• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Masana’antar Kannywood: Ganin Kitse Ake Wa Rogo – Mai Sana’a

byRabilu Sanusi Bena and Sulaiman
8 months ago
Kannywood

Guda daga cikin manyan jarumai, masu shirya fina-finan barkwanci da fadakarwa, Musa Mai Sana’a, ya bayyana abin da ya sani dangane da ci gaban da ake tunanin Masana’antar Kannywood ta samu, inda ya ce; ko shakka babu ganin kitse ake yi wa rogo, idan ana yin maganar ci gaba a wannan masana’anta ta shirya fina-finan Hausa.

A wata hira da aka yi da Mai Sana’ar, a gidan rediyon muryar Amurka, ya bayyana batutuwa da dama da suka shafi rayuwa da sauran al’amura na yau da kullum, tunda farko dai; jarumin ya yi bayani a kan yadda wasu lokutan yake samo labarun wasu daga cikin fina-finansa, don nishadantarwa ko fadakar da masu kallo.

  • An Kammala Aikin Tsugunar Da Mutane A Gundumar Tingri Ta Sin Bayan Bala’in Girgizar Kasa
  • AFCON 2025: Nijeriya Za Ta Fafata Da Tunisiya A Wasannin Rukuni

“Wasu lokutan, nakan tashi na tafi wani waje, wanda idan na fada; ba lallai a yarda ba. Misali, idan na so nishadi ko na dan bukaci yawon shakatawa, nakan tafi wurare kamar wajen da masu sana’ar Adaidaita Sahu ke tsayawa; su dan huta bayan sun yi aiki sun gaji, da sauran wurare da za ka ga rayuwa iri-iri, wanda hakan zai iya ba ka dama ka kwaikwayi abubuwan da ka gani; ka mayar da shi shirin fim, domin mutane su amfana; su kuma karu da ilimin zaman duniya”, in ji shi.

Da yake amsa tambaya kan yadda yake samo wasu ayoyi da hadisan da yake yawan amfani da su a fina-finansa, sai ya ce; duk da shi ba Malamin Addini ba ne, amma kuma Almajiri ne da ya yi karatun addini bakin gwargwado. Ya kara da cewa, ba Darakta ba ne yake rubuta masa wadannan ayoyi ko hadisai da yake karantowa a fim ba, kawai dai yana fadar su ne daga abin da ya koya a gaban Malamansa na addini.

Mai Sana’a ya ci gaba da bayyana cewa, dangane da abin da mutane ke fada cewa, gwamnatin tarayya ta yi matukar taka rawar gani ko ta sallami Masana’antar Kannywood, a kan gudunmawar da suka bayar a lokacin yakin neman zabe ta hanyar nada wasu daga cikin manyan jarumai manyan mukaman gwamnati, ko kusa ba haka abin yake ba; domin kuwa ba masana’antar aka sallama ba, illa kawai daidaikun wasu daga cikinsu.

LABARAI MASU NASABA

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

Har ila yau ya ce, idan aka yi maganar mukaman da gwamnatin tarayya da ta jihohi suka bai wa wasu daga cikinmu, ba yana nufin cewa; an taimaki masana’antar ba ne, domin kuwa; mafi yawancin wadanda suka samu wadannan mukamai, babu wani ci gaba ko hobbasa da suka yi wajen ciyar da Masana’antar Kannywood gaba.

Musa ya ce, illa kawai dai suna taimakon kansu da kuma na kusa da su, wanda kuma ba haka ya dace a ce suna yi ba, dalili kuwa shi ne, har yau babu wani daga cikin masana’antar tamu da ya taba samun wani mukamin gwamnati, ya taimaka wa ita kanta masana’antar, illa kalilan daga cikinmu.

A bangaren abokanan fada kuwa a Masana’antar Kannywood, Mai Sana’a ya ce; duk da wannan magana da yake yi a halin yanzu, babu wani a masana’antar da zai bude baki ya ce; shi ne abokin fadansa, domin kuwa dukkanin wadanda suke tare a masana’antar, yana kallonsu da mutunci duk da cewa dai wasu sun fi wasu zama mutanen kirki.

A karshe, Musa ya bayyana cewa; idan Allah ya kawo wata sana’ar da ta fi wannan harka ta fim a wajensa, zai ajiye ta a cikin lumana; ba wai don ta yi masa tsaroro ba ba, kawai dai yana fatan wata rana wani abu daban zai zo, wanda ya fi masa harkar fim din, domin babu wani mutum a duniya da ba ya son cigaba, idan kuma wannan sana’a ita ce tsira a wajensa, yana fatan mutuwa a cikinta, ba tare da ya bar ta ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano
Nishadi

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

October 6, 2025
An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana
Nishadi

An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

October 4, 2025
Daga Kallon Fina-finan Indiya Na Samu Sha’awar Fadawa Kannywood – Kamalu Mijinyawa
Nishadi

Daga Kallon Fina-finan Indiya Na Samu Sha’awar Fadawa Kannywood – Kamalu Mijinyawa

September 28, 2025
Next Post
Tafiye-Tafiye A Fadin Sin Ya Zarce Miliyan 300 A Rana Ta 4 Ta Hutun Bikin Bazara

Tafiye-Tafiye A Fadin Sin Ya Zarce Miliyan 300 A Rana Ta 4 Ta Hutun Bikin Bazara

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version