ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Tuesday, July 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cibiyar Ba Da Agaji Ta Sarki Salman Na Saudiya Ta Fara Tiyatar Zuciya A Nijeriya

by yahuzajere
3 years ago
Saudiya

Cibiyar Ba da Agaji ta Sarki Salman na Saudiya ta kaddamar da aikin kiwon tiyatar cututtukan zuciya ga manya a Jihar Kano, inda tawagar likitocin sa kai guda 20 suka gudanar bisa hadin gwiwa da Kungiyar Kasashen Musulmi ta Duniya.

Tun daga lokacin da aka fara aikin, tawagar likitocin sa kai masu kishin kasa a cibiyar sun gudanar da gagarumin aikin tiyatar zuciya guda hudu da aka samu nasara a kai. A dukkan tiyatar da aka yi, likitocin sun nuna kwarewa da jin kai, lamarin da ya nuna kyakkyawan misali bisa dukufar da likitocin suka yi wajen warkar da marasa lafiya da kuma kara kwarin gwiwa ga mabukata.

Saudiya

ADVERTISEMENT

Aikin dai ya zo ne a cikin tsarin tallafin da Masarautar Saudiya ta bayar ta sashen bayar da agaji na jin kan al’umma, watau cibiyar agaji ta Sarki Salman don tallafa wa fannin kiwon lafiya a Nijeriya, da kuma kafa tsarin gudanar da aiki na sa kai a tsakanin al’ummar Saudiyya, bisa manufofin da masarautar ta sa gaba da ake son cimmawa nan da 2030.

Wannan hadin gwiwa ya zama shaida ga irin karfin da hadin kai yake da shi na samar da sauki a lokacin ibtila’i, inda kungiyoyi da hukumomin da ke da nisa da juna za su rika hada karfi don sauya rayuwar jama’a bila’adadin.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

A yayin da aka kaddamar da aikin kiwon lafiyar na sa kai a Jihar Kano, hakan ya nuna kyakykyawan tausayi da jin kan bil’adama lokacin ibtila’i. A duk tiyatar zuciyar da aka yi, an rubuta bayanan sauyin da aka gani, wanda ke nuna babban tasiri da alherin da masarautar ta Saudiyya take aiwatarwa a Nijeriya.

Saudiya
Wani likita tare da majinyacin da ya yi wa aiki

Idan dai za a iya tunawa, a watan Yuni ne masarautar Saudiyya ta kuduri aniyar samar da cibiyar tiyatar zuciya a Kano domin rage radadin rashin lafiyar da ke bukatar tiyatar bugun zuciya a kasar.

Khalid Ahmad Al-adamawi, karamin jakadan Saudiyya a Nijeriya, wanda ya ziyarci Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano, ya yi wa gwamnan bayani dangane da aikin tiyatar zuciyar da ake yi a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano (AKTH).

A kwanakin baya ne dai Cibiyar Bayar da Agaji ta Sarki Salman ta kudiri aniyar samar da aikin jinya na sa-kai domin kula da masu cutar yoyon fitsari a jihar Kano. Inda daga ranar 6 zuwa 11 ga Agusta 2023, likitocin sa kai suka gudanar da aikin tiyata 65.

  • Sojojin Nijar Na Neman Goyon Bayan Kasashe Daban-Daban

Gidauniyar tana aiwatar da jerin shirye-shirye da tsare-tsare don samar wa marasa lafiya a duk fadin duniya da ingantaccen magani da sauran harkokin kiwon lafiyar da ba a samu a yankunan jama’ar da ake yi wa.

 

Saudiya
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato
Manyan Labarai

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”
Manyan Labarai

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160
Manyan Labarai

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Next Post
Shin Gobarar Da Ta Tashi A Maui Za Ta Iya Tada ‘Yan Siyasar Amurka?

Shin Gobarar Da Ta Tashi A Maui Za Ta Iya Tada 'Yan Siyasar Amurka?

LABARAI MASU NASABA

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

ADC Ta Nemi A Binciki Nafiu Bala Bayan INEC Ta Ƙaryata Iƙirarinsa

July 14, 2026
Sojoji Sun Kashe ’Yan Ta’adda 3, Sun Ƙwato Makamai A Sakkwato

Sojoji Sun Daƙile Harin ISWAP A Borno

July 14, 2026
Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

Tsaka mai wuyar Infantino da Koma bayan mulkin yamma

July 14, 2026
“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

“Buhari Ya Taɓa tambaya Ta Mutane Nawa Na Kashe Saboda Yawan Azumin Dana Ke Yi”

July 14, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

Gwamnatin Tarayya Ta Ce Za A Gurfanar Da Tubabbun ’Yan ta’addan Da Suka Sake Aikata Manyan Laifuka

July 14, 2026
Tinubu Ya Gana da Gwamnan Kwara Bayan Harin Ta’addanci Da Ya Yi Ajalin Sama Da Mutane 160

Kyawawan Manufofin Buhari Za Su Ci Gaba Da Yi Wa ’Yan Nijeriya Tasiri – Tinubu

July 14, 2026
Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

Abin Da Ake Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin” Da Aka Yanke Wa Sin Na Kashin Kanta Ba Shi Da Wani Amfani

July 13, 2026
Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

Tafiye-tafiyen Fasinjojin Jirgin Kasa A Kasar Sin Sun Haura Biliyan 2.3 A Rabin Farko Na Bana

July 13, 2026
Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

Gwamnatin Tarayya Za Ta Ƙaddamar Da Tsarin Daƙile Rugujewar Gine-Gine

July 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.