ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Monday, December 22, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bunkasa Kimiyya Da Fasaha: Nijeriya Ta Kulla Yarjejeniya Da Kasar Cuba

by Khalid Idris Doya
2 years ago
Cuba

Gwamnatin Tarayya ta sanya hannun yarjejeniyar fahimtar juna da Jamhuriyar Cuba, don bunkasa harkokin kere-kere, kimiyya da kuma fasaha a tsakanin kasashen biyu tare da kyautata harkokin ci gaba mai maidorewa.

Mataimakin Shugaban Kasa Kashim Shettima, shi ne ya jagoranci tawagar Nijeriya wajen sanya hannun yarjejeniyar a yayin taron ‘G77+China Summit’ da ya gudana a Habana, kamar yadda wata sanarwa wadda Daraktan Yada Labarai na ofishin Mataimakin Shugaban Kasar, Olusola Abiola ya fitar a karshen makon da ya gabata.

  • Tashar Binciken Samaniya Ta Sin Za Ta Ba Da Damar Cimma Manyan Nasarori Na Binciken Kimiyya

Ministan Kere-kere, Kimiyya da Fasaha, Uche Nnaji wanda ya sanya hannu a madadin Gwamnatin Nijeriya, ya jinjina wa salon mulkin Shugaban Kasa Bola Ahmad Tinubu, sakamakon kai wa ga cimma wannan yarjejeniya.

ADVERTISEMENT

Hadakar yarjejeniyar, za ta mai da hankali a bangarorin bincike da ci gaban harkokin rayuwar jama’a da kuma kyautata alaka a tsakanin kasashen biyu.

Bangarorin hadin guiwar tsakanin kasashen biyu, zai mai da hankali ne a kan fasahar kere-kere, binciken kimiyya, sabbin kirkire-kirkiren zamani, ci gaban fasaha, bunkasa harkokin rayuwar al’umma, musayar ra’ayoyin kwarewa kan kimiyya da kuma fasaha da kere-kere, domin musayar ra’ayoyi ta yadda za a samu bunkasar ci gaba mai muhimmancin gaske.

LABARAI MASU NASABA

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

Nnaji ya kara da cewa, Kasar Nijeriya za ta bayar da cikakkiyar gudunmawar da ake bukata daga gare ta, domin cimma nasarorin da yarjejeniyar ta sanya a gaba, ya sake jaddada cewa, gwamnati a shirye take ta aiwatar da tsare-tsaren yarjejeniyar da aka cimma.

Daga cikin wadanda suka shaidi wannan kyakkyawar kafa ta tarihin ci gaban kasashen biyu, sun hada da Babban Sakataren Ma’aikatar kula da harkokin cikin gida, Ambasada Adamu Lamuwa, Ambasadan Nijeriya a Kasar Cuba, Ambasada Ben Okoyen tare da sauran manyan jami’an gwamnati.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai
Da ɗumi-ɗuminsa

Jami’ar Bayero Ta Yi Rashin Fitaccen Masanin Ilimin Harshe, Farfesa Hafizu Miko Yakasai

September 5, 2025
Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Wayar Da Kai Kan Barazanar Intanet A Rayuwar Al’umma (CYBER AWARENESS)

April 19, 2025
Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet
Kimiyya Da Fasahar Sadarwa

Kariya Daga Soyayyar ‘Online’ Da Shagalta A Intanet

March 8, 2025
Next Post
Atiku

Yadda Gwamnatin Tinubu Ta Shirya Tsara ‘Yan Nijeriya Da Farfaganda – Atiku

LABARAI MASU NASABA

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

An Sako Ragowar Ɗalibai Da Malamai Da Aka Sace A Makarantar Katolika Ta Neja

December 21, 2025
Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

Raphinha Da Yamal Sun Ci Ƙwallaye Yayin Da Barcelona Ta Doke Villarreal

December 21, 2025
Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

Davido Zai Raƙashe A Bikin Buɗe Gasar AFCON 2025 A Morocco

December 21, 2025
Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

Yankin Rijiyoyin Mai Na Teku Mafi Girma Na Kasar Sin Ya Ba Da Rahoton Yawan Mai Da Iskar Gas Da Ya Fitar A Shekara

December 21, 2025
An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

An Bukaci Bunkasa Fannin Kiwo A Hadin Gwiwar Sin Da Afirka

December 21, 2025
Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.