• English
  • Business News
Thursday, September 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bunkasar Da Kawancen Kasuwancin Sin Da Afirka Ke Yi Ta Nuna Gaba Za Ta Fi Kyau

by Abdulrazaq Yahuza
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Bunkasar Da Kawancen Kasuwancin Sin Da Afirka Ke Yi Ta Nuna Gaba Za Ta Fi Kyau
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sannu a hankali, kasar Sin da Nahiyar Afirka na kara gina ‘yan uwantaka da yaukaka zumunci mai dadi a tsakaninsu bisa kawancen kasuwanci da bunkasa hada-hadar tattalin arziki domin cin gajiyar juna.
Aniyar kasar Sin ta ganin kasashen Afirka sun tsaya da kafafunsu da kuma amannar da suka yi cewa tabbas kawancensu da Sin ba karamin alheri ba ne, sun haifar da da mai ido bisa yadda Sin ta zama babbar kawar Afirka ta kasuwanci da babu kamarta a cikin shekaru 15 a jere, kana ta hudu wajen zuba jari a nahiyar.

Harkokin kasuwanci da zuba jari ba su samun tagomashi matukar babu ababen more rayuwa. Shi ya sa shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya” wanda Sin ta kulla kawance a karkashinta da kasashen Afirka 52 da ma kungiyar tarayyar Afirka (a karshen 2022), ta kasance alfijir ga samar da dimbin ababen more rayuwa domin hanzarta kawo ci gaban da ya kamata a Afirka.

Yanzu haka, kamfanonin Sin fiye da 3,000 da ke aiki a nahiyar, suna gudanar da ayyukan kawo ci gaba daban-daban har ma an sami nasarar gina ko gyara layin dogo fiye da kilomita dubu 10 da titinan mota su ma kimanin dubu 100, baya ga tasoshin jiragen ruwa kusan 100.

Sakamakon burin da Sin take da shi na cin moriyar juna a tsakaninta da Afirka, alkaluman baya-bayan nan sun nuna cewa a shekarar 2023, kasuwancin da ke tsakanin Sin da Afirka a mizanin shekara-shekara, ya habaka zuwa dala biliyan 282.1. Inda bangaren motoci masu aiki da sabbin makamashi ya karu da kashi 291 bisa dari sai baturan ‘lithium’ da Sin ke fitarwa zuwa nahiyar da ya karu zuwa kashi 109. Kana a hannu guda kuma, kayayyakin da Sin ke sayowa daga Afirka na amfanin gona masu kwaya suka karu da kashi 130 yayin da na kayan lambu suka habaka da kashi 32.
Abin bai tsaya nan ba, domin ganin Afirka ta kara samun damar kai kayayyakinta zuwa kasuwannin kasar Sin, kasar ta yi rangwamen biyan haraji da kashi 98 cikin dari a kan kayayyakin da ake biya musu harajin kwastam daga kasashe 20 da suka fi fuskantar koma-baya a nahiyar.
Bugu da kari, a farkon watanni shida na wannan shekarar kawai, kayayyakin da Sin ke shigowa da su kasarta daga Afirka sun kai na kimanin dala biliyan 60.1 wanda yake nuna an samu kari da kashi 14 a mizanin shekara-shekara. Haka nan, bayanai sun nuna cewa amfanin gonar da Sin ke shigo da su kasarta daga Afirka yana kara habaka inda a bana aka cika shekara bakwai a jere abin yana samun tagomashi.

Har ila yau, jarin da Sin ke zubawa a Afirka zuwa karshen 2023 ya zarce dala biliyan 40. A sakamakon haka ne ma, mu a nan Nijeriya muka samu tashar teku mai zurfi a Lekki da ke Jihar Legas wadda tuni manyan jiragen ruwa suka fara hada-hada a ciki. A baya, babban jirgin da zai zo tsohuwar tashar jiragen ruwa na Legas shi ne mai daukar kwantena 6,000 amma bisa samar da sabuwar tashar Lekki da taimakon kasar Sin, tuni har wani jirgin ruwa na kasar Faransa mai daukar kwantena 15,000 ya zo tashar don sauke kaya, inda hakan ke nuna cewa Nijeriya ta samu gagarumin ci gaban hada-hadar jiragen ruwa.

Labarai Masu Nasaba

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

A birnin Accra na kasar Ghana kuma, bisa taimakon kasar Sin, an zamanantar da tashar jiragen ruwan kamun kifi na zamani a Yankin Jamestown, da gyara tsohuwar tashar jiragen ruwa ta Bata a kasar Equatorial Guinea, sannan a 2023 kuma, an aza harsashin gina tashar jiragen ruwa na kamun kifi ta Kilwa a kasar Tanzania.

Akwai misalai da daman gaske da ke alamta yadda gaba za ta yi kyau a tsakanin Sin da Afirka bisa yadda harkokin cinikayya da tattalin arziki ke kara samun tagomashi.

  • Nesa Ta Zo Kusa a Afrika Karkashin Taimakon Sin

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfirkaKasuwanciKawanceSinTattalin Arziki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Majalisar Wakilai Ta Jinjina Wa Kamfanin Ɗangote Wajen Bunƙasa Tattalin Arzikin Ƙasa

Next Post

Bayan Fafatawa, Ƴan Ƙauye Sun Hallaka Ƴan Bindiga 37 A Zamfara

Related

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

17 minutes ago
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
Ra'ayi Riga

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

1 day ago
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

2 days ago
Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama
Ra'ayi Riga

Shawarar GGI: Faduwa Ta Zo Daidai Da Zama

2 days ago
Yadda Kasar Sin Ta Nuna Wa Afirka Asalin Ma’Anar Hakkin Dan Adam Sabanin Irin Na Kasashen Yamma
Ra'ayi Riga

Yadda Kasar Sin Ta Nuna Wa Afirka Asalin Ma’Anar Hakkin Dan Adam Sabanin Irin Na Kasashen Yamma

6 days ago
Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki
Ra'ayi Riga

Hadin Gwiwar Sin Da Afirka Ya Kawo Wa Afirka Fatan Warware Matsalar Karancin Wutar Lantarki

1 week ago
Next Post
Bayan Fafatawa, Ƴan Ƙauye Sun Hallaka Ƴan Bindiga 37 A Zamfara

Bayan Fafatawa, Ƴan Ƙauye Sun Hallaka Ƴan Bindiga 37 A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

September 4, 2025
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai

Tinubu Ya Fara Hutun Aiki Na Kwanakin 10 A Faransa Da Birtaniya

September 4, 2025
Ibtila’in Ambaliyar Ruwa: Halin Da Birnin Maiduguri Ya Tsinci Kansa A Ciki

Gargaɗi: Ƙauyuka 43 A Jihohi 14 Na Fuskantar Barazanar Ambaliyar Ruwa 

September 4, 2025
Hakimin Da Aka Sace A Jihar Kogi Ya Shaki Iskar ‘Yanci

Hakimin Da Aka Sace A Jihar Kogi Ya Shaki Iskar ‘Yanci

September 4, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Kama Wasu Mutane 3 Da Ake Zargi Da Damfara A Kano

September 4, 2025
Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Ƴan Ta’adda 15 A Borno

Harin Sojojin Sama Ya Hallaka Ƴan Ta’adda 15 A Borno

September 4, 2025
An Cafke Matar Da Ta Binne Jariri Da Rai A Kebbi

An Cafke Matar Da Ta Binne Jariri Da Rai A Kebbi

September 4, 2025
An Fara Bincike Kan Ɓarkewar Kwalara A Sokoto – Kwamishina

An Fara Bincike Kan Ɓarkewar Kwalara A Sokoto – Kwamishina

September 4, 2025
Gwamnatin Kebbi Ta Ba da Ƙwangilar Gina Hanyoyi Kan Naira Biliyan 2.1

Gwamnatin Kebbi Ta Ba da Ƙwangilar Gina Hanyoyi Kan Naira Biliyan 2.1

September 4, 2025
Tinubu Zai Ƙaddamar Da Masana’antar Battirin Lithium A Nasarawa

Tinubu Zai Ƙaddamar Da Masana’antar Battirin Lithium A Nasarawa

September 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.