• English
  • Business News
Sunday, November 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bunkasa Kimiyya Da Fasaha: Nijeriya Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasar Cuba

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Cuba

Gwamnatin Tarayya ta sanya hannun yarjejeniyar fahimtar juna da Jamhuriyar Cuba, don bunkasa harkokin kere-kere, kimiyya da kuma fasaha a tsakanin kasashen biyu tare da kyautata harkokin ci gaba mai maidorewa.

Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima, shi ne ya jagoranci tawagar Nijeriya wajen sanya hannun yarjejeniyar a yayin taron ‘G77+China Summit’ da ya gudana a Habana, kamar yadda wata sanarwa wadda Daraktan Yada Labarai na ofishin Mataimakin Shugaban Kasar, Olusola Abiola ya fitar a karshen makon da ya gabata.

  • Tashar Binciken Samaniya Ta Sin Za Ta Ba Da Damar Cimma Manyan Nasarori Na Binciken Kimiyya

Ministan Kere-kere, Kimiyya da Fasaha, Uche Nnaji wanda ya sanya hannu a madadin Gwamnatin Nijeriya, ya jinjina wa salon mulkin Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu, sakamakon kai wa ga cimma wannan yarjejeniya.

Hadakar yarjejeniyar, za ta mai da hankali a bangarorin bincike da ci gaban harkokin rayuwar jama’a da kuma kyautata alaka a tsakanin kasashen biyu.

Bangarorin hadin guiwar tsakanin kasashen biyu, zai mai da hankali ne a kan fasahar kere-kere, binciken kimiyya, sabbin kirkire-kirkiren zamani, ci gaban fasaha, bunkasa harkokin rayuwar al’umma, musayar ra’ayoyin kwarewa kan kimiyya da kuma fasaha da kere-kere, domin musayar ra’ayoyi ta yadda za a samu bunkasar ci gaba mai muhimmancin gaske.

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

Nnaji ya kara da cewa, Kasar Nijeriya za ta bayar da cikakkiyar gudunmawar da ake bukata daga gare ta, domin cimma nasarorin da yarjejeniyar ta sanya a gaba, ya sake jaddada cewa, gwamnati a shirye take ta aiwatar da tsare-tsaren yarjejeniyar da aka cimma.

Daga cikin wadanda suka shaidi wannan kyakkyawar kafa ta tarihin ci gaban kasashen biyu, sun hada da Babban Sakataren Ma’aikatar kula da harkokin cikin gida, Ambasada Adamu Lamuwa, Ambasadan Nijeriya a Kasar Cuba, Ambasada Ben Okoyen tare da sauran manyan jami’an gwamnati.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

April 19, 2025
Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

March 8, 2025
Next Post
Atiku

Yadda Gwamnatin Tinubu Ta Shirya Tsara ‘Yan Nijeriya Da Farfaganda – Atiku

LABARAI MASU NASABA

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

NBA Ta Yi Allah Wadai Da Yadda Hukuncin Alƙalai Ke Karo Da Juna

November 9, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Jihar Kebbi Bagudo Ya Shaƙi Iskar ‘Yanci Daga ‘Yan Bindiga

November 9, 2025
Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

Soludo Ya Sake Lashe Zaɓen Gwamnan Anambra

November 9, 2025
Triumph

Zargin Ɓatanci Ga Annabi: Alaƙar Triumph Da Gwamnatin Kano Da Majalisar Shura

November 9, 2025
Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

Kasar Sin Ta Fitar Da Takardar Bayani Kan Samun Ci Gaba Mai Karancin Fitar Da Hayaki

November 8, 2025
Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

Kasar Sin Ta Sake Jaddada Cikakken Goyon Bayanta Ga Muhimmiyar Rawar Da MDD Ke Takawa A Harkokin Kasa Da Kasa 

November 8, 2025
Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

Turkiyya Na Karbar Bakuncin Wasu Kasashen Musulmai Game Da Makomar Gaza

November 8, 2025
Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

Babban Yankin Sin Da Taiwan Sun Yi Tarukan Bita Don Tunawa Da Taron Xi Da Ma Mai Tarihi

November 8, 2025
Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

Kasashen Afirka Bakwai Da Sojojin Amurka Suka Shiga

November 8, 2025
Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

Firaministan Kasar Georgia: CIIE Muhimmin Dandali Ne

November 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.