ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CIIE Na Da Matukar Muhimmanci Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

by CGTN Hausa
2 years ago
CIIE

Tun lokacin da aka fara gudanar da baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin ko CIIE a takaice a shekarar 2018, kasashe masu halartar baje kolin na shekara-shekara sun yi amfani da tasirin girmar kasuwar kasar Sin, wanda ya kasance dandalin hada-hadar cinikayya na kasa da kasa, da inganta zuba jari, da mu’amalar jama’a da yin hadin gwiwa, da ba da gudummawa mai kyau wajen samar da sabbin tsarin ci gaba, da sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arzikin duniya.  

 

La’akari da tafiyar hawainiyar da tattalin arzikin duniya ke yi biyo bayan rashin cikakkiyar farfadowa daga tasirin annobar COVID 19, shugaba Xi Jinping a cikin wasikarsa na bikin bude baje kolin a jiya Lahadi ya ce, kasar Sin za ta kasance wata muhimmiyar dama ta ci gaban duniya a ko da yaushe, kuma za ta ci gaba da bude kofa ga kasashen waje, da kuma ci gaba da sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arzikin duniya, ta hanyar ci gaba da inganta baje kolin na kayayyaki da ake shigowa da su kasar daga kasashen waje.

ADVERTISEMENT
  • Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Yin Iyakar Kokarin Saukaka Rikicin Gaza
  • Xi Jinping Ya Taya Murnar Gudanar Da Babban Taron Birane Masu Sada Zumunta Na Sin Da Amurka

Baje kolin CIIE na bana ya jawo hankalin mahalarta daga kasashe, yankuna da kungiyoyin kasa da kasa 154. Sama da masu baje kolin 3,400 da kwararrun baki 394,000 suka yi rajista don halartar taron, wanda ke nuni da cikakkiyar karbuwar baje kolin.

Daga cikin kamfanoni 3,000 na duniya dake halartar baje kolin na wannan shekara, kusan kamfanoni 200 ne suka halarci baje kolin tun daga shekarar 2018 har ya zuwa yanzu, kuma kusan kamfanoni 400 ne ke dawowa baje kolin bayan duk shekaru biyu.

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

 

Yawancin kamfanonin kasashen waje da ke gudanar da kasuwanci a kasar Sin suna da kwarin gwiwa game da ci gaba da gudanar da kasuwancinsu a kasar, inda sama da kashi 90 cikin 100 na wadannan kamfanonin suna sa ran za su maido da jarinsu ko ribar da suke samu zai karu a cikin shekaru biyar masu zuwa ko kasa da haka, a cewar wani bincike na baya-bayan nan da Majalisar Bunkasa Harkokin Cinikayya ta Duniya ta gudanar a kasar Sin.

 

Binciken ya kuma nuna cewa, kamfanonin kasashen waje sun nuna kwarin gwiwar fadada hada-hadarsu na kasuwanci a kasar Sin, yayin da sama da kashi 70 cikin 100 na wadanda suka amsa tambayoyin binciken suka ce za su dawo da wasu sassan masana’antunsu kasar Sin.

 

Alkalumma a hukumance sun nuna cewa, hada-hadar kayayyakin da kasar Sin ke shigowa da su kasar na ci gaba da tafiya yadda ya kamata, inda yawan kayayyaki da take shigowa da su ya karu a kowane rubu’i na bana. Kasar Sin ta kasance kasa ta biyu a fannin shigo da kayayyaki a duniya tsawon shekaru 14 a jere.

“Baje kolin ya nuna cewa, kasar Sin a bude take don yin kasuwanci da sauran kasashen duniya. Wannan wata babbar dama ce ga kasashe daban-daban su yi baje kolin hajojinsu da fasahohinsu.”

 

Baya ga bayar da damammaki ga kasashe masu tasowa da kasuwanni masu tasowa, baje kolin CIIE ya kasance dandalin sada zumunta da kamfanonin kasar Sin ta hanyar yin hadin gwiwa da kamfanonin kasashen waje don samar da kayayyaki ko ayyuka ga kasuwannin kasar Sin ko na duniya baki daya. (Muhammed Yahaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku
Daga Birnin Sin

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Next Post
CIIE

Bikin CIIE Ya Sa Kayayyakin Kasashen Afirka Samun Karbuwa

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.