ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Duk Da Matsin Rayuwa: Bankuna Na Ci Gaba Da Cin Kazamar Riba Ta Hanyar Dora Wa Al’umma Haraji

by Rabi'u Ali Indabawa
1 year ago
Bankuna

Bankunan kasuwanci da wasu kamfanonin kere-kere a Nijeriya sun magance matsalolinsu ta hanyar share fagen samun dimbin riba tare da bayyana ta ga masu hannun jarinsu a shekarar kudi ta 2024.

Sakamakon binciken da LEADERSHIP Sunday ta gudanar ya yi nuni da cewa duk da koma-bayan tattalin arziki da kuma tsadar kayayyaki dake addabar ‘yan Nijeriya a cikin shekarar da ta gabata, tuni yawancin bankuna da kamfanoni suka shawo kan dukkanin wasu matsaloli tare da bayyana dimbin riba, kai har ma da biyan masu hannun jari.

  • Manchester Ta Kai Zagayen Semi Final A Europa Bayan Doke Lyon
  • Yawan Kudaden Da Al’ummun Sin Suka Kashe Kan Kayayyakin Masarufi Ya Kai Yuan Triliyan 12.5 A Rubu’in Farko

Financial edperts and shareholders who spoke with our correspondent edplained that the organisations’ positibe showings arose from fored windfall, as banks found themselbes at the surplus end of policy actions and, hence, realised unprecedented FD windfall and huge income from inbestment in public debt.

ADVERTISEMENT

Misali, kamfanonin siminti na Nijeiya sun bayyana samun ribar da ta kai Naira biliyan 984.432 kafin haraji, sakamakon karuwar girman arziki da kuma gyare-gyaren farashi.

A bangaren banki kuwa, Bankin Zenith, Guaranty Trust Holding Company, United Bank for Africa, Fidelity Bank, Stanbic IBTC Holdings da Wema Bank sun bayyana ribar Naira tiriliyan 3.41 bayan harajin shekarar 2024, an samu sama da Naira tiriliyan 2.1 a shekarar 2023.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Hakazalika, kamfanoni 43 da aka bayyana sun ba da shawarar raba jimillar Naira tiriliyan 1.678 ga masu hannun jarinsu, tare da yaba wa abokan huldarsu.

A cikin 2024, bangarori na kasuwancin Nijeriya ya gamu da kalubale masu yawa na tattalin arziki da samar da ababen more rayuwa wadanda suka yi matukar tasiri ga ayyukansa. Masana’antun sun fuskanci matsin lamba daga hauhawar farashin kayayyaki, faduwar darajar Naira, hauhawar kudin ruwa, karin kudin wutar lantarki, karancin tallace-tallace, yawan haraji da kuma tabarbarewar tsaro.

A cikin wannan babbana al’amari, kamfanoni a manyan sassan tattalin arziki sun ba da rahoton sakamako mai karfi na kamfanoni da kuma bayar da lada ga masu hannun jari.

Idan za a kimanta halin da ake ciki, babban jami’in gudanarwa (Shugaba) na HighCap Securities Limited, Mista Dabid Adonri, ya ce, “Ta hanyar samar da, bankunan sun sami kansu a karshen ayyuka na wasu manufofi, wanda ta haka ne suka fahimci faduwar canjin kasashen da ba a taba gani ba da kuma makudan kudaden shiga daga zuba jari a basussukan jama’a.

“Abin takaici shi ne, sauye-sauyen kasuwanni da matakan tsare-tsare na kudi wadanda ke samar da karuwar kudaden shiga na bankuna sun sanya yawancin masana’antun da suka dogara da shigo da kayayyaki zuwa cikin gida asara, wadanda babu shakka sun yi nasasar shawo kan lamarin, kamar masu samar da siminti, suna da kasuwancinsu na fitar da kayayyaki domin samun daidaito.”

Ya yi nuni da cewa, duk da rauni na kasuwancin kayan masarufi sakamakon hauhawar farashin kayayyaki, bangaren gwamnati na ci gaba da aiwatar da manyan ayyuka, wadanda ke cinye kayayyakin gini da dama. Don haka ne ribar da kamfanoni kamar Dangote Cement da BUA Cement suka bayyana.

“To kuwa tun da aka riga aka bayyana wadannan kamfanoni a bainar jama’a da kuma yadda tsarinsu yake, babu wani dalili da zai musanta ribar da suke samu a ce ba gaskiya ba ce.

Adonri ya ce “Yawancin kamfanoni na Nijeriya suna yin fatali da ci gaban tattalin arzikin kasar da ke tabarbarewa, suna ba da rahoton riba da kuma yawan kudaden da aka samu,” in ji Adonri.

Babban jami’in gudanarwa na InbestData Consulting Limited Ambrose Omordion, ya aminta da cewa “bankuna da sauran kamfanonin Nijeriya suna bayar da rahoton riba mai yawa da kuma kudaden da ake samu duk da tabarbarewar tattalin arzikin kasar da kuma karancin sayayyar kayayyaki.”

Ya lura cewa manyan kamfanoni, musamman a bangaren banki, na iya za su iya tsira daga manyan kalubalen tattalin arzikin da kananan ‘yan kasuwa da daidaikun mutane ke fuskanta.

Ya kara da cewa ” Alal misali, bankuna, na iya samun manyan kudaden shiga daga wasu kwamitoci ko ayyukan sanya hannun jari wadanda ba su da alaka da ainihin kasuwancin ba da lamuni,” in ji shi.

A halin da ake ciki, shugaban Kungiyar Masu Hannun Jari Mai Zaman Kanta ta Nijeriya (ISAN), Moses Igbrude, ya yi nuni da cewa, “Rabon da bankunan ke bayyanawa gaskiya ne, domin harkokin kasuwancinsu na bayar da hidima ne, wanda ke samar da jari don ciyar da tattalin arzikin kasa gaba.

“Ba tare da manyan kudaden da za a inganta tattalin arzikin kasa ba, to ba za a taba samar da wasu dabaru na farfado da shi ba. Tare da kowane ciniki, akwai farashi da ya shafi sakonnin rubutu zuwa riba akan lamuni da aka ba wa abokan ciniki, kuma hakan na ba da ayyuka da yawa ga abokan cinikinsu a duk fadin kasar,” in ji shi.

A halin yanzu dai, shugaban kungiyar masu Masana’antu ta Nijeriya (MAN), Otunba Francis Meshioye ya yi kira da a tallafa wa bangaren masana’antu.

Ya ce, “ A 2025, fannin masana’antu ya ta’allaka ne ga nasarar sauye-sauyen tattalin arziki da ake ci gaba da samu, wadanda suka hada da aiwatar da sauye-sauyen harajin da ake shirin yi, da daidaita muhimman alamomin tattalin arziki, da zuba hannun jari a fannonin ababen more rayuwa da fasaha.

“La’akari da jerin sauye-sauye na kasafin kudi na gwamnatin yanzu, ana sa ran samun saukin tabarbarewar tattalin arzikin da samun wasu ci gaba a wannan shekara tare da kwanciyar hankali a cikin tsarin musayar kudi a 2025.”

Meshioye ya kara da cewa, domin fannin ya dawo da karfinsa, dole ne a ci gaba da kokarin inganta ayyukan da ake yi da kuma kara yin gasa, domin hakan na da matukar muhimmanci wajen taimaka wa masana’antun Nijeriya su shawo kan kalubalen da suke fuskanta.

Meshioye ya ce, “Masana’antu na da muhimmanci wajen bunkasa da kuma dorewar ci gaban tattalin arzikin Nijeriya. Muna neman gwamnati ta daidaita tare da amincewarmu cewa samun nasarar masana’antu kai tsaye nasara ce ga tattalin arziki, da bin hanyar fadadawa, rayuwa mai kyau ga ‘yan kasa.”

Bankuna
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (3): Shari’ar Manzon Allah (SAW) Ta Zo Da Wayewa A Kowane Fanni

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (3): Shari’ar Manzon Allah (SAW) Ta Zo Da Wayewa A Kowane Fanni

LABARAI MASU NASABA

Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.