• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Lalubo Hanyoyin Cin Gajiyar Ma’adinai A Nijeriya

by Leadership Hausa
12 months ago
in Labarai
0
Nijeriya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ya kamata jawabin da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi kwanakin baya a taron nazarin yaki da ta’addanci ya zama matashiya ga al’umma a kan dangantakar masu hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba da harkokin ta’addanci a nahiyar Afirka,da kuma yadda suke daukar nauyin ta’addanci a sassan Nijeriya.

A jawabin ya yi nuni da cewa,bai kamata a kawar da kai daga abubuwan da suke faruwa ba, musamman ma ganin lamarin hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba, ba wai abu ne da ya shafi muhalli da tattalin arziki kawi bane, abu ne da a halin yanzu ya shafi tsaron kasa baka daya.An dade ana sa ido masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba na ci gaba da harkokinsu tare da hadin guiwar al’ummar yankin da ake hakar ma’adanan da kuma taimakon wasu bata gari daga cikin sarakuna gargajiya da kuma jami’an tsaro, akwai kuma sa hannun wasu jami’an gwamnati wadanda suka sa kishin kansu a gaba maimakon kishin kasa.

  • Da Dumi-Dumi: Majalisar Dokokin Kano Ta Rushe Masarautun Da Ganduje Ya Kirkiro
  • Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Nuna Kin Amincewa Da Kalamai Masu Matukar Hadari Na Jagoran Taiwan

Sakamakon wannan aiki na rashin gaskiya yana da yawan gaske, domin kuwa ana amfani da dukiyar kasa ne wajen kara wutar matsalar tsraon da ta yi sanadiyyar mutuwar al’ummar Nijeriya masu yawa a sassan kasa.
Kididdgar da ke fitowa ta abin da ke faruwa yana tayar da hankula.A rahoton wani kamfanin da ya shahara a fagen samar da bayanan tsaro mai suna ‘Beacon Security and Intelligence Limited’ ya bayyana cewa,akalla mutum 2,583 ne aka kashe an kuma yi garkuwa da mutum 2,164 a zangon farko na wannan shekarar.

Wannan kididdgar tana nuna cewa, ana kashe akalla mutum 28 tare da yin garkuwa da mutum 24 a kullum a cikin wannan lokacin.Wannan ba abin da za a amince da shi ba ne ya kuma kamata a gagguta daukar matakai masu muhimmanci don kawo karshen wannan bala’in.Amma kuma abubuwan da hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba ke haifarwa ya wuce matsalar tsaro gaba daya.Bayan barnar da lamarin ke haifarwa ga muhalli, ga kuma cutar da al’ummar yankin da ake hakar ma’adinan,haka kuma lafiyar su na cikin hadari.

Idan za mu iya tunawa a Jihar Zamfara kananan yara 400 suka rasa rayukansu sakamakon gubar dalma da suka shaka a wuraren da ake haka ma’adanin gwal, lamarin ya faru ne a tsakanin shekarar 2010 zuwa 2013.Kamar dai abin da ke faruwa a yankin Neja Delta inda sakamako hakar man fetur aka illata muhalli ta yadda harkokin rayuwar al’umma a yankin ya shiga matsala.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

A ra’ayin wannan jaridar, ya kamata gwamnati ta dauki mataki mai muhimmanci don maganin irin wannan matsalar a sassan kasar nan musamman wuraren da ake hakar ma’adinai. Matakin farko shi ne tabbatar da ana aiki da dokokin da ake da su a kasa game da yadda ake hakar ma’adinai ba tare da cutar da al’umma ba,a kuma sanya al’ummar yankin cikin dukkan tsarin da za a yi domin samun nasarar da ake bukata.

An dade da yin watsi da wadannan dokoki,an bar masu hakar ma’adinai suna cin karensu babu babbaka,babu mai sa ido a kan irin kayan aikin da suke amfani da su wajen aikin hakar ma’adanai da kuma ma’aikatan da suke amfani wajen wannan aikin.

Bugu da kari kuma muna bayar da shawarar cewa, dukkan masu lasisin Bugu kari cikakken kwarewar da ta kamata tare da cikakken shirin kare al’umma da muhalli daga dukkan cutar da aikin hakar ma’adinan zata iya haifarwa ga muhalli.

Ya kuma kamata gwamnatin tarayya da samar da wani tsari da zai tattauna da kamfanoni masu hakar ma’adanai don samar da yarjejeniyar da za ta kare dukkan masu ruwa da tsaki a yankin da ake hakar ma’adinan, kamar Sarakuna gargajiya,da kungiyoyin matasa masu fafutuka, a kuma tabbatar da an bi dukkan dokokin kasa tare da kare hakkin bil adam ba.

Samar da hukumar kula da yankunan hakar ma’adanai kamar dai yadda ake da hukumar kula da yankin Neja Delta, hakan zai iya taimaka wajen daidaita al’amura da bunkasa tattalin arzikn yankin da ake hakar ma’adinai gaba daya.

Akwai kuma bukatar tabbatar da gaskiya da rikon amana a tsakanin kamfanonin hakara ma’adanai a kasar nan.A tabbatar da ana fitar da kididdiga na gaskiya na abin da ake hakowa da sauran kididdigar yadda ake gudanar da harkoki a bangaren.Yin haka zai taimaka wajen gudanar da harkokin gwamnati cikin gaskiya ta yadda dukkan masu ruwa da tsaki za su amfana da albarkatun da ake samu a yankin gaba daya.

Domin cimma nasarar da ake bukata,ya kamata gwamnati ta tabbatar da ana tafiya tare da al’ummar da ke yankin da ake hakar ma’adanan domin suma su san ana tafiya tare da su musamman ganin yankin da suka dogara da shi ne aka lalata domin a hako ma’adinai an kuma lalata hanyoyin samun abincin su.

A ra’ayinmu kuma ya kamata al’ummar Nijeriya su rungumi kiran da Shugaban Kasa Bola Tinubu ya yi na neman hadin kan al’umma domin samun nasarar sake fasalin bangaren ma’adinai ta yadda za a amfana da dukkan abin da zai fito daga sashen ta yadda zai taimaka wajen bunkasa tattalin arzikin kasa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hakar Ma'adinaita'addanci a Nijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

An Fara Atisayen Soja Na Hadin Gwiwa A Kewayen Tsibirin Taiwan

Next Post

‘Yan Nijeriya A Hannun Tinubu Cikin Shekara Guda

Related

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

31 minutes ago
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi
Labarai

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

3 hours ago
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

6 hours ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

6 hours ago
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 
Labarai

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

7 hours ago
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

8 hours ago
Next Post
Tinubu

‘Yan Nijeriya A Hannun Tinubu Cikin Shekara Guda

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Sarki Mai Daraja Ta Ɗaya A Kogi

May 15, 2025
Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

Shugaba Xi Ya Amsa Wasikar Da Jagoran Da Ya Kafa Majalisar Cinikayya Ta Denmark A Sin Ya Aike Masa

May 15, 2025
An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.