• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bunkasuwar Kasar Sin Mai Inganci Ta Ingiza Kwarewar Jama’arta

byCMG Hausa
2 years ago
Kasar Sin

Shekarun nan na baya, wasu kafofin yada labarai na yamma sun yi ta karawa batun yawan jama’ar kasar Sin gishiri, musamman ma bayan da asusun kula da yawan jama’a na MDD ya gabatar da rahoton yanayin yawan jama’ar duniya na shekarar 2023 a ran 19 ga watan nan, inda aka yi kiyasin cewa, zuwa tsakiyar bana, yawan jama’ar kasar Indiya zai zarce Sin, inda Indiya za ta kai matsayin farko a duniya a bangare yawan jama’a, suna masu cewa, yanzu Sin za ta rasa fifikonta a fannin yawan jama’a, abin da zai haifar da koma bayan tattalin arzikinta.
To, shin ko wadannan kafofin yada labarai sun fadi gaskiyar halin da ake ciki a wannan fanni a Sin? Bari mu kalli alkaluman da aka fitar.

Ko da yake Sin na fuskantar wasu sabbin sauye-sauye a fannin yawan jama’a, amma har yanzu tana da ma’aikatan kwadago masu dimbin yawa. Sin ta gudanar kidayar jama’a a karo na 7 a shekarar 2020, alkaluma na nuna cewa, yawan al’umma masu shekaru tsakanin 16 zuwa 59 ya kai miliyan 880, kuma matsakaicin shekarunsu da haihuwa ya kai 38.8, wannan adadi ya nuna cewa, yawan masu jini a jika a kasar ya kai fiye da kashi 60%, wadanda suke taka muhimmyar rawa wajen ayyukan raya kasar. Kazalika, yawan yara na karuwa. Alkaluma na nuna cewa, yawan al’ummar kasar masu shekaru tsakanin 0 zuwa 14 ya karu da kashi 1.35% a cikin shekaru 10 da suka gabata, wanda ya kai kashi 17.95% na dukkan al’ummar kasar, wanda hakan ke zama tushen karuwar ma’aikatan kwadago a kasar a nan gaba.
A wani hannu na daban, fifikon yawan jama’a ba a fannin yawansu kadai yake bayyana ba, har ma da fannin kwarewarsu. Mai lambar yabo ta Nobel a fannin tattalin arziki Thodore W.Schults, ya dade yana nazari kan batun alakar tattalin arziki da ingancin jama’a, a ganinsa kwarewar jama’a na iya ingiza bunkasuwar tattalin arziki, don haka dole ne a inganta kwarewar jama’a. Alal misali, idan ana son yin girbi mai armashi, ba ma kawai ana bukatar gonaki masu fadi ba, kamata ya yi a shirya irrai masu inganci da amfani da taki mai kyau da sauransu.

Sin tana yin iyakacin kokarin bunkasa sha’anin ba da ilmi, matakin da ya sa matsakaicin matsayin samun ilmi na jama’ar kasar ya karu matuka. Ya zuwa yanzu, yawan mutanen kasar da shekarunsu ya kai shiga makarantar sakandare da jami’a wadanda kuma suka sama damar ya kai kashi 91.4% da 57.8%, adadan da suka karu da kashi 6.4% da 27.8% bisa na makamancin lokaci na shekaru 10 da suka gabata.

Bisa kididdigar da ma’aikatar ba da ilmi ta kasar Sin ta bayar, an ce, ya zuwa karshen shekarar 2021, matsakaicin shekarun da ma’aikatan kwadago suka kwashe wajen samun ilmi ya kai shekaru 10.9, wanda ya karu da shekara 1 bisa na shekarar 2012, a yayin da wannan adadi ya kai shekaru 14 ga karin sabbin ma’aikatan kwadago da aka samu a shekarar 2022, abin da ya nuna cewa, kwarewar ma’aikatan kwadago ya samu karuwa matuka. Wadannan adadai na samun karuwa a ko wace shekara, matakin da ya nuna cewa, kwarewar jama’ar kasar na ci gaba da karuwa, tare da samar da tallafi ga bunkasuwar tattalin arziki da al’ummar kasar Sin mai inganci.

Yawan jama’ar kasar Sin na rika karuwa, kuma kwarewarsu na dada ingantuwa, wadanda suke samun ilmi na zamani, zaman rayuwar jama’a na rika samun kyautatuwa, Abin da ya nuna cewa, fifikon da Sin take da shi a fannin yawan jama’a bai bace ba, ya zama sabon iri wato ingantuwar kwarewar jama’a. (Mai rubuta da fassarawa: MINA)1

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko
Daga Birnin Sin

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan
Daga Birnin Sin

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana
Daga Birnin Sin

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Next Post
Buhari Ya Dakatar Da Kwamishinan Zaben Jihar Adamawa

Buhari Ya Dakatar Da Kwamishinan Zaben Jihar Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version