• English
  • Business News
Thursday, October 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Canji Kudi: Matakin Da Gwamnonin Arewa Suka Dauka Barazana Ce Ga Dimokuradiyya

by Dokta Nasir Aminu
3 years ago
Kudi

LABARAI MASU NASABA

Raya Al’ada: Bikin Kalankuwa Na 2025 A Kano

Me Ake Nufi Da Ado? 

A halin da ake ciki a yanzu a bangaren masu yakin neman zaben dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Asiwaju Bola Ahmad Tinubu suna kallo Shugaban kasa Muhammadu Buhari kamar irin tsohon aboki da aka bata da shi a baya, wanda wannan zamantakewar ta yi tsami a tsakanin bangarorin biyu.

Magoya bayan Tinubu da gwamnonin jam’iyyar APC suna sukan dokar Buhari na sauya naira a matsayin abun da bai dace ba, kuma ya saka talakawa cikin wahala.

  • Me Ya Sa Amurka Ta Ga Balan-balan A Samaniya A Tsayin Mita 18000 A Maimakon Gajimare Mai Guba A Samaniyar Ohio Dake Kasar?
  • Kasar Sin Za Ta Soke Haraji Kan Kayan Da Ake Shigowa Daga Habasha Da Burundi Da Nijar 

Shi ma kansa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC ya zargi mutane da dama da suke yin masa bi-ta da kulli kuma suna nuna cewa kamar ba su suke yi ba. Ba don batanci ga wani ba, ina fatan Tinubu yana sane da cewa a yanzu yana tare da mutumin nan da ya rubuta littafin hatsarin ma’aikacin gwamnati wanda ya ware wasu shafuka har 4 a cikin littafin yana bayar da labarin yadda Atiku ya hana shi zambantar gwamnatin Nijeriya.

Ba wani lokaci mai tsawo ba, gwamnonin Arewa da Tinubu sun yi kira ga mutane da su goyi bayan gwamnati a kan duk wani abu da suke yi. A cewarsu, hakan shi ne kishin kasa. Amma a yanzu gwamnonin sai su tafi kafafen yada labarai suna bude wa Buhari wuta don ya warware masu matsalarsu a nan take, wanda zai kasance don biyan bukatarsu ne akarin kansu. Suna bukatar ya kara lokacin karbar tsofaffin kudade har sai bayan zaben shugaban kasa, don su cika alkawarinsu na ganin an zabi Tinubu a matsayin shugaban kasa.

Kudurin Buhari na sauya naira shi ne ya kawar da sayen kuru’u. Ba kamar Buhari ba, shi Tinubu yana ganin wannan tsarin na sauya naira ana yin masa bi-ta da kullin zama shugaban kasa ne. Wasu jam’iyyun siyasa sun goyi bayan wannan kuduri, saboda suna ganin zai taimaka masu wajen daina amfani da kudi a lokutan zabe. Ina nan a kan ra’ayina na illar sauya kudi da amfani da dokar takaita yawon kudade da lokacin da aka bayar, wanda ba shi ne abun da za mu tattauan a yanzu ba. Haka kuma idan wannan tsarin doka da aka sanya an sami nasara, Nijeriya za ta zama kasa ta farko a duniya da ta yi amfani da sauya kudi don yaki da magudin zabe. A saboda haka, abu ne da ‘yan kasa suke bukata a gudanar da ingantaccen zabe kuma sahihi a Nijeriya wanda zai kara karfin tsarin dimokuradiyya.

Abubuwan da al’umma suke bukata shi ne, ya kamata su kasance a gaba a yakin neman zabe lokacin zabe ba wai son kai ba. A wannan karon, gwamnonin Arewa sun fi mayar da hankali ne a kan son ransu da biyan bukatar kansu. Za mu iya gane haka daga yanayin Ganduje da El-Rufai a lokacin da gwamnonin Arewa suka yi taro da Buhari. Wadannan mutanen guda biyu sun bar wasu tarihi a jihohin Arewa.

Ganduje ya yi korafin cewa wannan tsarin da Emefiele ya yi ne don cutar da wasu; ma’ana akwai manufa. Wanda ya rika kokarin kawo wasu bayanai da ke nuna wasu daga cikin gwamnati ba sa goyoin bayan Tinubu da har ya kai ga kunnin Buhari. Amma dai su al’umma suna gani.

A cewar Emefiele, manufarsa na sauya naira shi ne a aiwatar da dokar nan na rage yawon kudade a hannun jama’a wanda zai rage hauhawar farashin kayayyaki. Wannan abu ne mai kyau da za a iya nasara a kai duk da yake ba shi a littafan nazarin tattalin arziki. Dole mu yi amfani da kalamansa.

A fili dai Buhari ya nuna goyon bayansa ga Tinubu, har yana yakin neman zabe tare da shi ma ya kaddamar da shi a jiharsa ta Katsina da wasu jihohin. Gwamnoni sun san cewa Buhari dattijo ne kuma mai magana daya. Ya bayyana cewa shi ya tuntubi Emefiele. Wasu za su iya tuna abun da ya yi a shekarar 1984, kuma yana sane da irin kuncin rayuwar da mutane suka shiga a wancan lokaci.

Mazari kaka dan shekara 63 wanda ya fito kafafen yada labarai a mabambantan lokuta yana sukar abun wanda ba ya bin dokar kotu ma. A daidai lokacin ne da yake zantawa da BBC Hausa inda ya barje guminsa. Ya caccaki dattawan Arewa da wasu ‘yan Billa da kowa ke magana a kai. Ban so in yi magana a kan ra’ayinsa na dattawa al’umma za su yi masa alkalanci. Ya bayyana cewa shi fa ba ya tsoron kowa kuma bai taba tsugunawa kowa daga cikinsu ba. Sai ga wasu hotuna an zakulo ya tsuguna wa wasu daga cikinsu har da Aisha da yake fada da ita. Shin wadannan ‘yan Billa suna da karfi haka?

Akwai lokacin da ya taba zagin manya-manyan Nijeriya da suka bayar da gudunmuwa wajen gina kasa, wato Ahmadu Bello Sardauna da Azikiwe da Awolowo, kawai sun tara kudi ne abun su wanda suka amfana da shi a siyasance. Kuma ya ki neman gafara a kan wadannan kalamai nasa. A saboda haka, mene ne ba zai fada a yanzu ba? Batun gaskiya amsar ba zai yi dadi ba kuma sakamakon wadannan karyayyaki ba za su yi dadi ba.

A kasar da take da manyan matsaloli da yunwa sakamakon talauci da matsalar rashin kudi da karancin mai. Tinubu da kowa ya sanshi da sakin layi idan yana jawabi wanda kuma yake ta yawan maimaita wannan sakin layin, jagororin Yarbawa sun karbe shi.  Wani daga cikin dattawansu ma yana kiran yaki idan mulkin shugaban kasa bai koma yankin kudu ba. Idan muka ci gaba da jin abubuwa irin haka da kuma maganganu daga bakin gwamnoni, tsarin dimokuradiyyarmu zai iya fuskantar barazanar.

A wani bangaren kuma, za su iya amfani da wata hanyar don ganin sun sauya wa shugaban kasa ra’ayi. Zai iya kasancewa ba daidai yake ba, amma kurakurai biyu ba za su taba zama gyara ba. A saboda haka, dimokuradiyyarmu da hukumominmu su ne abun da gwamnati ya kamata ta duba su, duban da ya dace.

Idan ba a dauki matakan da suka dace ba, Nijeriya na iya fuskantanr matsalar da ta faru a ranar 6 ga watan Janairu a zaben Amurka. Wannan zanga-zangar da Amurkawa suka yi ne, ‘yan Brazil suka kwaikwaya makonni kadan kafin zabe. Ga wadanda ba su sani ba, wannan rikicin ne ya zama matsala ga zaben kasar wanda ya yi kama da na Nijeriya. Idan haka ta faru, abun Allah ya kiyaye, hukumomi su tuna da wadanda suka haddasa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Raya Al’ada: Bikin Kalankuwa Na 2025 A Kano
Bakon Marubuci

Raya Al’ada: Bikin Kalankuwa Na 2025 A Kano

October 3, 2025
Me Ake Nufi Da Ado? 
Bakon Marubuci

Me Ake Nufi Da Ado? 

September 26, 2025
Ranar Hausa: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka
Bakon Marubuci

Ranar Hausa: Ba Ka Iyawa Duk Dagewarka Kuma Ba A Yaba Maka

August 30, 2025
Next Post
Abin Da Ya Sa Farashin Kayan Masarufi Ya Fadi Warwas A Nijeriya

Abin Da Ya Sa Farashin Kayan Masarufi Ya Fadi Warwas A Nijeriya

LABARAI MASU NASABA

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Sojoji Sun Kama Fitaccen Ɗan Bindiga Babawo Badoo Da Wasu 37 A Filato 

October 23, 2025
Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna

Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna

October 23, 2025
Gwamna Abba Ya Jaddada Mubaya’arsa Ga Kwankwaso 

Gwamna Abba Ya Jaddada Mubaya’arsa Ga Kwankwaso 

October 23, 2025
Shugabannin jam’iyyar PDP Na Arewa Sun Amince Da Turaki A Matsayin Ɗan Takarar Shugabancin Jam’iyyar Na Ƙasa

Shugabannin jam’iyyar PDP Na Arewa Sun Amince Da Turaki A Matsayin Ɗan Takarar Shugabancin Jam’iyyar Na Ƙasa

October 23, 2025
Yajin aiki

Gwamnatin Tarayya Ta Jajantawa Waɗanda Fashewar Tankar Mai Ta Rutsa Da Su A Neja 

October 23, 2025
Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas

Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Naira Biliyan 2.5 Na Aikin Haƙo Uranium, Mai Da Iskar Gas

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Diflomasiyyar Shugabanni Na Matukar Taka Rawar Gani Wajen Jagorantar Dangantakar Sin Da Amurka

October 22, 2025
NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

NUJ Reshen Kano Ta Taya Ahmed Mu’azu Murna Kan Naɗin Da NAHCON Ta Yi Masa

October 23, 2025
Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11

October 22, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Cafke Wani Matashi Ɗan Shekara 15 Da Ake Zargi Da Yin Fashi Da Makami A Gombe

October 22, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.