• English
  • Business News
Saturday, September 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukukuwan Kirismeti: Gwamnatin Tarayya Ta Jajanta Wa Iyalan Waɗanda Suka Rasu Sakamakon Turmutsitsi A Wasu Jihohi

by Sulaiman
9 months ago
in Labarai
0
Za A ƙarfafa Gyare-gyaren Tsarin Tattalin Arziki Da Gwamnatin Tinubu Ke Yi A 2025 – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya jajanta wa iyalai da ‘yan’uwan waɗanda suka rasa rayukan su sakamakon turmutsitsi yayin rabon abinci da aka yi a Ibadan, Okija da Abuja.

 

A cikin wata sanarwa da Rabi’u Ibrahim, Mataimaki na Musamman kan Harkokin Watsa Labarai ga Ministan, ya fitar a ranar Lahadi, ya ruwaito Idris yana cewa: “Tunanin mu da addu’o’in mu suna ga waɗanda suka rasa rayukan su da iyalan su da duk wanda wannan mummunan al’amari ya shafa.”

  • Trump Ya Gana Da Shugaban TikTok
  • Yadda Mai Haihuwar Farko Za Ta Kula Da Kanta

Ministan ya ce waɗannan abubuwan baƙin ciki sun yi matuƙar girgiza gwamnati kuma ya jaddada muhimmancin tabbatar da gudanar da taron jama’a yadda ya kamata yayin gudanar da irin waɗannan ayyukan alheri, musamman a lokacin bukukuwan Kirsimeti.

 

Labarai Masu Nasaba

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

Duk da yake ya yaba da kyawawan niyyar waɗanda suka shirya irin waɗannan ayyuka domin taimaka wa mabuƙata, ministan ya gargaɗi dukkan mutane da ƙungiyoyi da suke shirin gudanar da irin waɗannan ayyukan da su bi umarnin da Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, Mista Kayode Egbetokun, ya bayar kan a riƙa tuntuɓar ofisoshin ‘yan sanda domin gudanar da tsari mai kyau na kula da jama’a da tsaro.

 

Ya jaddada cewa haɗin kai tsakanin jami’an ‘yan sanda da Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) yana da matuƙar muhimmanci wajen kare rayuka da tabbatar da cewa irin wannan ƙoƙarin na agajin mabuƙata bai haifar da wata damuwa ba.

 

Haka kuma Idris ya yi kira ga ‘yan siyasa da sauran masu ruwa da tsaki da su guji siyasantar da irin waɗannan mummunan al’amuran, yana mai bayyana cewa waɗannan munanan al’amura ba su da alaƙa da tada komaɗar tattalin arziki na gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ke yi.

 

“Ya kamata a lura da cewa a baya an taɓa samun aukuwar irin waɗannan abubuwan takaici, kafin zuwan wannan gwamnati mai ci, don haka duk wani yunƙuri na danganta waɗannan bala’o’i da gyare-gyaren Shugaban Ƙasa ba shi da tushe kuma ba gaskiya ba ne,” inji shi.

 

Idris ya ce gyare-gyaren da ake yi, yayin da suke sake fasalin tattalin arzikin Nijeriya domin samun cigaba mai ɗorewa, an tsara su ne domin inganta rayuwar dukkan ‘yan Nijeriya, musamman mabuƙata, ba tare da haifar da wata damuwa ba.

 

Ministan ya yi kira ga ‘yan ƙasa da su haɗa kai wajen tabbatar da cewa lokacin bukukuwan Kirsimeti ya kasance lokacin zaman lafiya, kyakkyawan hali, da farin ciki, ba tare da abubuwan baƙin ciki da za a iya kauce wa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Ɗage Haramcin Haƙar Ma’adanai A Zamfara

Next Post

Kamfanin Jiragen Sama Na Azman Ya Musanta Zargin Sayar Da Jiragensa Ga Iran 

Related

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya
Labarai

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

2 hours ago
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 
Labarai

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

11 hours ago
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara
Labarai

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

12 hours ago
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu
Labarai

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

13 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 2 Da Wasu 156 Kan Aikata Laifuka A Jigawa

13 hours ago
Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai
Labarai

Ajandar Ci Gaban Tinubu Ta Ƙunshi Ƙasa Baki Ɗaya – Ministan Yaɗa Labarai

14 hours ago
Next Post
Kamfanin Jiragen Sama Na Azman Ya Musanta Zargin Sayar Da Jiragensa Ga Iran 

Kamfanin Jiragen Sama Na Azman Ya Musanta Zargin Sayar Da Jiragensa Ga Iran 

LABARAI MASU NASABA

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

Maulidi: Gwamnan Zamfara Ya Taya Al’ummar Musulmi Murna, Ya Buƙaci A Dage Da Addu’o’in Samun Zaman Lafiya

September 6, 2025
Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

Sashen Cinikayyar Bayar Da Hidima Na Sin Ya Bunkasa Cikin Watanni Bakwai Na Farkon Shekarar Bana

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

Kasar Sin Ta Yi Nasarar Harba Wani Sabon Tauraron Dan Adam

September 5, 2025
Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

Jami’an Kasa Da Kasa Sun Yi Matukar Jinjinawa Jawabin Xi Jinping

September 5, 2025
Za Mu Riƙe Wa Minista Tijjani Muƙaminsa Bayan Hamɓarar Da Tinubu A 2027 – El-Rufai 

Ana Ci Gaba Da Caccakar El-rufai Kan Kalamansa Game Da Tsaron Kasa

September 5, 2025
Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

Kasar Sin Ta Kasance Muhimmin Karfi Dake Tabbatar Da Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya

September 5, 2025
Yadda Al’ummar Da Ke Zaune Da ‘Yan Bindiga Ke Rayuwa A Zamfara

Duk Da Sulhu Da ‘Yan Bindiga Ana Ci Gaba Da Kai Hare-hare Wasu Yankunan Zamfara

September 5, 2025
Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Antonio Guterres Ya Yi Maraba Da Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 5, 2025
Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

Ban Yi Kuskure Wajen Zaben Kashim A Matsayin Mataimaki Ba – Tinubu

September 5, 2025
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Bikin Baje Kolin Masana’antun Kirkirarriyar Basira

September 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.