ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bunkasuwar Kasar Sin Mai Inganci Ta Ingiza Kwarewar Jama’arta

by CMG Hausa
3 years ago
Kasar Sin

Shekarun nan na baya, wasu kafofin yada labarai na yamma sun yi ta karawa batun yawan jama’ar kasar Sin gishiri, musamman ma bayan da asusun kula da yawan jama’a na MDD ya gabatar da rahoton yanayin yawan jama’ar duniya na shekarar 2023 a ran 19 ga watan nan, inda aka yi kiyasin cewa, zuwa tsakiyar bana, yawan jama’ar kasar Indiya zai zarce Sin, inda Indiya za ta kai matsayin farko a duniya a bangare yawan jama’a, suna masu cewa, yanzu Sin za ta rasa fifikonta a fannin yawan jama’a, abin da zai haifar da koma bayan tattalin arzikinta.
To, shin ko wadannan kafofin yada labarai sun fadi gaskiyar halin da ake ciki a wannan fanni a Sin? Bari mu kalli alkaluman da aka fitar.

Ko da yake Sin na fuskantar wasu sabbin sauye-sauye a fannin yawan jama’a, amma har yanzu tana da ma’aikatan kwadago masu dimbin yawa. Sin ta gudanar kidayar jama’a a karo na 7 a shekarar 2020, alkaluma na nuna cewa, yawan al’umma masu shekaru tsakanin 16 zuwa 59 ya kai miliyan 880, kuma matsakaicin shekarunsu da haihuwa ya kai 38.8, wannan adadi ya nuna cewa, yawan masu jini a jika a kasar ya kai fiye da kashi 60%, wadanda suke taka muhimmyar rawa wajen ayyukan raya kasar. Kazalika, yawan yara na karuwa. Alkaluma na nuna cewa, yawan al’ummar kasar masu shekaru tsakanin 0 zuwa 14 ya karu da kashi 1.35% a cikin shekaru 10 da suka gabata, wanda ya kai kashi 17.95% na dukkan al’ummar kasar, wanda hakan ke zama tushen karuwar ma’aikatan kwadago a kasar a nan gaba.
A wani hannu na daban, fifikon yawan jama’a ba a fannin yawansu kadai yake bayyana ba, har ma da fannin kwarewarsu. Mai lambar yabo ta Nobel a fannin tattalin arziki Thodore W.Schults, ya dade yana nazari kan batun alakar tattalin arziki da ingancin jama’a, a ganinsa kwarewar jama’a na iya ingiza bunkasuwar tattalin arziki, don haka dole ne a inganta kwarewar jama’a. Alal misali, idan ana son yin girbi mai armashi, ba ma kawai ana bukatar gonaki masu fadi ba, kamata ya yi a shirya irrai masu inganci da amfani da taki mai kyau da sauransu.

Sin tana yin iyakacin kokarin bunkasa sha’anin ba da ilmi, matakin da ya sa matsakaicin matsayin samun ilmi na jama’ar kasar ya karu matuka. Ya zuwa yanzu, yawan mutanen kasar da shekarunsu ya kai shiga makarantar sakandare da jami’a wadanda kuma suka sama damar ya kai kashi 91.4% da 57.8%, adadan da suka karu da kashi 6.4% da 27.8% bisa na makamancin lokaci na shekaru 10 da suka gabata.

ADVERTISEMENT

Bisa kididdigar da ma’aikatar ba da ilmi ta kasar Sin ta bayar, an ce, ya zuwa karshen shekarar 2021, matsakaicin shekarun da ma’aikatan kwadago suka kwashe wajen samun ilmi ya kai shekaru 10.9, wanda ya karu da shekara 1 bisa na shekarar 2012, a yayin da wannan adadi ya kai shekaru 14 ga karin sabbin ma’aikatan kwadago da aka samu a shekarar 2022, abin da ya nuna cewa, kwarewar ma’aikatan kwadago ya samu karuwa matuka. Wadannan adadai na samun karuwa a ko wace shekara, matakin da ya nuna cewa, kwarewar jama’ar kasar na ci gaba da karuwa, tare da samar da tallafi ga bunkasuwar tattalin arziki da al’ummar kasar Sin mai inganci.

Yawan jama’ar kasar Sin na rika karuwa, kuma kwarewarsu na dada ingantuwa, wadanda suke samun ilmi na zamani, zaman rayuwar jama’a na rika samun kyautatuwa, Abin da ya nuna cewa, fifikon da Sin take da shi a fannin yawan jama’a bai bace ba, ya zama sabon iri wato ingantuwar kwarewar jama’a. (Mai rubuta da fassarawa: MINA)1

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Kasar Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Daga Birnin Sin

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
Daga Birnin Sin

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Next Post
Buhari Ya Dakatar Da Kwamishinan Zaben Jihar Adamawa

Buhari Ya Dakatar Da Kwamishinan Zaben Jihar Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.