ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sojojin Nijar Na Neman Goyon Bayan Kasashe Daban-Daban

by Sadiq
3 years ago
Nijar

Sojojin da ke mulkin Nijar na ci gaba da neman goyon bayan kasashe musamman wadanda ba su nuna adawa da juyin mulkin da suka yi ba a kasar ba.

A ranar Talata firaministan Nijar da sojoji suka nada, Ali Mahaman Lamine Zeine, tare da wasu mambobin majalisar mulkin soja biyu suka ziyarci Chadi domin tattaunawa da shugaban kasar, Janar Mahamat Idriss Deby.

  • Kotu Ta Dakatar Da Sanata Ali Ndume Kan Yi Wa Wani Malami A Abuja Karan Tsaye
  • Manchester City Ta Lashe Kofin Super Cup Bayan Lallasa Sevilla

Zeine, wanda ya je a matsayin fuskar diflomasiyya ta gwamnatin soja – ya ce a yanzu kasarsa na karkashin gwamnatin mulkin soji, yana mai cewa a shirye suke da su bude kofar tattaunawa.

ADVERTISEMENT

Kazalika, sojojin mulkin sun tura wata tawaga zuwa Guinea ranar Asabar da ta gabata, duka dai da zimmar neman goyon baya.

Kafin haka, sabon ministan tsaron Nijar, Janar Salifou Mody, ya je Mali a ranar Juma’a cikin wata gajeriyar ziyara.

LABARAI MASU NASABA

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola

Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

Ƙasashen Mali da Burkina Faso da Gueinea mambobin ECOWAS ne – kungiyar da ke raya tattalin arzikin kasashen Afirka ta Yamma – amma ta dakatar da su sakamakon juyin mulkin da sojoji suka yi a kasashen.

Haka nan dukkansu sun ci alwashin goya wa Nijar baya idan dakarun ECOWAS ko na wata kasar waje suka kai wa sojojin hari.

A karshen makon da ya gabata gwamnatin sojin Mali ta sanar cewa za ta aika wa Nijar nau’in kayan abinci na hatsi kamar dawa masara da gero saboda takunkumin ECOWAS da ya hana sayar mata da kayayyaki.

Chadi ba ta cikin kungiyar ECOWAS, sannan kuma ba ta nuna adawa karara da juyin mulkin da sojojin Nijar suka yi ba, amma ta bayyana a fili cewa ba za ta goyi bayan yin amfani da karfi a kan makwabciyar tata ba.

Har yanzu ECOWAS na ci gaba da yunkurin difilomasiyya don sasanta rikicin siyasar, duk da barazanar amfani da karfin soja don taka wa sojojin karkashin Janar Abdourahmane Tchiani birki.

A ranar Alhamis da Juma’a hafsoshin tsaron kungiyar za su yi taro a birnin Accra na Ghana don ci gaba da tattaunawa bayan shugabannin Ecowas din sun ba su umarnin ɗaura damarar kutsawa Nijar a makon da ya gabata.

A gefe guda kuma, fitattun mutane da kungiyoyi a Nijeriya na ci gaba da nuna adawa da yin amfani da karfin yayin da Shugaba Bola Tinubu, a matsayinsa na shugaban ECOWAS, yake jagorantar yunkurin.

MASU ALAKA

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
Kasashen Ketare

Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola

May 30, 2026
Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya
Kasashen Ketare

Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

May 30, 2026
Iran Ta Zargi Amurka Da Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Da Ke Tsakaninsu
Kasashen Ketare

Iran Ta Zargi Amurka Da Karya Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Da Ke Tsakaninsu

May 30, 2026
Next Post
Emefiele Ya Maka DSS A Kotu Kan Tsare Shi

An Sake Gurfanar Da Emefiele A Kotu Kan Tuhume-Tuhume 20

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.