• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cibiyar Ba Da Agaji Ta Sarki Salman Na Saudiya Ta Fara Tiyatar Zuciya A Nijeriya

by yahuzajere
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Saudiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Cibiyar Ba da Agaji ta Sarki Salman na Saudiya ta kaddamar da aikin kiwon tiyatar cututtukan zuciya ga manya a Jihar Kano, inda tawagar likitocin sa kai guda 20 suka gudanar bisa hadin gwiwa da Kungiyar Kasashen Musulmi ta Duniya.

Tun daga lokacin da aka fara aikin, tawagar likitocin sa kai masu kishin kasa a cibiyar sun gudanar da gagarumin aikin tiyatar zuciya guda hudu da aka samu nasara a kai. A dukkan tiyatar da aka yi, likitocin sun nuna kwarewa da jin kai, lamarin da ya nuna kyakkyawan misali bisa dukufar da likitocin suka yi wajen warkar da marasa lafiya da kuma kara kwarin gwiwa ga mabukata.

Saudiya

Aikin dai ya zo ne a cikin tsarin tallafin da Masarautar Saudiya ta bayar ta sashen bayar da agaji na jin kan al’umma, watau cibiyar agaji ta Sarki Salman don tallafa wa fannin kiwon lafiya a Nijeriya, da kuma kafa tsarin gudanar da aiki na sa kai a tsakanin al’ummar Saudiyya, bisa manufofin da masarautar ta sa gaba da ake son cimmawa nan da 2030.

Wannan hadin gwiwa ya zama shaida ga irin karfin da hadin kai yake da shi na samar da sauki a lokacin ibtila’i, inda kungiyoyi da hukumomin da ke da nisa da juna za su rika hada karfi don sauya rayuwar jama’a bila’adadin.

Labarai Masu Nasaba

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

A yayin da aka kaddamar da aikin kiwon lafiyar na sa kai a Jihar Kano, hakan ya nuna kyakykyawan tausayi da jin kan bil’adama lokacin ibtila’i. A duk tiyatar zuciyar da aka yi, an rubuta bayanan sauyin da aka gani, wanda ke nuna babban tasiri da alherin da masarautar ta Saudiyya take aiwatarwa a Nijeriya.

Saudiya
Wani likita tare da majinyacin da ya yi wa aiki

Idan dai za a iya tunawa, a watan Yuni ne masarautar Saudiyya ta kuduri aniyar samar da cibiyar tiyatar zuciya a Kano domin rage radadin rashin lafiyar da ke bukatar tiyatar bugun zuciya a kasar.

Khalid Ahmad Al-adamawi, karamin jakadan Saudiyya a Nijeriya, wanda ya ziyarci Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano, ya yi wa gwamnan bayani dangane da aikin tiyatar zuciyar da ake yi a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH).

A kwanakin baya ne dai Cibiyar Bayar da Agaji ta Sarki Salman ta kudiri aniyar samar da aikin jinya na sa-kai domin kula da masu cutar yoyon fitsari a jihar Kano. Inda daga ranar 6 zuwa 11 ga Agusta 2023, likitocin sa kai suka gudanar da aikin tiyata 65.

  • Sojojin Nijar Na Neman Goyon Bayan Kasashe Daban-Daban

Gidauniyar tana aiwatar da jerin shirye-shirye da tsare-tsare don samar wa marasa lafiya a duk fadin duniya da ingantaccen magani da sauran harkokin kiwon lafiyar da ba a samu a yankunan jama’ar da ake yi wa.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AgajiLikitociSaudiyaZuciya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Soji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 28, Sun Kama 114, Sun Kubutar Da Mutane 82- Hedikwatar Tsaro

Next Post

Shin Gobarar Da Ta Tashi A Maui Za Ta Iya Tada ‘Yan Siyasar Amurka?

Related

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

11 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

20 hours ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

22 hours ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

23 hours ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

2 days ago
Next Post
Shin Gobarar Da Ta Tashi A Maui Za Ta Iya Tada ‘Yan Siyasar Amurka?

Shin Gobarar Da Ta Tashi A Maui Za Ta Iya Tada 'Yan Siyasar Amurka?

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.