• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

CIIE Na Da Matukar Muhimmanci Ga Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
CIIE
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Tun lokacin da aka fara gudanar da baje kolin kayayyakin da ake shigowa da su kasar Sin ko CIIE a takaice a shekarar 2018, kasashe masu halartar baje kolin na shekara-shekara sun yi amfani da tasirin girmar kasuwar kasar Sin, wanda ya kasance dandalin hada-hadar cinikayya na kasa da kasa, da inganta zuba jari, da mu’amalar jama’a da yin hadin gwiwa, da ba da gudummawa mai kyau wajen samar da sabbin tsarin ci gaba, da sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arzikin duniya.  

 

La’akari da tafiyar hawainiyar da tattalin arzikin duniya ke yi biyo bayan rashin cikakkiyar farfadowa daga tasirin annobar COVID 19, shugaba Xi Jinping a cikin wasikarsa na bikin bude baje kolin a jiya Lahadi ya ce, kasar Sin za ta kasance wata muhimmiyar dama ta ci gaban duniya a ko da yaushe, kuma za ta ci gaba da bude kofa ga kasashen waje, da kuma ci gaba da sa kaimi ga bunkasuwar tattalin arzikin duniya, ta hanyar ci gaba da inganta baje kolin na kayayyaki da ake shigowa da su kasar daga kasashen waje.

  • Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Yin Iyakar Kokarin Saukaka Rikicin Gaza
  • Xi Jinping Ya Taya Murnar Gudanar Da Babban Taron Birane Masu Sada Zumunta Na Sin Da Amurka

Baje kolin CIIE na bana ya jawo hankalin mahalarta daga kasashe, yankuna da kungiyoyin kasa da kasa 154. Sama da masu baje kolin 3,400 da kwararrun baki 394,000 suka yi rajista don halartar taron, wanda ke nuni da cikakkiyar karbuwar baje kolin.

Daga cikin kamfanoni 3,000 na duniya dake halartar baje kolin na wannan shekara, kusan kamfanoni 200 ne suka halarci baje kolin tun daga shekarar 2018 har ya zuwa yanzu, kuma kusan kamfanoni 400 ne ke dawowa baje kolin bayan duk shekaru biyu.

Labarai Masu Nasaba

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

 

Yawancin kamfanonin kasashen waje da ke gudanar da kasuwanci a kasar Sin suna da kwarin gwiwa game da ci gaba da gudanar da kasuwancinsu a kasar, inda sama da kashi 90 cikin 100 na wadannan kamfanonin suna sa ran za su maido da jarinsu ko ribar da suke samu zai karu a cikin shekaru biyar masu zuwa ko kasa da haka, a cewar wani bincike na baya-bayan nan da Majalisar Bunkasa Harkokin Cinikayya ta Duniya ta gudanar a kasar Sin.

 

Binciken ya kuma nuna cewa, kamfanonin kasashen waje sun nuna kwarin gwiwar fadada hada-hadarsu na kasuwanci a kasar Sin, yayin da sama da kashi 70 cikin 100 na wadanda suka amsa tambayoyin binciken suka ce za su dawo da wasu sassan masana’antunsu kasar Sin.

 

Alkalumma a hukumance sun nuna cewa, hada-hadar kayayyakin da kasar Sin ke shigowa da su kasar na ci gaba da tafiya yadda ya kamata, inda yawan kayayyaki da take shigowa da su ya karu a kowane rubu’i na bana. Kasar Sin ta kasance kasa ta biyu a fannin shigo da kayayyaki a duniya tsawon shekaru 14 a jere.

“Baje kolin ya nuna cewa, kasar Sin a bude take don yin kasuwanci da sauran kasashen duniya. Wannan wata babbar dama ce ga kasashe daban-daban su yi baje kolin hajojinsu da fasahohinsu.”

 

Baya ga bayar da damammaki ga kasashe masu tasowa da kasuwanni masu tasowa, baje kolin CIIE ya kasance dandalin sada zumunta da kamfanonin kasar Sin ta hanyar yin hadin gwiwa da kamfanonin kasashen waje don samar da kayayyaki ko ayyuka ga kasuwannin kasar Sin ko na duniya baki daya. (Muhammed Yahaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CCTVCGTNCIIE
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Bikin CIIE Ya Inganta Ci Gaban Sin Da Sassan Kasa Da Kasa

Next Post

Bikin CIIE Ya Sa Kayayyakin Kasashen Afirka Samun Karbuwa

Related

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa
Daga Birnin Sin

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

12 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

13 hours ago
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

14 hours ago
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci
Daga Birnin Sin

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

15 hours ago
Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu
Daga Birnin Sin

Xi Da Takwaransa Na Bangladesh Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kulla Alakar Kasashensu

17 hours ago
Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo
Daga Birnin Sin

Fim Na Nezha 2 Na Kasar Sin Ya Kara Samun Lambar Yabo

1 day ago
Next Post
CIIE

Bikin CIIE Ya Sa Kayayyakin Kasashen Afirka Samun Karbuwa

LABARAI MASU NASABA

Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Al’ummar Sokoto Sun Koka Kan Yadda Hare-haren Lakurawa Ke Kara Ta’azzara

October 5, 2025
Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.