• English
  • Business News
Thursday, July 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bunkasuwar Kasar Sin Mai Inganci Ta Ingiza Kwarewar Jama’arta

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Bunkasuwar Kasar Sin Mai Inganci Ta Ingiza Kwarewar Jama’arta
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shekarun nan na baya, wasu kafofin yada labarai na yamma sun yi ta karawa batun yawan jama’ar kasar Sin gishiri, musamman ma bayan da asusun kula da yawan jama’a na MDD ya gabatar da rahoton yanayin yawan jama’ar duniya na shekarar 2023 a ran 19 ga watan nan, inda aka yi kiyasin cewa, zuwa tsakiyar bana, yawan jama’ar kasar Indiya zai zarce Sin, inda Indiya za ta kai matsayin farko a duniya a bangare yawan jama’a, suna masu cewa, yanzu Sin za ta rasa fifikonta a fannin yawan jama’a, abin da zai haifar da koma bayan tattalin arzikinta.
To, shin ko wadannan kafofin yada labarai sun fadi gaskiyar halin da ake ciki a wannan fanni a Sin? Bari mu kalli alkaluman da aka fitar.

Ko da yake Sin na fuskantar wasu sabbin sauye-sauye a fannin yawan jama’a, amma har yanzu tana da ma’aikatan kwadago masu dimbin yawa. Sin ta gudanar kidayar jama’a a karo na 7 a shekarar 2020, alkaluma na nuna cewa, yawan al’umma masu shekaru tsakanin 16 zuwa 59 ya kai miliyan 880, kuma matsakaicin shekarunsu da haihuwa ya kai 38.8, wannan adadi ya nuna cewa, yawan masu jini a jika a kasar ya kai fiye da kashi 60%, wadanda suke taka muhimmyar rawa wajen ayyukan raya kasar. Kazalika, yawan yara na karuwa. Alkaluma na nuna cewa, yawan al’ummar kasar masu shekaru tsakanin 0 zuwa 14 ya karu da kashi 1.35% a cikin shekaru 10 da suka gabata, wanda ya kai kashi 17.95% na dukkan al’ummar kasar, wanda hakan ke zama tushen karuwar ma’aikatan kwadago a kasar a nan gaba.
A wani hannu na daban, fifikon yawan jama’a ba a fannin yawansu kadai yake bayyana ba, har ma da fannin kwarewarsu. Mai lambar yabo ta Nobel a fannin tattalin arziki Thodore W.Schults, ya dade yana nazari kan batun alakar tattalin arziki da ingancin jama’a, a ganinsa kwarewar jama’a na iya ingiza bunkasuwar tattalin arziki, don haka dole ne a inganta kwarewar jama’a. Alal misali, idan ana son yin girbi mai armashi, ba ma kawai ana bukatar gonaki masu fadi ba, kamata ya yi a shirya irrai masu inganci da amfani da taki mai kyau da sauransu.

Sin tana yin iyakacin kokarin bunkasa sha’anin ba da ilmi, matakin da ya sa matsakaicin matsayin samun ilmi na jama’ar kasar ya karu matuka. Ya zuwa yanzu, yawan mutanen kasar da shekarunsu ya kai shiga makarantar sakandare da jami’a wadanda kuma suka sama damar ya kai kashi 91.4% da 57.8%, adadan da suka karu da kashi 6.4% da 27.8% bisa na makamancin lokaci na shekaru 10 da suka gabata.

Bisa kididdigar da ma’aikatar ba da ilmi ta kasar Sin ta bayar, an ce, ya zuwa karshen shekarar 2021, matsakaicin shekarun da ma’aikatan kwadago suka kwashe wajen samun ilmi ya kai shekaru 10.9, wanda ya karu da shekara 1 bisa na shekarar 2012, a yayin da wannan adadi ya kai shekaru 14 ga karin sabbin ma’aikatan kwadago da aka samu a shekarar 2022, abin da ya nuna cewa, kwarewar ma’aikatan kwadago ya samu karuwa matuka. Wadannan adadai na samun karuwa a ko wace shekara, matakin da ya nuna cewa, kwarewar jama’ar kasar na ci gaba da karuwa, tare da samar da tallafi ga bunkasuwar tattalin arziki da al’ummar kasar Sin mai inganci.

Yawan jama’ar kasar Sin na rika karuwa, kuma kwarewarsu na dada ingantuwa, wadanda suke samun ilmi na zamani, zaman rayuwar jama’a na rika samun kyautatuwa, Abin da ya nuna cewa, fifikon da Sin take da shi a fannin yawan jama’a bai bace ba, ya zama sabon iri wato ingantuwar kwarewar jama’a. (Mai rubuta da fassarawa: MINA)1

Labarai Masu Nasaba

Binciken CGTN: Masu Bayyana Raayoyi Na Turai Sun Gamsu Da Moriyar Cinikayya Tsakanin Sin Da Turai Sama Da Ta Turai Da Amurka

Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bangaren Sin: Ya kamata Al’ummar Kasa Da Kasa Ta Goyi Bayan Kasashen Yankin Manyan Tabkuna Wajen Gina Makomar Bai Daya

Next Post

Buhari Ya Dakatar Da Kwamishinan Zaben Jihar Adamawa

Related

Binciken CGTN: Masu Bayyana Raayoyi Na Turai Sun Gamsu Da Moriyar Cinikayya Tsakanin Sin Da Turai Sama Da Ta Turai Da Amurka
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Masu Bayyana Raayoyi Na Turai Sun Gamsu Da Moriyar Cinikayya Tsakanin Sin Da Turai Sama Da Ta Turai Da Amurka

19 minutes ago
Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar
Daga Birnin Sin

Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar

1 hour ago
Xi Ya Bukaci Sin Da EU Su Samar Da Kwanciyar Hankali Da Tabbaci Ga Duniya
Daga Birnin Sin

Xi Ya Bukaci Sin Da EU Su Samar Da Kwanciyar Hankali Da Tabbaci Ga Duniya

2 hours ago
Anacláudia Rossbach: Ya Kamata Kasashen Afirka Su Koyi Darasi Daga Sin Na Kawar Da Talauci Da Kyautata Kauyuka Zuwa Birane
Daga Birnin Sin

Anacláudia Rossbach: Ya Kamata Kasashen Afirka Su Koyi Darasi Daga Sin Na Kawar Da Talauci Da Kyautata Kauyuka Zuwa Birane

3 hours ago
Tsibirin Ciniki Maras Shinge Na Hainan Na Ci Gaba Da Jawo Hankalin Jarin Waje
Daga Birnin Sin

Tsibirin Ciniki Maras Shinge Na Hainan Na Ci Gaba Da Jawo Hankalin Jarin Waje

4 hours ago
Ministan Lafiya Na Kamaru: Hadin-Gwiwa Ta Fuskar Kiwon Lafiya Ta Shaida Zumunci Mai Karfi Tsakanin Kamaru Da Sin
Daga Birnin Sin

Ministan Lafiya Na Kamaru: Hadin-Gwiwa Ta Fuskar Kiwon Lafiya Ta Shaida Zumunci Mai Karfi Tsakanin Kamaru Da Sin

9 hours ago
Next Post
Buhari Ya Dakatar Da Kwamishinan Zaben Jihar Adamawa

Buhari Ya Dakatar Da Kwamishinan Zaben Jihar Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Masu Bayyana Raayoyi Na Turai Sun Gamsu Da Moriyar Cinikayya Tsakanin Sin Da Turai Sama Da Ta Turai Da Amurka

Binciken CGTN: Masu Bayyana Raayoyi Na Turai Sun Gamsu Da Moriyar Cinikayya Tsakanin Sin Da Turai Sama Da Ta Turai Da Amurka

July 24, 2025
Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda

Abubuwan Da Ya Kamata Ku Sani Game Da Sabon Shugaban APC Na Ƙasa, Farfesa Yilwatda

July 24, 2025
Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar

Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar

July 24, 2025
Nijeriya Ta Gabatar Da Ƙudurin Karɓar Gasar Formula 1 A Abuja

Nijeriya Ta Gabatar Da Ƙudurin Karɓar Gasar Formula 1 A Abuja

July 24, 2025
Xi Ya Bukaci Sin Da EU Su Samar Da Kwanciyar Hankali Da Tabbaci Ga Duniya

Xi Ya Bukaci Sin Da EU Su Samar Da Kwanciyar Hankali Da Tabbaci Ga Duniya

July 24, 2025
An Fara Binciken Bidiyon Ciyar Da Sojoji Garaugarau

An Fara Binciken Bidiyon Ciyar Da Sojoji Garaugarau

July 24, 2025
Anacláudia Rossbach: Ya Kamata Kasashen Afirka Su Koyi Darasi Daga Sin Na Kawar Da Talauci Da Kyautata Kauyuka Zuwa Birane

Anacláudia Rossbach: Ya Kamata Kasashen Afirka Su Koyi Darasi Daga Sin Na Kawar Da Talauci Da Kyautata Kauyuka Zuwa Birane

July 24, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar da Sababbin Cibiyoyin Maganin Ciwon Daji

July 24, 2025
Gwamnatin Bauchi Ta Cire Shugaban Makaranta Kan Satar Kayan Gwamnati

Gwamnatin Bauchi Ta Cire Shugaban Makaranta Kan Satar Kayan Gwamnati

July 24, 2025
Tsibirin Ciniki Maras Shinge Na Hainan Na Ci Gaba Da Jawo Hankalin Jarin Waje

Tsibirin Ciniki Maras Shinge Na Hainan Na Ci Gaba Da Jawo Hankalin Jarin Waje

July 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.