin kasa, akasari, yana da wuyar lamari, wajen warware wa, musamman duba da cewa, Nijeriya da kasar Kamaru, kasashe ne, da suka gaji iyakoin kasa daga turawan mulkin mallaka, wadanda kuma, tun a baya, ba a fayyace yadda suke ba.

Bugu da kari, wannan lamari ne, mai matukar mahimmanci da ya shafi kasar nan.

Kazalika, ya zama waji, ‘yan Nijeriya su hada kansu, domin kare iyakokin kasar ga dukkan wata barazana, da za ta iya shafar kasar.

Sai dai, damuwar da akasarin ‘yan Nijeriya ke ci gaba da nunawa kan batun shi ne, na rashin mayar da hankali a siyasance, domin lalubo da mafita kan lamari irin wannan.

Mu a nan, muna kira ga Gwamnatin Tarayya da ta kasance mai sanya ido sosai da kuma daukar kwararan matakai da za su kasance ba su kai ga zubar da kimar Nijeriya a idon duniya ba, wajen kare yiwa tattalin arzikin kasar nan.

Hakazalika, ya zama wajbi, Nijeriya ta tashi tsaye, wajen kare kasar daga dukkan wani na’ui na barazana daga kere domin kare kasar nan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KamaruMamayaNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Manchester Ta Kai Zagayen Semi Final A Europa Bayan Doke Lyon

Next Post

Duk Da Matsin Rayuwa: Bankuna Na Ci Gaba Da Cin Kazamar Riba Ta Hanyar Dora Wa Al’umma Haraji

Related

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje
Manyan Labarai

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

11 hours ago
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai
Manyan Labarai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

12 hours ago
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa
Manyan Labarai

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

21 hours ago
Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma
Da É—umi-É—uminsa

Robert Prevost Ya Zama Ba’amurke Na Farko Da Ya Zama Fafaroma

1 day ago
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

1 day ago
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kai Ziyarar Aiki Jihar Anambra

1 day ago
Next Post
Duk Da Matsin Rayuwa: Bankuna Na Ci Gaba Da Cin Kazamar Riba Ta Hanyar Dora Wa Al’umma Haraji

Duk Da Matsin Rayuwa: Bankuna Na Ci Gaba Da Cin Kazamar Riba Ta Hanyar Dora Wa Al’umma Haraji

LABARAI MASU NASABA

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

Haraji: Amurka Ta Kama Hanyar Durkusar Da Kanta

May 9, 2025
Kotu Ta ÆŠage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

Kotu Ta ÆŠage Shari’ar Yahaya Bello Zuwa 26 Ga Yuni Don Yanke Hukunci

May 9, 2025
Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma

May 9, 2025
Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

Hada-hadar Cinikayyar Waje Ta Kasar Sin Ta Karu Da Kaso 5.6 Bisa Dari A Watan Afirilu

May 9, 2025
Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

May 9, 2025
GORON JUMA’A 09/05/2025

GORON JUMA’A 09/05/2025

May 9, 2025
Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.