ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cibiyar Ba Da Agaji Ta Sarki Salman Na Saudiya Ta Fara Tiyatar Zuciya A Nijeriya

by yahuzajere
3 years ago
Saudiya

Cibiyar Ba da Agaji ta Sarki Salman na Saudiya ta kaddamar da aikin kiwon tiyatar cututtukan zuciya ga manya a Jihar Kano, inda tawagar likitocin sa kai guda 20 suka gudanar bisa hadin gwiwa da Kungiyar Kasashen Musulmi ta Duniya.

Tun daga lokacin da aka fara aikin, tawagar likitocin sa kai masu kishin kasa a cibiyar sun gudanar da gagarumin aikin tiyatar zuciya guda hudu da aka samu nasara a kai. A dukkan tiyatar da aka yi, likitocin sun nuna kwarewa da jin kai, lamarin da ya nuna kyakkyawan misali bisa dukufar da likitocin suka yi wajen warkar da marasa lafiya da kuma kara kwarin gwiwa ga mabukata.

Saudiya

ADVERTISEMENT

Aikin dai ya zo ne a cikin tsarin tallafin da Masarautar Saudiya ta bayar ta sashen bayar da agaji na jin kan al’umma, watau cibiyar agaji ta Sarki Salman don tallafa wa fannin kiwon lafiya a Nijeriya, da kuma kafa tsarin gudanar da aiki na sa kai a tsakanin al’ummar Saudiyya, bisa manufofin da masarautar ta sa gaba da ake son cimmawa nan da 2030.

Wannan hadin gwiwa ya zama shaida ga irin karfin da hadin kai yake da shi na samar da sauki a lokacin ibtila’i, inda kungiyoyi da hukumomin da ke da nisa da juna za su rika hada karfi don sauya rayuwar jama’a bila’adadin.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

A yayin da aka kaddamar da aikin kiwon lafiyar na sa kai a Jihar Kano, hakan ya nuna kyakykyawan tausayi da jin kan bil’adama lokacin ibtila’i. A duk tiyatar zuciyar da aka yi, an rubuta bayanan sauyin da aka gani, wanda ke nuna babban tasiri da alherin da masarautar ta Saudiyya take aiwatarwa a Nijeriya.

Saudiya
Wani likita tare da majinyacin da ya yi wa aiki

Idan dai za a iya tunawa, a watan Yuni ne masarautar Saudiyya ta kuduri aniyar samar da cibiyar tiyatar zuciya a Kano domin rage radadin rashin lafiyar da ke bukatar tiyatar bugun zuciya a kasar.

Khalid Ahmad Al-adamawi, karamin jakadan Saudiyya a Nijeriya, wanda ya ziyarci Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano, ya yi wa gwamnan bayani dangane da aikin tiyatar zuciyar da ake yi a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH).

A kwanakin baya ne dai Cibiyar Bayar da Agaji ta Sarki Salman ta kudiri aniyar samar da aikin jinya na sa-kai domin kula da masu cutar yoyon fitsari a jihar Kano. Inda daga ranar 6 zuwa 11 ga Agusta 2023, likitocin sa kai suka gudanar da aikin tiyata 65.

  • Sojojin Nijar Na Neman Goyon Bayan Kasashe Daban-Daban

Gidauniyar tana aiwatar da jerin shirye-shirye da tsare-tsare don samar wa marasa lafiya a duk fadin duniya da ingantaccen magani da sauran harkokin kiwon lafiyar da ba a samu a yankunan jama’ar da ake yi wa.

 

Saudiya
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Shin Gobarar Da Ta Tashi A Maui Za Ta Iya Tada ‘Yan Siyasar Amurka?

Shin Gobarar Da Ta Tashi A Maui Za Ta Iya Tada 'Yan Siyasar Amurka?

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.