• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Canjin Kudi: Buhari Ya Yi Ganawar Sirri Da Emefiele

by Sadiq
3 years ago
Buhari

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya yi ganawar sirri da Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), Godwin Emefiele da shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa (EFCC), AbdulRasheed Bawa da Sakataren Gwamnatin Tarayya, Boss Mustapha da kuma shugaban ma’aikatan fadar shugaban kasa, Farfesa Ibrahim Gambari game da halin da ake cikin na karancin takardar kudin Naira.

Kazalika gwamnan Sakkwato, Aminu Waziri Tambuwal da takwaransa na Jihar Kebbi, Atiku Bagudu, su ma sun halarci ganawar sirrin da aka yi a yammacin ranar Talata.

  • Gwajin Dawo Da Rukunonin Yawon Bude Ido Zuwa Kasashen Ketare Da Sin Ke Yi Zai Farfado Da Kasuwar Yawon Bude Ido Ta Duniya
  • Masana’antun Kasar Sin Sun Taka Rawa Wajen Farfado Da Tattalin Arzikin Duniya

An gudanar da wannan zaman ne a daidai lokacin da ake fama da matsanancin karancin takardar kudin Naira wanda ya haddasa zanga-zanga a wasu sassan Nijeriya tare da kaddamar da hari kan wasu bankuna da jami’an tsaro.

A ranar Juma’a ne, shugaba Buhari ya roki ‘yan Nijeriya da su ba shi wa’adin kwanaki bakwai domin magance matsalar karancin takardun Naira wanda ya samo asali sakamakon shirin CBN na sauya fasalin Naira 1000 da 500 da kuma 200.

Nan da ranar 10 ga wannan wata ne, wa’adin da shugaban ya nema zai cika, yayin da mutane suka zura idanu domin ganin yadda za ta kaya.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da ake shirin gudanar da zaben shugaban kasa nan da ‘yan kwanaki kalilan, yayin da batun karancin Naira ya yamutsa hazon siyasar kasar nan, inda har dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu ke zargin cewa, zagon kasa ake yi masa, shi ya sa aka bullo da shirin sauya fasalin Naira gami da kirkirar matsalar karancin man fetur.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta
Manyan Labarai

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin
Manyan Labarai

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Next Post
Jam’iyyun Adawa Ba Su So Buhari Ya Yi Nasara Kan Tsarin Canjin Kudi – Lai Mohammed

Jam'iyyun Adawa Ba Su So Buhari Ya Yi Nasara Kan Tsarin Canjin Kudi - Lai Mohammed

LABARAI MASU NASABA

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

SSANU Da NASU Sun Yi Zanga-Zanga A Abuja Kan Rashin Cika Alƙawarin Gwamnati

October 9, 2025
An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

An Umurci Manyan Makarantu Su Mayar Da Kuɗaɗen TETFund Da Ba Su Kashe Ba

October 9, 2025
Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

Kotu Ta Ba Da Umarnin Kama Tsohon Shugaban INEC, Mahmood Yakubu, Kan Saɓa Umarninta

October 9, 2025
Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.