ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Lalubo Hanyoyin Cin Gajiyar Ma’adinai A Nijeriya

by Leadership Hausa
2 years ago
Nijeriya

Ya kamata jawabin da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi kwanakin baya a taron nazarin yaki da ta’addanci ya zama matashiya ga al’umma a kan dangantakar masu hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba da harkokin ta’addanci a nahiyar Afirka,da kuma yadda suke daukar nauyin ta’addanci a sassan Nijeriya.

A jawabin ya yi nuni da cewa,bai kamata a kawar da kai daga abubuwan da suke faruwa ba, musamman ma ganin lamarin hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba, ba wai abu ne da ya shafi muhalli da tattalin arziki kawi bane, abu ne da a halin yanzu ya shafi tsaron kasa baka daya.An dade ana sa ido masu hakar ma’adanai ba bisa ka’ida ba na ci gaba da harkokinsu tare da hadin guiwar al’ummar yankin da ake hakar ma’adanan da kuma taimakon wasu bata gari daga cikin sarakuna gargajiya da kuma jami’an tsaro, akwai kuma sa hannun wasu jami’an gwamnati wadanda suka sa kishin kansu a gaba maimakon kishin kasa.

  • Da Dumi-Dumi: Majalisar Dokokin Kano Ta Rushe Masarautun Da Ganduje Ya Kirkiro
  • Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Nuna Kin Amincewa Da Kalamai Masu Matukar Hadari Na Jagoran Taiwan

Sakamakon wannan aiki na rashin gaskiya yana da yawan gaske, domin kuwa ana amfani da dukiyar kasa ne wajen kara wutar matsalar tsraon da ta yi sanadiyyar mutuwar al’ummar Nijeriya masu yawa a sassan kasa.
Kididdgar da ke fitowa ta abin da ke faruwa yana tayar da hankula.A rahoton wani kamfanin da ya shahara a fagen samar da bayanan tsaro mai suna ‘Beacon Security and Intelligence Limited’ ya bayyana cewa,akalla mutum 2,583 ne aka kashe an kuma yi garkuwa da mutum 2,164 a zangon farko na wannan shekarar.

ADVERTISEMENT

Wannan kididdgar tana nuna cewa, ana kashe akalla mutum 28 tare da yin garkuwa da mutum 24 a kullum a cikin wannan lokacin.Wannan ba abin da za a amince da shi ba ne ya kuma kamata a gagguta daukar matakai masu muhimmanci don kawo karshen wannan bala’in.Amma kuma abubuwan da hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba ke haifarwa ya wuce matsalar tsaro gaba daya.Bayan barnar da lamarin ke haifarwa ga muhalli, ga kuma cutar da al’ummar yankin da ake hakar ma’adinan,haka kuma lafiyar su na cikin hadari.

Idan za mu iya tunawa a Jihar Zamfara kananan yara 400 suka rasa rayukansu sakamakon gubar dalma da suka shaka a wuraren da ake haka ma’adanin gwal, lamarin ya faru ne a tsakanin shekarar 2010 zuwa 2013.Kamar dai abin da ke faruwa a yankin Neja Delta inda sakamako hakar man fetur aka illata muhalli ta yadda harkokin rayuwar al’umma a yankin ya shiga matsala.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

A ra’ayin wannan jaridar, ya kamata gwamnati ta dauki mataki mai muhimmanci don maganin irin wannan matsalar a sassan kasar nan musamman wuraren da ake hakar ma’adinai. Matakin farko shi ne tabbatar da ana aiki da dokokin da ake da su a kasa game da yadda ake hakar ma’adinai ba tare da cutar da al’umma ba,a kuma sanya al’ummar yankin cikin dukkan tsarin da za a yi domin samun nasarar da ake bukata.

An dade da yin watsi da wadannan dokoki,an bar masu hakar ma’adinai suna cin karensu babu babbaka,babu mai sa ido a kan irin kayan aikin da suke amfani da su wajen aikin hakar ma’adanai da kuma ma’aikatan da suke amfani wajen wannan aikin.

Bugu da kari kuma muna bayar da shawarar cewa, dukkan masu lasisin Bugu kari cikakken kwarewar da ta kamata tare da cikakken shirin kare al’umma da muhalli daga dukkan cutar da aikin hakar ma’adinan zata iya haifarwa ga muhalli.

Ya kuma kamata gwamnatin tarayya da samar da wani tsari da zai tattauna da kamfanoni masu hakar ma’adanai don samar da yarjejeniyar da za ta kare dukkan masu ruwa da tsaki a yankin da ake hakar ma’adinan, kamar Sarakuna gargajiya,da kungiyoyin matasa masu fafutuka, a kuma tabbatar da an bi dukkan dokokin kasa tare da kare hakkin bil adam ba.

Samar da hukumar kula da yankunan hakar ma’adanai kamar dai yadda ake da hukumar kula da yankin Neja Delta, hakan zai iya taimaka wajen daidaita al’amura da bunkasa tattalin arzikn yankin da ake hakar ma’adinai gaba daya.

Akwai kuma bukatar tabbatar da gaskiya da rikon amana a tsakanin kamfanonin hakara ma’adanai a kasar nan.A tabbatar da ana fitar da kididdiga na gaskiya na abin da ake hakowa da sauran kididdigar yadda ake gudanar da harkoki a bangaren.Yin haka zai taimaka wajen gudanar da harkokin gwamnati cikin gaskiya ta yadda dukkan masu ruwa da tsaki za su amfana da albarkatun da ake samu a yankin gaba daya.

Domin cimma nasarar da ake bukata,ya kamata gwamnati ta tabbatar da ana tafiya tare da al’ummar da ke yankin da ake hakar ma’adanan domin suma su san ana tafiya tare da su musamman ganin yankin da suka dogara da shi ne aka lalata domin a hako ma’adinai an kuma lalata hanyoyin samun abincin su.

A ra’ayinmu kuma ya kamata al’ummar Nijeriya su rungumi kiran da Shugaban Kasa Bola Tinubu ya yi na neman hadin kan al’umma domin samun nasarar sake fasalin bangaren ma’adinai ta yadda za a amfana da dukkan abin da zai fito daga sashen ta yadda zai taimaka wajen bunkasa tattalin arzikin kasa.

Nijeriya
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi
Labarai

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”
Ra'ayi Riga

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma
Labarai

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Next Post
Tinubu

‘Yan Nijeriya A Hannun Tinubu Cikin Shekara Guda

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.