• English
  • Business News
Sunday, August 10, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Lalubo Hanyoyin Cin Gajiyar Ma’adinai A Nijeriya

by Leadership Hausa
1 year ago
in Labarai
0
Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ya kamata jawabin da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi kwanakin baya a taron nazarin yaki da ta’addanci ya zama matashiya ga al’umma a kan dangantakar masu hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba da harkokin ta’addanci a nahiyar Afirka,da kuma yadda suke daukar nauyin ta’addanci a sassan Nijeriya.

A jawabin ya yi nuni da cewa,bai kamata a kawar da kai daga abubuwan da suke faruwa ba, musamman ma ganin lamarin hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba, ba wai abu ne da ya shafi muhalli da tattalin arziki kawi bane, abu ne da a halin yanzu ya shafi tsaron kasa baka daya.An dade ana sa ido masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba na ci gaba da harkokinsu tare da hadin guiwar al’ummar yankin da ake hakar ma’adanan da kuma taimakon wasu bata gari daga cikin sarakuna gargajiya da kuma jami’an tsaro, akwai kuma sa hannun wasu jami’an gwamnati wadanda suka sa kishin kansu a gaba maimakon kishin kasa.

  • Da Dumi-Dumi: Majalisar Dokokin Kano Ta Rushe Masarautun Da Ganduje Ya Kirkiro
  • Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Nuna Kin Amincewa Da Kalamai Masu Matukar Hadari Na Jagoran Taiwan

Sakamakon wannan aiki na rashin gaskiya yana da yawan gaske, domin kuwa ana amfani da dukiyar kasa ne wajen kara wutar matsalar tsraon da ta yi sanadiyyar mutuwar al’ummar Nijeriya masu yawa a sassan kasa.
Kididdgar da ke fitowa ta abin da ke faruwa yana tayar da hankula.A rahoton wani kamfanin da ya shahara a fagen samar da bayanan tsaro mai suna ‘Beacon Security and Intelligence Limited’ ya bayyana cewa,akalla mutum 2,583 ne aka kashe an kuma yi garkuwa da mutum 2,164 a zangon farko na wannan shekarar.

Wannan kididdgar tana nuna cewa, ana kashe akalla mutum 28 tare da yin garkuwa da mutum 24 a kullum a cikin wannan lokacin.Wannan ba abin da za a amince da shi ba ne ya kuma kamata a gagguta daukar matakai masu muhimmanci don kawo karshen wannan bala’in.Amma kuma abubuwan da hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba ke haifarwa ya wuce matsalar tsaro gaba daya.Bayan barnar da lamarin ke haifarwa ga muhalli, ga kuma cutar da al’ummar yankin da ake hakar ma’adinan,haka kuma lafiyar su na cikin hadari.

Idan za mu iya tunawa a Jihar Zamfara kananan yara 400 suka rasa rayukansu sakamakon gubar dalma da suka shaka a wuraren da ake haka ma’adanin gwal, lamarin ya faru ne a tsakanin shekarar 2010 zuwa 2013.Kamar dai abin da ke faruwa a yankin Neja Delta inda sakamako hakar man fetur aka illata muhalli ta yadda harkokin rayuwar al’umma a yankin ya shiga matsala.

Labarai Masu Nasaba

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

A ra’ayin wannan jaridar, ya kamata gwamnati ta dauki mataki mai muhimmanci don maganin irin wannan matsalar a sassan kasar nan musamman wuraren da ake hakar ma’adinai. Matakin farko shi ne tabbatar da ana aiki da dokokin da ake da su a kasa game da yadda ake hakar ma’adinai ba tare da cutar da al’umma ba,a kuma sanya al’ummar yankin cikin dukkan tsarin da za a yi domin samun nasarar da ake bukata.

An dade da yin watsi da wadannan dokoki,an bar masu hakar ma’adinai suna cin karensu babu babbaka,babu mai sa ido a kan irin kayan aikin da suke amfani da su wajen aikin hakar ma’adanai da kuma ma’aikatan da suke amfani wajen wannan aikin.

Bugu da kari kuma muna bayar da shawarar cewa, dukkan masu lasisin Bugu kari cikakken kwarewar da ta kamata tare da cikakken shirin kare al’umma da muhalli daga dukkan cutar da aikin hakar ma’adinan zata iya haifarwa ga muhalli.

Ya kuma kamata gwamnatin tarayya da samar da wani tsari da zai tattauna da kamfanoni masu hakar ma’adanai don samar da yarjejeniyar da za ta kare dukkan masu ruwa da tsaki a yankin da ake hakar ma’adinan, kamar Sarakuna gargajiya,da kungiyoyin matasa masu fafutuka, a kuma tabbatar da an bi dukkan dokokin kasa tare da kare hakkin bil adam ba.

Samar da hukumar kula da yankunan hakar ma’adanai kamar dai yadda ake da hukumar kula da yankin Neja Delta, hakan zai iya taimaka wajen daidaita al’amura da bunkasa tattalin arzikn yankin da ake hakar ma’adinai gaba daya.

Akwai kuma bukatar tabbatar da gaskiya da rikon amana a tsakanin kamfanonin hakara ma’adanai a kasar nan.A tabbatar da ana fitar da kididdiga na gaskiya na abin da ake hakowa da sauran kididdigar yadda ake gudanar da harkoki a bangaren.Yin haka zai taimaka wajen gudanar da harkokin gwamnati cikin gaskiya ta yadda dukkan masu ruwa da tsaki za su amfana da albarkatun da ake samu a yankin gaba daya.

Domin cimma nasarar da ake bukata,ya kamata gwamnati ta tabbatar da ana tafiya tare da al’ummar da ke yankin da ake hakar ma’adanan domin suma su san ana tafiya tare da su musamman ganin yankin da suka dogara da shi ne aka lalata domin a hako ma’adinai an kuma lalata hanyoyin samun abincin su.

A ra’ayinmu kuma ya kamata al’ummar Nijeriya su rungumi kiran da Shugaban Kasa Bola Tinubu ya yi na neman hadin kan al’umma domin samun nasarar sake fasalin bangaren ma’adinai ta yadda za a amfana da dukkan abin da zai fito daga sashen ta yadda zai taimaka wajen bunkasa tattalin arzikin kasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hakar Ma'adinaita'addanci a Nijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Fara Atisayen Soja Na Hadin Gwiwa A Kewayen Tsibirin Taiwan

Next Post

‘Yan Nijeriya A Hannun Tinubu Cikin Shekara Guda

Related

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto
Labarai

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

9 hours ago
An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

14 hours ago
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi
Labarai

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

15 hours ago
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
Labarai

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

16 hours ago
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi
Labarai

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

18 hours ago
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

21 hours ago
Next Post
Tinubu

‘Yan Nijeriya A Hannun Tinubu Cikin Shekara Guda

LABARAI MASU NASABA

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

August 9, 2025
Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

August 9, 2025
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

August 9, 2025
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

August 9, 2025
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.