• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cikin Watanni 29 Mun Kama ‘Yan Kwaya 31,675 Da Kwace Miliyoyin Muggan Kwayoyi – Buba Marwa

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
marwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban hukumar hana sha da fataucin muggan kwayoyi (NDLEA), Buba Marwa ya tabatar da cewa tsauraren matakan da suke dauka kan yaki da ta’ammuli da muggan kwayoyi ya haifar da mai ido, domin a cikin watani 29 kacal hukumar ta damke masu ta’ammuli da muyagun kwayoyi su 31,675.

Hukumar ta NDLEA ta kara da cewa cikin 31,675 da aka kama, 5,147 an tabbatar da laifinsu kuma an yanke masu hukunci, yayin da hukumar ta kwace muggan kwayoyi da suke da nauyin miliyan 6.3 a tsawon wannan lokaci.
Ya kara da cewa wannan kokarin yana cikin hobbasan da hukumar ke yi don hana jama’a ta’ammuli miyagun kwayoyi wanda a yanzu ya zama ruwan dare a tsakanin al’umma kuma yana barzana ga ci gaban tattalin arziki da su kansu masu amfani da kwayoyin da kuma iyalansu.

  • Kotu Ta Daure Insifektan ‘Yansanda Kan Dirka Wa Diyarsa Ciki Da Kashe Jaririn

Sakataren hukumar NDLEA, Mista Shadrach Haruna wanda shi ne ya wakilcin shugaban hukumar ya bayyana hakan a Abuja ranar Litinin a lokacin taron manema labarai na hadin gwiwa gami da karin haske ga wakilin ofishin Majalisar Dinkin Duniya da yaki da shan miyagun kwayoyi karkashin jagorancin, Mista Oliber Stolpe, don shirin aikace-aikace game da ranar yaki da miyagun kwayoyi ta Duniya ta shekarar 2023.

A cewasa, “Babban taken bikin wannan shekarar shi ne, ‘mutane su daina nuna wariya ga masu ta’ammuli da muyagun kwayoyi tare da ba su kariya game da wannan yanayi da ake ciki a nan Nijeriya”.

“A cikin shekara 2 da rabi da suka gabata, mun yi kokari wajen tsaurara matakanmu wanda ya rage safarar miyagun kwayoyi a cikin al’umma. A cikin watanni 29 mun kama masu ta’ammuli da miyagun kwayoyi 31,675 da suka hada da manyan dilolin kwaya 35 tare da samun nasarar yanke wa 5,147 hukunci da kuma sama da mutum 11 da a yanzu haka ake ci gaba da gudanar da shari’arsu a kotu, a yayin da masu ta’ammuli da miyagun kwayoyi 23,725 aka shiryar da su tare da gyara dabi’unsu wanda mafi yawansu sun shiga cikin sana’o’i a cibiyoyinmu da muka kafa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

“Akalla kilogiram miliyan 6.3 na muggan kwayoyin muka kwace, a cikin kokarinmu na hana safara da rarraba wadannan miyagun kwayoyin. Mun samu nasarar lalata gonakin tabar wiwi mai fadin hekta 852.142 da lalata manyan dakunan harhada magunguna da suke sanya maye guda 3. Zan iya tabbatar maku da cewa ko a yanzu da muke magana, jami’an hukumar NDLEA suna can suna aiki ba dare ba rana don ganin an kawo karshen ta’ammuli da miyagun kwayoyi”.

Ya kuma tabbatar da cewa a yanzu safarar miyagun kwayoyi ya ragu matuka, wanda an sami nasarar haka ne sakamakon namijin kokarin da hukumar take yi tare da wayar da kan masu ta’ammuli da miyagun kwayoyin don ganin sun bari kwata-kwata a harshe daban-daban a kafafen sadarwa a Nijeriya.

A nasa jawabin, Mista Stolpe ya kara jaddada alfanun hadin kai tsakanin kasa da kasa a ayyukan kawar da aikata ta’ammuli da muggan kwayoyi, musamman wajen kawar da duk hanyoyin yada wadannan muggan ayyuka.

“Yana da kyau al’umma da hukumomin kula da lafiya a matakin farko su yi dukkan mai yiwuwa wajen samar da bayanai na wayar da kai game da ta’ammuli da miyagun kwayoyi da nuna masu yadda illar da shan muggan kwayoyi ke yi wa mutane.

Mista Stolpe ya yaba wa ayyukan hukumar NDLEA wajen yaki da ta’ammuli da miyagun kwayoyi da kuma safarar kwayoyin a Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sauye-sauye Da Garambawul A Gwamnatin Tinubu…

Next Post

Da Ikon Allah Babu Bacci Ko Daga Kafa Sai Na Shawo Kan Matsalar Tsaro – Gwamnan Zamfara

Related

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

2 hours ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

3 hours ago
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara
Labarai

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

6 hours ago
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

7 hours ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

17 hours ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

19 hours ago
Next Post
Gwamnan Zamfara

Da Ikon Allah Babu Bacci Ko Daga Kafa Sai Na Shawo Kan Matsalar Tsaro – Gwamnan Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

Super Falcons Za Su Samu Kyakkyawar Tarɓa Daga Gare Ni A Abuja — Tinubu

July 27, 2025
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

July 27, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

July 27, 2025
Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

Ƴansanda Sun Kama Masu Garkuwa Da Mutane 6 A Kaduna Da Zamfara

July 27, 2025
aure

Ko Kin San… Matsalolin Mahaifa Da Suke Hana Haihuwa 

July 27, 2025
VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.