ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ci Gaban Masana’antar Kannywood: Ganin Kitse Ake Wa Rogo – Mai Sana’a

by Rabilu Sanusi Bena and Sulaiman
1 year ago
Kannywood

Guda daga cikin manyan jarumai, masu shirya fina-finan barkwanci da fadakarwa, Musa Mai Sana’a, ya bayyana abin da ya sani dangane da ci gaban da ake tunanin Masana’antar Kannywood ta samu, inda ya ce; ko shakka babu ganin kitse ake yi wa rogo, idan ana yin maganar ci gaba a wannan masana’anta ta shirya fina-finan Hausa.

A wata hira da aka yi da Mai Sana’ar, a gidan rediyon muryar Amurka, ya bayyana batutuwa da dama da suka shafi rayuwa da sauran al’amura na yau da kullum, tunda farko dai; jarumin ya yi bayani a kan yadda wasu lokutan yake samo labarun wasu daga cikin fina-finansa, don nishadantarwa ko fadakar da masu kallo.

  • An Kammala Aikin Tsugunar Da Mutane A Gundumar Tingri Ta Sin Bayan Bala’in Girgizar Kasa
  • AFCON 2025: Nijeriya Za Ta Fafata Da Tunisiya A Wasannin Rukuni

“Wasu lokutan, nakan tashi na tafi wani waje, wanda idan na fada; ba lallai a yarda ba. Misali, idan na so nishadi ko na dan bukaci yawon shakatawa, nakan tafi wurare kamar wajen da masu sana’ar Adaidaita Sahu ke tsayawa; su dan huta bayan sun yi aiki sun gaji, da sauran wurare da za ka ga rayuwa iri-iri, wanda hakan zai iya ba ka dama ka kwaikwayi abubuwan da ka gani; ka mayar da shi shirin fim, domin mutane su amfana; su kuma karu da ilimin zaman duniya”, in ji shi.

ADVERTISEMENT

Da yake amsa tambaya kan yadda yake samo wasu ayoyi da hadisan da yake yawan amfani da su a fina-finansa, sai ya ce; duk da shi ba Malamin Addini ba ne, amma kuma Almajiri ne da ya yi karatun addini bakin gwargwado. Ya kara da cewa, ba Darakta ba ne yake rubuta masa wadannan ayoyi ko hadisai da yake karantowa a fim ba, kawai dai yana fadar su ne daga abin da ya koya a gaban Malamansa na addini.

Mai Sana’a ya ci gaba da bayyana cewa, dangane da abin da mutane ke fada cewa, gwamnatin tarayya ta yi matukar taka rawar gani ko ta sallami Masana’antar Kannywood, a kan gudunmawar da suka bayar a lokacin yakin neman zabe ta hanyar nada wasu daga cikin manyan jarumai manyan mukaman gwamnati, ko kusa ba haka abin yake ba; domin kuwa ba masana’antar aka sallama ba, illa kawai daidaikun wasu daga cikinsu.

LABARAI MASU NASABA

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

Har ila yau ya ce, idan aka yi maganar mukaman da gwamnatin tarayya da ta jihohi suka bai wa wasu daga cikinmu, ba yana nufin cewa; an taimaki masana’antar ba ne, domin kuwa; mafi yawancin wadanda suka samu wadannan mukamai, babu wani ci gaba ko hobbasa da suka yi wajen ciyar da Masana’antar Kannywood gaba.

Musa ya ce, illa kawai dai suna taimakon kansu da kuma na kusa da su, wanda kuma ba haka ya dace a ce suna yi ba, dalili kuwa shi ne, har yau babu wani daga cikin masana’antar tamu da ya taba samun wani mukamin gwamnati, ya taimaka wa ita kanta masana’antar, illa kalilan daga cikinmu.

A bangaren abokanan fada kuwa a Masana’antar Kannywood, Mai Sana’a ya ce; duk da wannan magana da yake yi a halin yanzu, babu wani a masana’antar da zai bude baki ya ce; shi ne abokin fadansa, domin kuwa dukkanin wadanda suke tare a masana’antar, yana kallonsu da mutunci duk da cewa dai wasu sun fi wasu zama mutanen kirki.

A karshe, Musa ya bayyana cewa; idan Allah ya kawo wata sana’ar da ta fi wannan harka ta fim a wajensa, zai ajiye ta a cikin lumana; ba wai don ta yi masa tsaroro ba ba, kawai dai yana fatan wata rana wani abu daban zai zo, wanda ya fi masa harkar fim din, domin babu wani mutum a duniya da ba ya son cigaba, idan kuma wannan sana’a ita ce tsira a wajensa, yana fatan mutuwa a cikinta, ba tare da ya bar ta ba.

Kannywood
Rabilu Sanusi Bena
+ posts Bio
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    FIFA Na Nazarin Faɗaɗa Gasar Kofin Duniya Zuwa Ƙasashe 64
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Harry Kane: Lashe Kofin Duniya Ya Fi Mini Muhimmanci Fiye da Takalmin Zinare
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Kofin Duniya: Na fi Son Faransa Ta Kara Da Argentina A Wasan Ƙarshe A Kan Ingila — Vieira
  • Rabilu Sanusi Bena
    https://hausa.leadership.ng/author/rabilu-sanusi-bena/
    Argentina Ta Kai Zagayen Kwata Fainal Bayan Nunawa Egypt Ƙwanji
Kannywood
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
  • Sulaiman
    Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
  • Sulaiman
    Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030
  • Sulaiman
    Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Labarai

Daraktan Hollywood Carl Rinsch Zai Shafe Watanni 30 A Gidan Gyaran Hali

July 12, 2026
Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina
Nishadi

Zan Iya Auren Namiji Komai Talaucinsa Muddin Muna Son Junanmu -Maryam Labarina

June 14, 2026
Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi
Nishadi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

June 14, 2026
Next Post
Tafiye-Tafiye A Fadin Sin Ya Zarce Miliyan 300 A Rana Ta 4 Ta Hutun Bikin Bazara

Tafiye-Tafiye A Fadin Sin Ya Zarce Miliyan 300 A Rana Ta 4 Ta Hutun Bikin Bazara

LABARAI MASU NASABA

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026
Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

Tsohon Sanatan Gombe, Bayero Nafada, Ya Fice Daga PDP Bayan Ganawa da Shugabannin APC

July 14, 2026
ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.