• English
  • Business News
Thursday, July 31, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cibiyar Ba Da Agaji Ta Sarki Salman Na Saudiya Ta Fara Tiyatar Zuciya A Nijeriya

by yahuzajere
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Saudiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Cibiyar Ba da Agaji ta Sarki Salman na Saudiya ta kaddamar da aikin kiwon tiyatar cututtukan zuciya ga manya a Jihar Kano, inda tawagar likitocin sa kai guda 20 suka gudanar bisa hadin gwiwa da Kungiyar Kasashen Musulmi ta Duniya.

Tun daga lokacin da aka fara aikin, tawagar likitocin sa kai masu kishin kasa a cibiyar sun gudanar da gagarumin aikin tiyatar zuciya guda hudu da aka samu nasara a kai. A dukkan tiyatar da aka yi, likitocin sun nuna kwarewa da jin kai, lamarin da ya nuna kyakkyawan misali bisa dukufar da likitocin suka yi wajen warkar da marasa lafiya da kuma kara kwarin gwiwa ga mabukata.

Saudiya

Aikin dai ya zo ne a cikin tsarin tallafin da Masarautar Saudiya ta bayar ta sashen bayar da agaji na jin kan al’umma, watau cibiyar agaji ta Sarki Salman don tallafa wa fannin kiwon lafiya a Nijeriya, da kuma kafa tsarin gudanar da aiki na sa kai a tsakanin al’ummar Saudiyya, bisa manufofin da masarautar ta sa gaba da ake son cimmawa nan da 2030.

Wannan hadin gwiwa ya zama shaida ga irin karfin da hadin kai yake da shi na samar da sauki a lokacin ibtila’i, inda kungiyoyi da hukumomin da ke da nisa da juna za su rika hada karfi don sauya rayuwar jama’a bila’adadin.

Labarai Masu Nasaba

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

A yayin da aka kaddamar da aikin kiwon lafiyar na sa kai a Jihar Kano, hakan ya nuna kyakykyawan tausayi da jin kan bil’adama lokacin ibtila’i. A duk tiyatar zuciyar da aka yi, an rubuta bayanan sauyin da aka gani, wanda ke nuna babban tasiri da alherin da masarautar ta Saudiyya take aiwatarwa a Nijeriya.

Saudiya
Wani likita tare da majinyacin da ya yi wa aiki

Idan dai za a iya tunawa, a watan Yuni ne masarautar Saudiyya ta kuduri aniyar samar da cibiyar tiyatar zuciya a Kano domin rage radadin rashin lafiyar da ke bukatar tiyatar bugun zuciya a kasar.

Khalid Ahmad Al-adamawi, karamin jakadan Saudiyya a Nijeriya, wanda ya ziyarci Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano, ya yi wa gwamnan bayani dangane da aikin tiyatar zuciyar da ake yi a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH).

A kwanakin baya ne dai Cibiyar Bayar da Agaji ta Sarki Salman ta kudiri aniyar samar da aikin jinya na sa-kai domin kula da masu cutar yoyon fitsari a jihar Kano. Inda daga ranar 6 zuwa 11 ga Agusta 2023, likitocin sa kai suka gudanar da aikin tiyata 65.

  • Sojojin Nijar Na Neman Goyon Bayan Kasashe Daban-Daban

Gidauniyar tana aiwatar da jerin shirye-shirye da tsare-tsare don samar wa marasa lafiya a duk fadin duniya da ingantaccen magani da sauran harkokin kiwon lafiyar da ba a samu a yankunan jama’ar da ake yi wa.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AgajiLikitociSaudiyaZuciya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Soji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 28, Sun Kama 114, Sun Kubutar Da Mutane 82- Hedikwatar Tsaro

Next Post

Shin Gobarar Da Ta Tashi A Maui Za Ta Iya Tada ‘Yan Siyasar Amurka?

Related

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC
Manyan Labarai

Matatar Mai Ta Fatakwal Ba Ta Siyarwa Ba Ce – NNPC

14 hours ago
Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Yi Allah-wadai Da Zanga-zangar Ƙin Jinin ’Yan Nijeriya A Ghana

16 hours ago
Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Ceto Mutane 28 Da ‘Yan Bindiga Suka Sace A Katsina

18 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Jihar Neja

20 hours ago
Tinubu Ya Nada Ribadu Da Wasu A Matsayin Masu Ba Shi Shawara
Manyan Labarai

Ku Daina Kashe Mutane Ko Ku MiÆ™a Wuya – Ribadu Ya GargaÉ—i ‘Yan Bindiga

23 hours ago
Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace
Manyan Labarai

Cikin Wata 2 Ƴansanda Sun Damƙe Mutane 5,488, Sun Ceto 170 Da Aka Sace

1 day ago
Next Post
Shin Gobarar Da Ta Tashi A Maui Za Ta Iya Tada ‘Yan Siyasar Amurka?

Shin Gobarar Da Ta Tashi A Maui Za Ta Iya Tada 'Yan Siyasar Amurka?

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

Sin Ta Dade Tana Aiki Tukuru Kan Kiyaye Zaman Lafiya Da Kwanciyar Hankali Na Yanki

July 30, 2025
Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega

July 30, 2025
Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

Salisu Yusuf Ya Ajiye Aikinsa Na Kocin Nasarawa United

July 30, 2025
Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

Rikicin Makiyaya Da Manoma: An Kashe Mutum Daya, Gidaje 31 Sun Kone A Abuja

July 30, 2025
Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

Binciken CGTN: Za A Ci Gaba Da Nuna Kyakkyawan Fata Ga Bunkasar Sin Nan Da Shekaru 5

July 30, 2025
Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

Wasan Kwallon Mutum-Mutumi Ya Nuna Yadda Sin Ta Shirya Wa Karbar Bakuncin Wasanninsu Na Duniya

July 30, 2025
Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

Gwamnati Za Ta Kafa Cibiyoyin Kiwo a Yankuna Shida — Ƙaramin Ministan Noma

July 30, 2025
Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

Gine-gine 8 Sun Ruguje, Makabarta Ta Nutse A Wata Sabuwar Ambaliyar Ruwa A Borno

July 30, 2025
Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

Kwamitin Kolin JKS Ya Shirya Taron Bita Tare Da Wadanda Ba ’Yan Jam’iyyar Ba 

July 30, 2025
Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana

Za A Bude Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Koli Na 20 Na JKS A Watan Oktoban bana

July 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.