• English
  • Business News
Monday, August 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CBN Ya Kara Yawan Kudin Ruwa Zuwa Kaso 18 Cikin 100 Daga Kaso 17

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
CBN Ya Kara Yawan Kudin Ruwa Zuwa Kaso 18 Cikin 100 Daga Kaso 17
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), ya bayyana cewa, kwamitin manufofin kudin bankin ya kada kuri’ar kara yawan kudin ruwa da kashi 50 zuwa kashi 18 cikin 100 daga kaso 17 da digo 5 cikin 100.

Wannan mataki dai an dauke shi ne don dakile hauhawar farashin kayayyaki a halin yanzu da ya kai kaso 21 cikin dari kuma saboda a saukaka wa ‘yan kasa da kuma bunkasa tattalin arzikin kasar nan.

  • APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP
  • Sin Ta Yi Kira Da A Gaggauta Dawo Da Taimakon Kudin Da Ake Baiwa Sudan Ba Tare Da Wani Sharadi Ba

Gwamnan CBN, Godwin Emefiele, ya bayyana matsayar da kwamitin da manufofin bankin ya cimma bayan taronsu na yini biyu wanda mambobi 10 suka amince da daga kudin ruwan daga kaso 17.5 cikin 100 zuwa kaso 18 wanda ke nufin an samu karin kashi 50 a kan yadda yake a da a ranar Talata yayin da yake karanta sanarwar taron MPC karo na biyu na 2023 a birnin tarayya Abuja.

Malam Haruna Bala Mustapha, ne daraktan lura da harkokin bankuna na babban bankin CBN, ya ce taron kwamitin manufofin kudi da aka kammala a ranar Talata ya duba muhimman abubuwa ciki da matsalar hauhawar farashi da ya addabi kasar nan don kawo sauki da kuma irin tasirin da rushewar wasu bankunan kasar Amurka za su iya yi a Nijeriya.

Sai dai, a nasa bangaren, masanin tattalin arziki a Nijeriya, Malam Yusha’u Aliyu, ya ce matakin na kwamitin manufofin kudi na bankin CBN zai kara hauhawar farashi ne kawai, yana mai cewa ana yin irin wannan karin ne don rage yawan kudi da ke yawo tsakanin al’umma, wanda bankin ya riga ya janye kudaden daga hannun al’umma.

Labarai Masu Nasaba

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

Baya ga batun kara kudin ruwa, Emefiele ya bayyana cewa bankin ya goyi bayan hukuncin kotun koli na a ci gaba da mu’amala da tsoffin takardun kudi baya ga sabbin da aka sake fasalinsu wanda adadinsu ya kai kusan Naira tiriliyan daya.

Kazalika, Emefiele ya ce babban banki na da kwarin gwiwa a kan bankunan kasuwancin Nijeriya wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyansu ganin yadda suke ci gaba da jure wa asalin jarin da suka zuba na kaso 13 cikin 100, ba da lamuni wanda mutumin da ya karbin rance bai sanya lokacin fara biyansu ba na kaso 4.2 cikin 100 da kuma kudaden ajiyar bankunan da aka kara zuwa naira tiriliyan goma sha hudu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CBNKudin Haraji
ShareTweetSendShare
Previous Post

APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP

Next Post

Zaben 2023 Ya Nuna Dimokuradiyyar Nijeriya Ta Bunkasa -Buhari

Related

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare
Manyan Labarai

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

18 hours ago
Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 
Da ɗumi-ɗuminsa

Ma’aikatan Jinya Sun Janye Yajin Aiki Bayan Gwamnatin Tarayya Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu 

2 days ago
Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO
Manyan Labarai

Kongo Na Neman Goyon Bayan Nijeriya Kan Shugabancin UNESCO

2 days ago
Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu
Manyan Labarai

Yarjejeniyar Dala Biliyan Ɗaya Da Ƙasar Brazil Za Ta Haɓaka Fannin Noma A Nijeriya —Tinubu

2 days ago
ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye
Manyan Labarai

ADC Za Ta Kayar Da Tinubu A 2027 – Dino Melaye

2 days ago
Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauke Gawuna A Matsayin Shugaban Kwamitin Gudanarwar BUK, Ya Maye Gurbinsa Da Kaita 

2 days ago
Next Post
Zaben 2023 Ya Nuna Dimokuradiyyar Nijeriya Ta Bunkasa -Buhari

Zaben 2023 Ya Nuna Dimokuradiyyar Nijeriya Ta Bunkasa -Buhari

LABARAI MASU NASABA

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

Wani Babban Jigon APC Ya Fice Daga Jam’iyyar A Katsina

August 3, 2025
Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi

August 3, 2025
Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu?

August 3, 2025
Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

Dangote Ya Ɗauki Nauyin Bikin Baje Kolin Gidajen Afrika Da Mahalarta Ƙasashe 21

August 3, 2025
An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

An Fara Bayar Da Hidimomin Da Suka Shafi Sauka Da Tashi Domin Gasar Wasanni Ta Duniya Ta Chengdu

August 3, 2025
Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

Rikici Ya Ɓarke A Zaɓen Ribas, Ƴan PDP Sun Fito A Matsayin Ƴan Takarar APC

August 3, 2025
Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

Ana Gaggauta Ayyukan Gyara Tituna Da Gadojin Da Ambaliya Ta Lalata A Arewacin Kasar Sin

August 3, 2025
Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

Shugabar Tanzania Ta Kaddamar Da Cibiyar Cinikayya Da Jigila Da Sin Ta Gina A Kasar

August 3, 2025
Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

Manoma Sun Caccaki Tinubu Kan Ƙarfafa Shigo Da Shinkafa Da Masara Daga Ƙasashen Waje

August 3, 2025
Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

Amurka Ta Gargaɗi Ƴan Nijeriya Kan Zuwa Ƙasarta Domin Haihuwa

August 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.