• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cikin Watanni 29 Mun Kama ‘Yan Kwaya 31,675 Da Kwace Miliyoyin Muggan Kwayoyi – Buba Marwa

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Labarai
0
marwa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban hukumar hana sha da fataucin muggan kwayoyi (NDLEA), Buba Marwa ya tabatar da cewa tsauraren matakan da suke dauka kan yaki da ta’ammuli da muggan kwayoyi ya haifar da mai ido, domin a cikin watani 29 kacal hukumar ta damke masu ta’ammuli da muyagun kwayoyi su 31,675.

Hukumar ta NDLEA ta kara da cewa cikin 31,675 da aka kama, 5,147 an tabbatar da laifinsu kuma an yanke masu hukunci, yayin da hukumar ta kwace muggan kwayoyi da suke da nauyin miliyan 6.3 a tsawon wannan lokaci.
Ya kara da cewa wannan kokarin yana cikin hobbasan da hukumar ke yi don hana jama’a ta’ammuli miyagun kwayoyi wanda a yanzu ya zama ruwan dare a tsakanin al’umma kuma yana barzana ga ci gaban tattalin arziki da su kansu masu amfani da kwayoyin da kuma iyalansu.

  • Kotu Ta Daure Insifektan ‘Yansanda Kan Dirka Wa Diyarsa Ciki Da Kashe Jaririn

Sakataren hukumar NDLEA, Mista Shadrach Haruna wanda shi ne ya wakilcin shugaban hukumar ya bayyana hakan a Abuja ranar Litinin a lokacin taron manema labarai na hadin gwiwa gami da karin haske ga wakilin ofishin Majalisar Dinkin Duniya da yaki da shan miyagun kwayoyi karkashin jagorancin, Mista Oliber Stolpe, don shirin aikace-aikace game da ranar yaki da miyagun kwayoyi ta Duniya ta shekarar 2023.

A cewasa, “Babban taken bikin wannan shekarar shi ne, ‘mutane su daina nuna wariya ga masu ta’ammuli da muyagun kwayoyi tare da ba su kariya game da wannan yanayi da ake ciki a nan Nijeriya”.

“A cikin shekara 2 da rabi da suka gabata, mun yi kokari wajen tsaurara matakanmu wanda ya rage safarar miyagun kwayoyi a cikin al’umma. A cikin watanni 29 mun kama masu ta’ammuli da miyagun kwayoyi 31,675 da suka hada da manyan dilolin kwaya 35 tare da samun nasarar yanke wa 5,147 hukunci da kuma sama da mutum 11 da a yanzu haka ake ci gaba da gudanar da shari’arsu a kotu, a yayin da masu ta’ammuli da miyagun kwayoyi 23,725 aka shiryar da su tare da gyara dabi’unsu wanda mafi yawansu sun shiga cikin sana’o’i a cibiyoyinmu da muka kafa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

“Akalla kilogiram miliyan 6.3 na muggan kwayoyin muka kwace, a cikin kokarinmu na hana safara da rarraba wadannan miyagun kwayoyin. Mun samu nasarar lalata gonakin tabar wiwi mai fadin hekta 852.142 da lalata manyan dakunan harhada magunguna da suke sanya maye guda 3. Zan iya tabbatar maku da cewa ko a yanzu da muke magana, jami’an hukumar NDLEA suna can suna aiki ba dare ba rana don ganin an kawo karshen ta’ammuli da miyagun kwayoyi”.

Ya kuma tabbatar da cewa a yanzu safarar miyagun kwayoyi ya ragu matuka, wanda an sami nasarar haka ne sakamakon namijin kokarin da hukumar take yi tare da wayar da kan masu ta’ammuli da miyagun kwayoyin don ganin sun bari kwata-kwata a harshe daban-daban a kafafen sadarwa a Nijeriya.

A nasa jawabin, Mista Stolpe ya kara jaddada alfanun hadin kai tsakanin kasa da kasa a ayyukan kawar da aikata ta’ammuli da muggan kwayoyi, musamman wajen kawar da duk hanyoyin yada wadannan muggan ayyuka.

“Yana da kyau al’umma da hukumomin kula da lafiya a matakin farko su yi dukkan mai yiwuwa wajen samar da bayanai na wayar da kai game da ta’ammuli da miyagun kwayoyi da nuna masu yadda illar da shan muggan kwayoyi ke yi wa mutane.

Mista Stolpe ya yaba wa ayyukan hukumar NDLEA wajen yaki da ta’ammuli da miyagun kwayoyi da kuma safarar kwayoyin a Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Sauye-sauye Da Garambawul A Gwamnatin Tinubu…

Next Post

Da Ikon Allah Babu Bacci Ko Daga Kafa Sai Na Shawo Kan Matsalar Tsaro – Gwamnan Zamfara

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

15 minutes ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

1 hour ago
Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu
Manyan Labarai

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

4 hours ago
An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya
Labarai

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

9 hours ago
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

20 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

21 hours ago
Next Post
Gwamnan Zamfara

Da Ikon Allah Babu Bacci Ko Daga Kafa Sai Na Shawo Kan Matsalar Tsaro – Gwamnan Zamfara

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Wa Fursunoni 59,786 Rijistar NIN A Faɗin Nijeriya

June 8, 2025
Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

Sin Ta Amince Da Bukatar Fitar Da Wasu Nau’o’in Ma’adinai Na “Rare Earth” 

June 8, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

Gwamnatin Tarayya Ta Ayyana Alhamis, 12 Ga Yuni A Matsayin Ranar Hutu

June 8, 2025
Wakilin Sin Ya Bayyana Rashin Gamsuwa Da Yadda Amurka Ta Gabatar Da Daftarin Kudurin Kwamitin Sulhu Kan Sudan Ta Kudu

Bangarorin Sudan Da Ke Dauki Ba Dadi Sun Zargi Juna Da Kai Hari Kan Jerin Gwanon Motocin MDD

June 8, 2025
Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

Rashin Abinci Na A Waka Ya Sa Na Daina Yi -T Y Shaba

June 8, 2025
Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

Bambancin Bukukuwan Sallar Bara Da Ta Bana

June 8, 2025
Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

Amfanin Ganyen Mangwaro Ga Masu Ciki

June 8, 2025
Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

June 8, 2025
An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

An Daure ‘Yan Nijeriya Uku Shekaru 15 A Bisa Laifin Zamba A Indiya

June 8, 2025
Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.