• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukukuwan Kirismeti: Gwamnatin Tarayya Ta Jajanta Wa Iyalan Waɗanda Suka Rasu Sakamakon Turmutsitsi A Wasu Jihohi

by Sulaiman
6 months ago
in Labarai
0
Za A ƙarfafa Gyare-gyaren Tsarin Tattalin Arziki Da Gwamnatin Tinubu Ke Yi A 2025 – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya jajanta wa iyalai da ‘yan’uwan waɗanda suka rasa rayukan su sakamakon turmutsitsi yayin rabon abinci da aka yi a Ibadan, Okija da Abuja.

 

A cikin wata sanarwa da Rabi’u Ibrahim, Mataimaki na Musamman kan Harkokin Watsa Labarai ga Ministan, ya fitar a ranar Lahadi, ya ruwaito Idris yana cewa: “Tunanin mu da addu’o’in mu suna ga waɗanda suka rasa rayukan su da iyalan su da duk wanda wannan mummunan al’amari ya shafa.”

  • Trump Ya Gana Da Shugaban TikTok
  • Yadda Mai Haihuwar Farko Za Ta Kula Da Kanta

Ministan ya ce waɗannan abubuwan baƙin ciki sun yi matuƙar girgiza gwamnati kuma ya jaddada muhimmancin tabbatar da gudanar da taron jama’a yadda ya kamata yayin gudanar da irin waɗannan ayyukan alheri, musamman a lokacin bukukuwan Kirsimeti.

 

Labarai Masu Nasaba

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

Duk da yake ya yaba da kyawawan niyyar waɗanda suka shirya irin waɗannan ayyuka domin taimaka wa mabuƙata, ministan ya gargaɗi dukkan mutane da ƙungiyoyi da suke shirin gudanar da irin waɗannan ayyukan da su bi umarnin da Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, Mista Kayode Egbetokun, ya bayar kan a riƙa tuntuɓar ofisoshin ‘yan sanda domin gudanar da tsari mai kyau na kula da jama’a da tsaro.

 

Ya jaddada cewa haɗin kai tsakanin jami’an ‘yan sanda da Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) yana da matuƙar muhimmanci wajen kare rayuka da tabbatar da cewa irin wannan ƙoƙarin na agajin mabuƙata bai haifar da wata damuwa ba.

 

Haka kuma Idris ya yi kira ga ‘yan siyasa da sauran masu ruwa da tsaki da su guji siyasantar da irin waɗannan mummunan al’amuran, yana mai bayyana cewa waɗannan munanan al’amura ba su da alaƙa da tada komaɗar tattalin arziki na gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ke yi.

 

“Ya kamata a lura da cewa a baya an taɓa samun aukuwar irin waɗannan abubuwan takaici, kafin zuwan wannan gwamnati mai ci, don haka duk wani yunƙuri na danganta waɗannan bala’o’i da gyare-gyaren Shugaban Ƙasa ba shi da tushe kuma ba gaskiya ba ne,” inji shi.

 

Idris ya ce gyare-gyaren da ake yi, yayin da suke sake fasalin tattalin arzikin Nijeriya domin samun cigaba mai ɗorewa, an tsara su ne domin inganta rayuwar dukkan ‘yan Nijeriya, musamman mabuƙata, ba tare da haifar da wata damuwa ba.

 

Ministan ya yi kira ga ‘yan ƙasa da su haɗa kai wajen tabbatar da cewa lokacin bukukuwan Kirsimeti ya kasance lokacin zaman lafiya, kyakkyawan hali, da farin ciki, ba tare da abubuwan baƙin ciki da za a iya kauce wa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Ɗage Haramcin Haƙar Ma’adanai A Zamfara

Next Post

Kamfanin Jiragen Sama Na Azman Ya Musanta Zargin Sayar Da Jiragensa Ga Iran 

Related

Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

8 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

10 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

11 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

12 hours ago
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu
Labarai

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

14 hours ago
Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara
Labarai

Gwamnatin Tarayya Na Yunkurin Rage Dala Biliyan 1.5 Da Ake Kashewa Wajen Shigo Da Madara

15 hours ago
Next Post
Kamfanin Jiragen Sama Na Azman Ya Musanta Zargin Sayar Da Jiragensa Ga Iran 

Kamfanin Jiragen Sama Na Azman Ya Musanta Zargin Sayar Da Jiragensa Ga Iran 

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.