ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukukuwan Kirismeti: Gwamnatin Tarayya Ta Jajanta Wa Iyalan Waɗanda Suka Rasu Sakamakon Turmutsitsi A Wasu Jihohi

by Sulaiman
1 year ago
Turmutsitsi

Ministan Yaɗa Labarai da Wayar da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya jajanta wa iyalai da ‘yan’uwan waɗanda suka rasa rayukan su sakamakon turmutsitsi yayin rabon abinci da aka yi a Ibadan, Okija da Abuja.

 

A cikin wata sanarwa da Rabi’u Ibrahim, Mataimaki na Musamman kan Harkokin Watsa Labarai ga Ministan, ya fitar a ranar Lahadi, ya ruwaito Idris yana cewa: “Tunanin mu da addu’o’in mu suna ga waɗanda suka rasa rayukan su da iyalan su da duk wanda wannan mummunan al’amari ya shafa.”

ADVERTISEMENT
  • Trump Ya Gana Da Shugaban TikTok
  • Yadda Mai Haihuwar Farko Za Ta Kula Da Kanta

Ministan ya ce waɗannan abubuwan baƙin ciki sun yi matuƙar girgiza gwamnati kuma ya jaddada muhimmancin tabbatar da gudanar da taron jama’a yadda ya kamata yayin gudanar da irin waɗannan ayyukan alheri, musamman a lokacin bukukuwan Kirsimeti.

 

LABARAI MASU NASABA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Duk da yake ya yaba da kyawawan niyyar waɗanda suka shirya irin waɗannan ayyuka domin taimaka wa mabuƙata, ministan ya gargaɗi dukkan mutane da ƙungiyoyi da suke shirin gudanar da irin waɗannan ayyukan da su bi umarnin da Sufeto Janar na ‘Yan Sanda, Mista Kayode Egbetokun, ya bayar kan a riƙa tuntuɓar ofisoshin ‘yan sanda domin gudanar da tsari mai kyau na kula da jama’a da tsaro.

 

Ya jaddada cewa haɗin kai tsakanin jami’an ‘yan sanda da Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) yana da matuƙar muhimmanci wajen kare rayuka da tabbatar da cewa irin wannan ƙoƙarin na agajin mabuƙata bai haifar da wata damuwa ba.

 

Haka kuma Idris ya yi kira ga ‘yan siyasa da sauran masu ruwa da tsaki da su guji siyasantar da irin waɗannan mummunan al’amuran, yana mai bayyana cewa waɗannan munanan al’amura ba su da alaƙa da tada komaɗar tattalin arziki na gwamnatin Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ke yi.

 

“Ya kamata a lura da cewa a baya an taɓa samun aukuwar irin waɗannan abubuwan takaici, kafin zuwan wannan gwamnati mai ci, don haka duk wani yunƙuri na danganta waɗannan bala’o’i da gyare-gyaren Shugaban Ƙasa ba shi da tushe kuma ba gaskiya ba ne,” inji shi.

 

Idris ya ce gyare-gyaren da ake yi, yayin da suke sake fasalin tattalin arzikin Nijeriya domin samun cigaba mai ɗorewa, an tsara su ne domin inganta rayuwar dukkan ‘yan Nijeriya, musamman mabuƙata, ba tare da haifar da wata damuwa ba.

 

Ministan ya yi kira ga ‘yan ƙasa da su haɗa kai wajen tabbatar da cewa lokacin bukukuwan Kirsimeti ya kasance lokacin zaman lafiya, kyakkyawan hali, da farin ciki, ba tare da abubuwan baƙin ciki da za a iya kauce wa ba.

Turmutsitsi
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya
  • Sulaiman
    Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina
  • Sulaiman
    Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026
  • Sulaiman
    Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

MASU ALAKA

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato
Tsaro

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi
Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Next Post
Kamfanin Jiragen Sama Na Azman Ya Musanta Zargin Sayar Da Jiragensa Ga Iran 

Kamfanin Jiragen Sama Na Azman Ya Musanta Zargin Sayar Da Jiragensa Ga Iran 

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.