ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bunkasuwar Kasar Sin Mai Inganci Ta Ingiza Kwarewar Jama’arta

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

Shekarun nan na baya, wasu kafofin yada labarai na yamma sun yi ta karawa batun yawan jama’ar kasar Sin gishiri, musamman ma bayan da asusun kula da yawan jama’a na MDD ya gabatar da rahoton yanayin yawan jama’ar duniya na shekarar 2023 a ran 19 ga watan nan, inda aka yi kiyasin cewa, zuwa tsakiyar bana, yawan jama’ar kasar Indiya zai zarce Sin, inda Indiya za ta kai matsayin farko a duniya a bangare yawan jama’a, suna masu cewa, yanzu Sin za ta rasa fifikonta a fannin yawan jama’a, abin da zai haifar da koma bayan tattalin arzikinta.
To, shin ko wadannan kafofin yada labarai sun fadi gaskiyar halin da ake ciki a wannan fanni a Sin? Bari mu kalli alkaluman da aka fitar.

Ko da yake Sin na fuskantar wasu sabbin sauye-sauye a fannin yawan jama’a, amma har yanzu tana da ma’aikatan kwadago masu dimbin yawa. Sin ta gudanar kidayar jama’a a karo na 7 a shekarar 2020, alkaluma na nuna cewa, yawan al’umma masu shekaru tsakanin 16 zuwa 59 ya kai miliyan 880, kuma matsakaicin shekarunsu da haihuwa ya kai 38.8, wannan adadi ya nuna cewa, yawan masu jini a jika a kasar ya kai fiye da kashi 60%, wadanda suke taka muhimmyar rawa wajen ayyukan raya kasar. Kazalika, yawan yara na karuwa. Alkaluma na nuna cewa, yawan al’ummar kasar masu shekaru tsakanin 0 zuwa 14 ya karu da kashi 1.35% a cikin shekaru 10 da suka gabata, wanda ya kai kashi 17.95% na dukkan al’ummar kasar, wanda hakan ke zama tushen karuwar ma’aikatan kwadago a kasar a nan gaba.
A wani hannu na daban, fifikon yawan jama’a ba a fannin yawansu kadai yake bayyana ba, har ma da fannin kwarewarsu. Mai lambar yabo ta Nobel a fannin tattalin arziki Thodore W.Schults, ya dade yana nazari kan batun alakar tattalin arziki da ingancin jama’a, a ganinsa kwarewar jama’a na iya ingiza bunkasuwar tattalin arziki, don haka dole ne a inganta kwarewar jama’a. Alal misali, idan ana son yin girbi mai armashi, ba ma kawai ana bukatar gonaki masu fadi ba, kamata ya yi a shirya irrai masu inganci da amfani da taki mai kyau da sauransu.

Sin tana yin iyakacin kokarin bunkasa sha’anin ba da ilmi, matakin da ya sa matsakaicin matsayin samun ilmi na jama’ar kasar ya karu matuka. Ya zuwa yanzu, yawan mutanen kasar da shekarunsu ya kai shiga makarantar sakandare da jami’a wadanda kuma suka sama damar ya kai kashi 91.4% da 57.8%, adadan da suka karu da kashi 6.4% da 27.8% bisa na makamancin lokaci na shekaru 10 da suka gabata.

ADVERTISEMENT

Bisa kididdigar da ma’aikatar ba da ilmi ta kasar Sin ta bayar, an ce, ya zuwa karshen shekarar 2021, matsakaicin shekarun da ma’aikatan kwadago suka kwashe wajen samun ilmi ya kai shekaru 10.9, wanda ya karu da shekara 1 bisa na shekarar 2012, a yayin da wannan adadi ya kai shekaru 14 ga karin sabbin ma’aikatan kwadago da aka samu a shekarar 2022, abin da ya nuna cewa, kwarewar ma’aikatan kwadago ya samu karuwa matuka. Wadannan adadai na samun karuwa a ko wace shekara, matakin da ya nuna cewa, kwarewar jama’ar kasar na ci gaba da karuwa, tare da samar da tallafi ga bunkasuwar tattalin arziki da al’ummar kasar Sin mai inganci.

Yawan jama’ar kasar Sin na rika karuwa, kuma kwarewarsu na dada ingantuwa, wadanda suke samun ilmi na zamani, zaman rayuwar jama’a na rika samun kyautatuwa, Abin da ya nuna cewa, fifikon da Sin take da shi a fannin yawan jama’a bai bace ba, ya zama sabon iri wato ingantuwar kwarewar jama’a. (Mai rubuta da fassarawa: MINA)1

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

Kasar Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace
Daga Birnin Sin

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin
Daga Birnin Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Next Post
Buhari Ya Dakatar Da Kwamishinan Zaben Jihar Adamawa

Buhari Ya Dakatar Da Kwamishinan Zaben Jihar Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026
Sabbin Ministoci

Kafa ‘Yansandan Jihohi: Majalisa Ta Amince Da Tsarin ‘Yar Tinƙe Wajen Kaɗa Ƙuri’a 

June 24, 2026
Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

Sin Ta Gabatar Da Tsarin Karfafa Kwarin Gwiwar Kamfanoni Masu Jarin Waje

June 24, 2026
Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Kasar Burundi: Dangantakar Afirka Da Sin Misali Ce Ta Hadin Gwiwar Kasashe Masu Tasowa

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.