• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Canjin Kudi: Dalilin Da El-Rufai Ba Ya Ganin Girman Buhari A Yanzu – Shehu Sani

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Canjin Kudi: Dalilin Da El-Rufai Ba Ya Ganin Girman Buhari A Yanzu – Shehu Sani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tsohon Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Sanata Shehu Sani ya bayyana dalilan da ya sa gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ke sukar shugaban kasa Muhammadu Buhari kan batun canjin kudi.

Ya mayar da martani ne biyo bayan kalaman gwamnan game da zaben shugaban kasa da ake shirin shiga.

  • Boko Haram Ta Hallaka Malaman Makaranta Sama Da 2000 A Shekara 8
  • Gwamnatin Neja Ta Bayar Umarnin Kama Duk Wanda Ya Ki Karbar Tsofaffin Kudi

A wata hira da ya yi da a Abuja a ranar Talata.

“Ya kamata Buhari ya jira karin wasu kalaman sukar daga Elrufai saboda dalilai uku.

“Biyayyar da El-Rufai ke yi wa Buhari ta kare. Ya samu duk abin da yake so a wajen Buhari, yanzu Buhari ba shi da amfani a wajensa.

Labarai Masu Nasaba

An NaÉ—a Farfesa Adamu MuÆ™amin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

“Karfin Buhari da tasirinsa a siyasa ya zo karshe; El-Rufai ya koma tsagin Tinubu.

“El-Rufai yana yi wa Buhari hidima ne don biyan bukatar kansa.

“Buhari ya watsar da dukkan abokansa nagari da suka yi masa hidima kuma suka sadaukar da kansu tsawon shekaru a Kaduna saboda kaunarsa ga El-Rufai. Mun gargade shi a kan El-Rufai amma ya yi biris; lokaci ya yi da Buhari zai san cewa abin da ya girka ya kwashe.

“Ban taba yarda cewa El-Rufai na son Buhari ba, ban taba yarda El-Rufai ya taba yi wa Buhari biyayya ba, na san duk wani abu da ya faru da shi, kuma na san cewa wannan rana za ta zo, El-Rufai ya ce yana son Buhari, kawai dai ya kwantar da kai ne domin ya samu duk abin da yake so a wurin Buhari kuma yanzu Buhari ba shi da wani amfani a gare shi.

“El-Rufa’i ya kwashe shekaru takwas yana yabon Buhari kuma Buhari ya kwashe shekaru takwas yana yabon El-Rufai duk lokacin da ya zo Kaduna; Buhari ya aminta ya ajiye kunama a kusa da shi.

“Ya kamata Tinubu ya kula da El-Rufai. El-Rufai ya fi son Amaechi ba Tinubu ba. Wakilan APC na Kaduna Amaechi suka zaba ba Tinubu ba.

“Ya kamata Tinubu ya yi taka-tsan-tsan don kada El-Rufai ya yi masa abin da ya yi wa Buhari.

“El-Rufai bai taba son talaka ba kuma ba zai taba son shi ba,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BuhariCanjin KudiEl-RufaiKadunaShehu Sani
ShareTweetSendShare
Previous Post

Boko Haram Ta Hallaka Malaman Makaranta Sama Da 2000 A Shekara 8

Next Post

Girgizar Kasar Turkiyya: An Ceto Wata Yarinya Bayan Shafe Awa 178 A Cikin Baraguzai

Related

An NaÉ—a Farfesa Adamu MuÆ™amin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An NaÉ—a Farfesa Adamu MuÆ™amin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

2 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

22 hours ago
Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara
Manyan Labarai

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

2 days ago
Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin
Manyan Labarai

Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin

2 days ago
Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano
Manyan Labarai

Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano

2 days ago
Jami’an Tsaro Sun DaÆ™ile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun DaÆ™ile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

2 days ago
Next Post
Girgizar Kasar Turkiyya: An Ceto Wata Yarinya Bayan Shafe Awa 178 A Cikin Baraguzai

Girgizar Kasar Turkiyya: An Ceto Wata Yarinya Bayan Shafe Awa 178 A Cikin Baraguzai

LABARAI MASU NASABA

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

Man United Sun Kammala Sayen Benjamin Sesko Daga RB Leipzig

August 9, 2025
An NaÉ—a Farfesa Adamu MuÆ™amin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

An NaÉ—a Farfesa Adamu MuÆ™amin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

August 9, 2025
Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

Gwamnan Kano Ya Sallami Mataimaka Biyu Kan Zargin Karkatar Da Kayan Tallafi

August 9, 2025
Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu

August 9, 2025
Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

August 9, 2025
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

August 9, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya

August 9, 2025
Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

August 9, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

August 9, 2025
ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.