• Leadership Hausa
Sunday, June 4, 2023
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Sana’a Sa’a
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ce-ce-kucen Al’umma Ke Ci Wa Mawakan Kannywood Tuwo A Kwarya —Jibrin Yahaya

by Rabi'at Sidi Bala
3 months ago
in Nishadi
0
Ce-ce-kucen Al’umma Ke Ci Wa Mawakan Kannywood Tuwo A Kwarya —Jibrin Yahaya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wannan makon mun kawo maku cigaban tattaunawar da muka kawo muku a fitowarmu ta makon da ya gabata. Kamar kowanne mako wannan shafi ya kan zakulo maku fitattun jarumai, har ma da masu tasowa daga cikin masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood.

Tare da manyan mawaka har ma da kanana, kana da wadanda suka yi fuce. A yau ma shafin na tafe da bako na musamman wanda ya shafe tsahon shekaru goma a cikin masana’antar shirya fina-finan Hausa ta Kannywood, Jarumi mai taka rawa da kuma shirya fina-finai cikin masana’atar kannywood, kana shahararren mawakin wakokin Hausa da suka shafi kowanne bangare. JIBRIN YAHAYA wanda aka fi sani da MISTER D MAIWAKA, Ya bayyanawa masu karatu musabbabin fara wakarsa tare da dalilansa na shiga masana’antar Kannywood, har ma da wasu batutuwan da suka shafi sana’arsa ta fim. Ga dai yadda tattaunawar tasu da wakiliyarmu RABI’AT SIDI BALA Kamar haka:

Kana fidda bidiyos ne ko iya odiyo kake yi ?
Ina fidda ‘Audio’ da kuma Bidiyo.

Idan mutum yana son samun wakokinka ta wacce hanya zai nema?
Wakokina za a same su a ‘Youtube Channel’ dina mai suna ‘MD 24 TB’ ko a WhatsApp line kamar haka 08029157961 ko wurin ‘yan ‘Download’.

Wacce irin matsala kake fuskanta game da harkokin fina-finanku da kuma bangaren waka?
Matsala ba ta wuce ce-ce-ku-ce na mutanan gari wanda shi daman dan Adam ba a iya masa, kuma duk abin da za ka yi in kai bawa ka tsarkake zuciyarka duk abin da mutum zai fada yai ta fada domin Allah na kallon mu kuma zai wa bawa a kan aibata wanda ya ke yi.

Labarai Masu Nasaba

Burina Tinubu Ya Tilasta Wa Maza Kara Aure —Rashida Mai Sa’a

Na Cinma Duk Abin Da Nake So A Fim – Suwaiba Makauniya

Me za ka ce da su masu ce ce-ku ce a kanku?
Kalma daya ce su daina, hakan ba daidai bane. Domin ko da mutum bai haifa ba ‘yan uwansa sun haifa, kuma duk abin da kai za a yi ma wani, kairan o sharren.

Toh! Ya batun aure fa?
Ina da aure, Allah ya azurta ni da ‘ya’ya hudu, daya ta rasu Allah ya ji kanta. Uku na raye Khalid da Auwal, sai Fatima, Allah ya albarkace su Ameen.

Shin ka taba fuskantar wani kalubale daga wajen matarka game da aikinka, musamman ma yadda jama’a ke kallon yanayin aikin na cakude da wasu matan daban?
Gaskiya so daya na taba haduwa da hakan, shi ma ba wai na bacin rai bane, wani lokacin ne aka je aka ce da ita gani can da mata sai ta ce hanyar cin abincin sa ce a haka, Allah da ikonsa ni dai ban taba jin an ce gashi can an kama shi da wata mace ba, na ga a cikin garin nan kuma wanda baya fim ko waka an kama shi da mace ba. ita ta gayan ba matar aboki na ce take gaya min har ita ma matar abokin nawa ta ce ‘hanyar cin abincin sa ce a haka kuma ko wane bawa baya tsallake kaddarar sa.

Mene ne burinka na karshe a rayuwa?
Shi ne na gama da duniya lafiya.

Me za ka ce da makaranta shafin Rumbun Nishadi?
Su ci gaba da kasancewa tare da wannan shafi, domin karanta gaskiyar zance game da Jarumi ko Jaruma haka ma mawaka, domin shafi ne da yake fidda masu kallo daga cikin duhun ka ce na ce akan jarumi, irin na wasu mutanen.

Me za ka ce da ita kanta Jaridar LEADERSHIP Hausa?
Ina yi mata fatan alkhairi, ubangiji ya kara daukakata ya sa ta fi haka, ya karawa ma’aikatanta hazaka da basira.

Ko kana da wadanda za ka gaisar?
Kwarai kuwa, sai dai amma suna da yawa ba zan iya fado su ba, zan yi su a dunkule, bayan gaisuwa ga dukkanin iyayena, ‘yan uwana, da matata da kuma iyalaina baki daya, ina gaida duk wadanda suka zamo na kusa da ni abokaina da kuma masoyana a duk inda suke, da sauran al’ummar musulmi baki daya.

Muna godiya ka huta lafiya.
Ni ma na gode.

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Umarci NSIB Ta Binciko Musabbabin Hatsarin Jirgin Kasan Legas

Next Post

Babban Mai Tattara Sakamakon Zaben Atiku A Ogun Ya Sauya Sheka Zuwa APC

Related

Burina Tinubu Ya Tilasta Wa Maza Kara Aure —Rashida Mai Sa’a
Nishadi

Burina Tinubu Ya Tilasta Wa Maza Kara Aure —Rashida Mai Sa’a

4 days ago
Na Cinma Duk Abin Da Nake So A Fim – Suwaiba Makauniya
Nishadi

Na Cinma Duk Abin Da Nake So A Fim – Suwaiba Makauniya

2 weeks ago
Jibrin Yahaya
Nishadi

Zumunci Da Hadin Kan Marubuta Na Matukar Burge Ni – Manab ‘Yar Baba

4 weeks ago
Jibrin Yahaya
Nishadi

Na Fi Son ‘Acting’ Na Masifa Don Na Fi Sabawa Da Shi – Sadiya Musa

4 weeks ago
Har Yanzu Wasu Na Yi Wa ‘Yan Fim Kallon Mutanen Banza —Auwal West
Nishadi

Har Yanzu Wasu Na Yi Wa ‘Yan Fim Kallon Mutanen Banza —Auwal West

1 month ago
Har Yanzu Wasu Na Yi Wa ‘Yan Fim Kallon Mutanen Banza —Auwal West
Nishadi

Har Yanzu Wasu Na Yi Wa ‘Yan Fim Kallon Mutanen Banza —Auwal West

1 month ago
Next Post
Babban Mai Tattara Sakamakon Zaben Atiku A Ogun Ya Sauya Sheka Zuwa APC

Babban Mai Tattara Sakamakon Zaben Atiku A Ogun Ya Sauya Sheka Zuwa APC

LABARAI MASU NASABA

Hajjin Bana: Adadin Alhazan Nijeriya A Saudiyya A Yanzun Ya kai 24,324 

Hajjin Bana: Adadin Alhazan Nijeriya A Saudiyya A Yanzun Ya kai 24,324 

June 4, 2023
Tawagar Sojin Injiniya Ta Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Kasar Sin Ta Tallafawa Kongo Kinshasa Ta Fuskar Aikin Ceto

Tawagar Sojin Injiniya Ta Wanzar Da Zaman Lafiya Ta Kasar Sin Ta Tallafawa Kongo Kinshasa Ta Fuskar Aikin Ceto

June 4, 2023
Ana Bin Jihar Kano Bashin Sama Da Naira Biliyan 240, Inji Abba Gida-gida 

Gwamna Yusuf Ya Kori Jami’an Cibiyar Alhazan Kananan Hukumomi 44 Na Jihar Kano

June 4, 2023
Me Ya Sa BRICS Ke Kara Samun Karbuwa Daga Kasashen Duniya

Me Ya Sa BRICS Ke Kara Samun Karbuwa Daga Kasashen Duniya

June 4, 2023
Sana’ar Kwalliya

Sana’ar Kwalliya

June 4, 2023
Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli

Ranar Muhalli Ta Duniya: Kwanturolan NIS Na Jihar Ribas Ya Gargadi Jami’ai Kan Gurbata Muhalli

June 4, 2023
Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

Mutane 18 Sun Mutu A Wani Hatsarin Mota A Kano

June 4, 2023
Takaitaccen Tarihin Ka’idojin Rubutun Hausa (II)

Takaitaccen Tarihin Ka’idojin Rubutun Hausa (II)

June 4, 2023
Dalilin Da Manoman Rama A Jihar Katsina Ke Kara Habaka

Dalilin Da Manoman Rama A Jihar Katsina Ke Kara Habaka

June 4, 2023
Farashin Tumatir Ya Karye Bayan Ghana Da Kamaru Sun Turo Shi Kasuwannin Nijeriya

Farashin Tumatir Ya Karye Bayan Ghana Da Kamaru Sun Turo Shi Kasuwannin Nijeriya

June 4, 2023
Advertise with us

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2022 Leadership Media Group - All Right Reserved.