ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CBN Ya Kara Yawan Kudin Ruwa Zuwa Kaso 18 Cikin 100 Daga Kaso 17

by Sadiq
3 years ago
CBN

Gwamnan Babban Bankin Nijeriya (CBN), ya bayyana cewa, kwamitin manufofin kudin bankin ya kada kuri’ar kara yawan kudin ruwa da kashi 50 zuwa kashi 18 cikin 100 daga kaso 17 da digo 5 cikin 100.

Wannan mataki dai an dauke shi ne don dakile hauhawar farashin kayayyaki a halin yanzu da ya kai kaso 21 cikin dari kuma saboda a saukaka wa ‘yan kasa da kuma bunkasa tattalin arzikin kasar nan.

  • APC Da Uba Sani Ba Su Lashe Zaben Gwamnan Kaduna Ba -PDP
  • Sin Ta Yi Kira Da A Gaggauta Dawo Da Taimakon Kudin Da Ake Baiwa Sudan Ba Tare Da Wani Sharadi Ba

Gwamnan CBN, Godwin Emefiele, ya bayyana matsayar da kwamitin da manufofin bankin ya cimma bayan taronsu na yini biyu wanda mambobi 10 suka amince da daga kudin ruwan daga kaso 17.5 cikin 100 zuwa kaso 18 wanda ke nufin an samu karin kashi 50 a kan yadda yake a da a ranar Talata yayin da yake karanta sanarwar taron MPC karo na biyu na 2023 a birnin tarayya Abuja.

ADVERTISEMENT

Malam Haruna Bala Mustapha, ne daraktan lura da harkokin bankuna na babban bankin CBN, ya ce taron kwamitin manufofin kudi da aka kammala a ranar Talata ya duba muhimman abubuwa ciki da matsalar hauhawar farashi da ya addabi kasar nan don kawo sauki da kuma irin tasirin da rushewar wasu bankunan kasar Amurka za su iya yi a Nijeriya.

Sai dai, a nasa bangaren, masanin tattalin arziki a Nijeriya, Malam Yusha’u Aliyu, ya ce matakin na kwamitin manufofin kudi na bankin CBN zai kara hauhawar farashi ne kawai, yana mai cewa ana yin irin wannan karin ne don rage yawan kudi da ke yawo tsakanin al’umma, wanda bankin ya riga ya janye kudaden daga hannun al’umma.

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Baya ga batun kara kudin ruwa, Emefiele ya bayyana cewa bankin ya goyi bayan hukuncin kotun koli na a ci gaba da mu’amala da tsoffin takardun kudi baya ga sabbin da aka sake fasalinsu wanda adadinsu ya kai kusan Naira tiriliyan daya.

Kazalika, Emefiele ya ce babban banki na da kwarin gwiwa a kan bankunan kasuwancin Nijeriya wajen sauke nauyin da ya rataya a wuyansu ganin yadda suke ci gaba da jure wa asalin jarin da suka zuba na kaso 13 cikin 100, ba da lamuni wanda mutumin da ya karbin rance bai sanya lokacin fara biyansu ba na kaso 4.2 cikin 100 da kuma kudaden ajiyar bankunan da aka kara zuwa naira tiriliyan goma sha hudu.

MASU ALAKA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe
Manyan Labarai

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare
Manyan Labarai

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu
Manyan Labarai

Mutfwang Ya Buƙaci Sojoji Su Ƙara Ƙaimi A Aikinsu

July 16, 2026
Next Post
Zaben 2023 Ya Nuna Dimokuradiyyar Nijeriya Ta Bunkasa -Buhari

Zaben 2023 Ya Nuna Dimokuradiyyar Nijeriya Ta Bunkasa -Buhari

LABARAI MASU NASABA

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026
Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Fitar Da Tsarin Sanya Ido Don Inganta Muhalli Da Muhallin Halittu Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 16, 2026
Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

Nazari Game Da Damammakin Da Sin Ta Samar Cikin Rahoton Ci Gaban Tattalin Arzikinta Na Rabin Farkon Shekara

July 16, 2026
Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

Gwamna Bala Ya Rushe Kwamitin Gudanarwar Wikki Tourists Bayan Rashin Nasararta A Gasar NPFL

July 16, 2026
Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

Tasirin Da Sabbin Hare-haren Amurka Da Iran Za Su Iya Haifarwa Duniya

July 16, 2026
Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

Sin Na Kokarin Sanya Ci Gaban Fasaha Ya Inganta Bunkasa Da Wadatar Dan Adam

July 16, 2026
Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

Tinubu Ya Miƙa Wa Shettima Takardar Tabbatar Da Shi Abokin Takararsa A Zaɓen 2027

July 16, 2026
Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Kazakhstan

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.