• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bunkasar Da Kawancen Kasuwancin Sin Da Afirka Ke Yi Ta Nuna Gaba Za Ta Fi Kyau

by Abdulrazaq Yahuza
1 year ago
Afirka

Sannu a hankali, kasar Sin da Nahiyar Afirka na kara gina ‘yan uwantaka da yaukaka zumunci mai dadi a tsakaninsu bisa kawancen kasuwanci da bunkasa hada-hadar tattalin arziki domin cin gajiyar juna.
Aniyar kasar Sin ta ganin kasashen Afirka sun tsaya da kafafunsu da kuma amannar da suka yi cewa tabbas kawancensu da Sin ba karamin alheri ba ne, sun haifar da da mai ido bisa yadda Sin ta zama babbar kawar Afirka ta kasuwanci da babu kamarta a cikin shekaru 15 a jere, kana ta hudu wajen zuba jari a nahiyar.

Harkokin kasuwanci da zuba jari ba su samun tagomashi matukar babu ababen more rayuwa. Shi ya sa shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya” wanda Sin ta kulla kawance a karkashinta da kasashen Afirka 52 da ma kungiyar tarayyar Afirka (a karshen 2022), ta kasance alfijir ga samar da dimbin ababen more rayuwa domin hanzarta kawo ci gaban da ya kamata a Afirka.

Yanzu haka, kamfanonin Sin fiye da 3,000 da ke aiki a nahiyar, suna gudanar da ayyukan kawo ci gaba daban-daban har ma an sami nasarar gina ko gyara layin dogo fiye da kilomita dubu 10 da titinan mota su ma kimanin dubu 100, baya ga tasoshin jiragen ruwa kusan 100.

Sakamakon burin da Sin take da shi na cin moriyar juna a tsakaninta da Afirka, alkaluman baya-bayan nan sun nuna cewa a shekarar 2023, kasuwancin da ke tsakanin Sin da Afirka a mizanin shekara-shekara, ya habaka zuwa dala biliyan 282.1. Inda bangaren motoci masu aiki da sabbin makamashi ya karu da kashi 291 bisa dari sai baturan ‘lithium’ da Sin ke fitarwa zuwa nahiyar da ya karu zuwa kashi 109. Kana a hannu guda kuma, kayayyakin da Sin ke sayowa daga Afirka na amfanin gona masu kwaya suka karu da kashi 130 yayin da na kayan lambu suka habaka da kashi 32.
Abin bai tsaya nan ba, domin ganin Afirka ta kara samun damar kai kayayyakinta zuwa kasuwannin kasar Sin, kasar ta yi rangwamen biyan haraji da kashi 98 cikin dari a kan kayayyakin da ake biya musu harajin kwastam daga kasashe 20 da suka fi fuskantar koma-baya a nahiyar.
Bugu da kari, a farkon watanni shida na wannan shekarar kawai, kayayyakin da Sin ke shigowa da su kasarta daga Afirka sun kai na kimanin dala biliyan 60.1 wanda yake nuna an samu kari da kashi 14 a mizanin shekara-shekara. Haka nan, bayanai sun nuna cewa amfanin gonar da Sin ke shigo da su kasarta daga Afirka yana kara habaka inda a bana aka cika shekara bakwai a jere abin yana samun tagomashi.

Har ila yau, jarin da Sin ke zubawa a Afirka zuwa karshen 2023 ya zarce dala biliyan 40. A sakamakon haka ne ma, mu a nan Nijeriya muka samu tashar teku mai zurfi a Lekki da ke Jihar Legas wadda tuni manyan jiragen ruwa suka fara hada-hada a ciki. A baya, babban jirgin da zai zo tsohuwar tashar jiragen ruwa na Legas shi ne mai daukar kwantena 6,000 amma bisa samar da sabuwar tashar Lekki da taimakon kasar Sin, tuni har wani jirgin ruwa na kasar Faransa mai daukar kwantena 15,000 ya zo tashar don sauke kaya, inda hakan ke nuna cewa Nijeriya ta samu gagarumin ci gaban hada-hadar jiragen ruwa.

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

A birnin Accra na kasar Ghana kuma, bisa taimakon kasar Sin, an zamanantar da tashar jiragen ruwan kamun kifi na zamani a Yankin Jamestown, da gyara tsohuwar tashar jiragen ruwa ta Bata a kasar Equatorial Guinea, sannan a 2023 kuma, an aza harsashin gina tashar jiragen ruwa na kamun kifi ta Kilwa a kasar Tanzania.

Akwai misalai da daman gaske da ke alamta yadda gaba za ta yi kyau a tsakanin Sin da Afirka bisa yadda harkokin cinikayya da tattalin arziki ke kara samun tagomashi.

  • Nesa Ta Zo Kusa a Afrika Karkashin Taimakon Sin

 

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?
Ra'ayi Riga

Me Ya Sa Kasar Sin Ke Son Ganin Ci Gaban Kasashen Afirka?

October 27, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata
Ra'ayi Riga

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?
Ra'ayi Riga

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

October 23, 2025
Next Post
Bayan Fafatawa, Ƴan Ƙauye Sun Hallaka Ƴan Bindiga 37 A Zamfara

Bayan Fafatawa, Ƴan Ƙauye Sun Hallaka Ƴan Bindiga 37 A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Afirka

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025
Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.