ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CBN Ya Kara Yawan Kudin Ruwa Zuwa Kaso 18 Cikin 100 Daga Kaso 17

by Sadiq
3 years ago
CBN

Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), ya bayyana cewa, kwamitin manufofin kudin bankin ya kada kuri’ar kara yawan kudin ruwa da kashi 50 zuwa kashi 18 cikin 100 daga kaso 17 da digo 5 cikin 100.

Wannan mataki dai an dauke shi ne don dakile hauhawar farashin kayayyaki a halin yanzu da ya kai kaso 21 cikin dari kuma saboda a saukaka wa ‘yan kasa da kuma bunkasa tattalin arzikin kasar nan.

  • APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP
  • Sin Ta Yi Kira Da A Gaggauta Dawo Da Taimakon Kudin Da Ake Baiwa Sudan Ba Tare Da Wani Sharadi Ba

Gwamnan CBN, Godwin Emefiele, ya bayyana matsayar da kwamitin da manufofin bankin ya cimma bayan taronsu na yini biyu wanda mambobi 10 suka amince da daga kudin ruwan daga kaso 17.5 cikin 100 zuwa kaso 18 wanda ke nufin an samu karin kashi 50 a kan yadda yake a da a ranar Talata yayin da yake karanta sanarwar taron MPC karo na biyu na 2023 a birnin tarayya Abuja.

ADVERTISEMENT

Malam Haruna Bala Mustapha, ne daraktan lura da harkokin bankuna na babban bankin CBN, ya ce taron kwamitin manufofin kudi da aka kammala a ranar Talata ya duba muhimman abubuwa ciki da matsalar hauhawar farashi da ya addabi kasar nan don kawo sauki da kuma irin tasirin da rushewar wasu bankunan kasar Amurka za su iya yi a Nijeriya.

Sai dai, a nasa bangaren, masanin tattalin arziki a Nijeriya, Malam Yusha’u Aliyu, ya ce matakin na kwamitin manufofin kudi na bankin CBN zai kara hauhawar farashi ne kawai, yana mai cewa ana yin irin wannan karin ne don rage yawan kudi da ke yawo tsakanin al’umma, wanda bankin ya riga ya janye kudaden daga hannun al’umma.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Baya ga batun kara kudin ruwa, Emefiele ya bayyana cewa bankin ya goyi bayan hukuncin kotun koli na a ci gaba da mu’amala da tsoffin takardun kudi baya ga sabbin da aka sake fasalinsu wanda adadinsu ya kai kusan Naira tiriliyan daya.

Kazalika, Emefiele ya ce babban banki na da kwarin gwiwa a kan bankunan kasuwancin Nijeriya wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyansu ganin yadda suke ci gaba da jure wa asalin jarin da suka zuba na kaso 13 cikin 100, ba da lamuni wanda mutumin da ya karbin rance bai sanya lokacin fara biyansu ba na kaso 4.2 cikin 100 da kuma kudaden ajiyar bankunan da aka kara zuwa naira tiriliyan goma sha hudu.

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Zaben 2023 Ya Nuna Dimokuradiyyar Nijeriya Ta Bunkasa -Buhari

Zaben 2023 Ya Nuna Dimokuradiyyar Nijeriya Ta Bunkasa -Buhari

LABARAI MASU NASABA

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.