ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bunkasar Da Kawancen Kasuwancin Sin Da Afirka Ke Yi Ta Nuna Gaba Za Ta Fi Kyau

by Abdulrazaq Yahuza
2 years ago
Afirka

Sannu a hankali, kasar Sin da Nahiyar Afirka na kara gina ‘yan uwantaka da yaukaka zumunci mai dadi a tsakaninsu bisa kawancen kasuwanci da bunkasa hada-hadar tattalin arziki domin cin gajiyar juna.
Aniyar kasar Sin ta ganin kasashen Afirka sun tsaya da kafafunsu da kuma amannar da suka yi cewa tabbas kawancensu da Sin ba karamin alheri ba ne, sun haifar da da mai ido bisa yadda Sin ta zama babbar kawar Afirka ta kasuwanci da babu kamarta a cikin shekaru 15 a jere, kana ta hudu wajen zuba jari a nahiyar.

Harkokin kasuwanci da zuba jari ba su samun tagomashi matukar babu ababen more rayuwa. Shi ya sa shawarar “Ziri Daya da Hanya Daya” wanda Sin ta kulla kawance a karkashinta da kasashen Afirka 52 da ma kungiyar tarayyar Afirka (a karshen 2022), ta kasance alfijir ga samar da dimbin ababen more rayuwa domin hanzarta kawo ci gaban da ya kamata a Afirka.

Yanzu haka, kamfanonin Sin fiye da 3,000 da ke aiki a nahiyar, suna gudanar da ayyukan kawo ci gaba daban-daban har ma an sami nasarar gina ko gyara layin dogo fiye da kilomita dubu 10 da titinan mota su ma kimanin dubu 100, baya ga tasoshin jiragen ruwa kusan 100.

ADVERTISEMENT

Sakamakon burin da Sin take da shi na cin moriyar juna a tsakaninta da Afirka, alkaluman baya-bayan nan sun nuna cewa a shekarar 2023, kasuwancin da ke tsakanin Sin da Afirka a mizanin shekara-shekara, ya habaka zuwa dala biliyan 282.1. Inda bangaren motoci masu aiki da sabbin makamashi ya karu da kashi 291 bisa dari sai baturan ‘lithium’ da Sin ke fitarwa zuwa nahiyar da ya karu zuwa kashi 109. Kana a hannu guda kuma, kayayyakin da Sin ke sayowa daga Afirka na amfanin gona masu kwaya suka karu da kashi 130 yayin da na kayan lambu suka habaka da kashi 32.
Abin bai tsaya nan ba, domin ganin Afirka ta kara samun damar kai kayayyakinta zuwa kasuwannin kasar Sin, kasar ta yi rangwamen biyan haraji da kashi 98 cikin dari a kan kayayyakin da ake biya musu harajin kwastam daga kasashe 20 da suka fi fuskantar koma-baya a nahiyar.
Bugu da kari, a farkon watanni shida na wannan shekarar kawai, kayayyakin da Sin ke shigowa da su kasarta daga Afirka sun kai na kimanin dala biliyan 60.1 wanda yake nuna an samu kari da kashi 14 a mizanin shekara-shekara. Haka nan, bayanai sun nuna cewa amfanin gonar da Sin ke shigo da su kasarta daga Afirka yana kara habaka inda a bana aka cika shekara bakwai a jere abin yana samun tagomashi.

Har ila yau, jarin da Sin ke zubawa a Afirka zuwa karshen 2023 ya zarce dala biliyan 40. A sakamakon haka ne ma, mu a nan Nijeriya muka samu tashar teku mai zurfi a Lekki da ke Jihar Legas wadda tuni manyan jiragen ruwa suka fara hada-hada a ciki. A baya, babban jirgin da zai zo tsohuwar tashar jiragen ruwa na Legas shi ne mai daukar kwantena 6,000 amma bisa samar da sabuwar tashar Lekki da taimakon kasar Sin, tuni har wani jirgin ruwa na kasar Faransa mai daukar kwantena 15,000 ya zo tashar don sauke kaya, inda hakan ke nuna cewa Nijeriya ta samu gagarumin ci gaban hada-hadar jiragen ruwa.

LABARAI MASU NASABA

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

A birnin Accra na kasar Ghana kuma, bisa taimakon kasar Sin, an zamanantar da tashar jiragen ruwan kamun kifi na zamani a Yankin Jamestown, da gyara tsohuwar tashar jiragen ruwa ta Bata a kasar Equatorial Guinea, sannan a 2023 kuma, an aza harsashin gina tashar jiragen ruwa na kamun kifi ta Kilwa a kasar Tanzania.

Akwai misalai da daman gaske da ke alamta yadda gaba za ta yi kyau a tsakanin Sin da Afirka bisa yadda harkokin cinikayya da tattalin arziki ke kara samun tagomashi.

  • Nesa Ta Zo Kusa a Afrika Karkashin Taimakon Sin

 

Afirka
Abdulrazaq Yahuza
+ postsBio
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana (2)
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Halaye 8 Na Rayuwa Da Aka Fi So A Yi Shiru Maimakon Magana A Ciki 
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Abdulrazaq Yahuza
    https://hausa.leadership.ng/author/abdulrazaq-yahuza/
    Majalisar Dinkin Duniya Ta Amince Da Wata Sabuwar Yarjejeniya Domin Inganta Tsarin Shugabancin Duniya

MASU ALAKA

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Sin Ke Ba Da Misali Ga Duniya Wajen Raya Aikin Noma Da Kauyuka

July 7, 2026
Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC
Ra'ayi Riga

Mu Leka Yadda Kasar Sin Ke Raya Hakkin Dan Adam Daga Taron Gefe Na UNHRC

July 6, 2026
Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin
Ra'ayi Riga

Ga “Itacen Kuka” Na Kasar Sin

July 1, 2026
Next Post
Bayan Fafatawa, Ƴan Ƙauye Sun Hallaka Ƴan Bindiga 37 A Zamfara

Bayan Fafatawa, Ƴan Ƙauye Sun Hallaka Ƴan Bindiga 37 A Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026
Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

July 8, 2026
Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

Badaƙalar PFIPC: Ban Taɓa Haɗuwa Da Gbajabiamila Ba – Adeyemi

July 8, 2026
NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

NNGF Ta Kaddamar Da Kwamitin Amintattu Na Gidauniyar Asusun Tsaro Ta Yankin

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.