ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Ikon Allah Babu Bacci Ko Daga Kafa Sai Na Shawo Kan Matsalar Tsaro – Gwamnan Zamfara

•Abubuwan Da Na Tarar Sun Wuce Tunanina

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
Gwamnan Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara DAUDA LAWAL ya ayyana cewa ba zai yi bacci ko daga kafa ba da ikon Allah sai ya shawo kan matsalar tsaro a Zamfara. Gwamnan ya sha wannan alwashi ne yayin hirarsa da Sashen Hausa na BBC a wannan makon, in ya yi bayanai masu muhimmanci da suka hada da tarin matsalolin da ya tarar da su a jihar da suka shafi ilimi, Ruwan sha da kuma rashin biyan albashin ma’aikatan jihar. Ga dai yadda hirar ta kasance kamar yadda RABI’U ALI INDABAWA ya rubuto mana:

Daga lokacin da Allah ya baka kujerar Gwamnan Zamfara ya ka samu kanka a matsayin gwamna?
Alhamdu lillahi, mun amshi wannan mulki, kuma kamar yadda nake zato abubuwan da muka samu sun ma fi tunanina, tun da muka amshi mulkin nan mun samu asusun Zamfara babu kudi, kusan asusu daya na gani watakil in ce kamar akwai miliyan uku ko miliyan hudu.

…Na Naira ko na Dala?
Na Naira, yau jihar nan wata uku ba a biya albashi ba kuma har yanzu a kai ake. Sannan yau idan ka duba duk ma’aikatun da ke Jihar Zamfara an yanke musu wuta ana bin su bashi, bashi na miliyoyi dari-dari. Yau idan ka duba duk wata ma’aikata tun daga ma’aikatar shari’a ko jami’an tsaro yau ba biya kudadensu na yau da kullum na tafiyar da harkokinsu ba fiye da wata uku. Da na tattauna da alkalai sun gaya min cewa wata uku ko kwabo ba a basu ba, saboda haka yanzu ma ba a iya zama a yi shari’a don ko takardar da za su yi rubutu yanzu ba su da ita. Jami’an tsaro na zauna da su yau wata uku ‘yankudaden da ake ba su na yau da kullum da za su shiga nan su shiga can babu su. kai motocin ma da suke amfani da su yanzu wallahi ba su da tayoyi ballantana a ce maka kudin mai da makamantansu. Yau ‘yan makaranta daliban Zamfara Saifuros jiya an yi min waya cewa an kore su, daliban Zamfara, a Indiya, an yi min waya an kore su. yau da muke maganar nan wani dalibi na Jihar Zamfara bai rubuta NECO ba bai rubuta WAEC ba saboda ana bin gwamnati fiye da Naira biliyan 1.6. yau idan ka je gidanmu na Kaduna na gwamnati kotu ta kulle shi ana bin mu kudi. Jiya-jiyan nan a Abuja gidajenmu na gwamnati kotu ta zo ta sa a kulle su ana bin mu kudi.

ADVERTISEMENT

Kafin ka samu wannan nasara ta zama gwamna ka taba tunanin wannan matsalar
Na yi tunanin wadansu daga cikinsu kamar yadda na ce, amma da na zo sai na ga cewa abin ma ya wuce misali.

Ka yi maganar an bar kusan miliyan uku zuwa hudu, amma gwamnatin APC da ta tafi ta fito tana cewa ta bar kudi kusan biliyan ashirin a asusun gwamnatin Zamfara har da wasu daloli kusan miliyan uku haka.
Na ji wannan, sannan na ce don Allah don Annabi ina so a zo a nuna mana shi a wane asusu ne aka ajiye wannan kudi. Kuma sun san cewa suna da wannan kudin a she keta ta hana a biya ma’aikata kudadensu, keta ce ta hana a ba da kudaden da za a sayo sinadaren da za a kai hukumar samar da ruwa, keta ta hana a biya ‘yan makaranta kudadensu, keta ce ta hana a biya jami’an tsaro kudadensu, keta ce ta hana duk wadannan koyu da muke fama da su da makamantansu, don Allah ina roko a nuna min wane asusu ne kuma a nuna wa duniya bayanan cewa ga biliyan ashirin da gwamnati ta bari.

LABARAI MASU NASABA

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

Yanzu me ka fara da shi?
Na farko maganar ruwa, kusan wata hudu ke nan babu ruwa a cikin garin Gusau, to Alhamdu lillahi wannan sati na zagaya na je gida na ga irin matsalolin da suke fama da su, na farko da ba su da wuta saboda an yanke wutarsu fiye da wata hudu, na biyu babu ‘yan sinadaran da ake sawa wanda da shi a ke tura ruwa al’umma su yi amfani da shi, sai da na je ciwo bashi aka sayo wadannan sinadarai aka zo sa. Sannan da ikon Allah kuma na samu wasu bayin Allah Indiyoyi da suka zo wasu na’urori wanda na roke su suka bamu kyauta. Na’urorin nan in za a saye su za a kashe miliyan 200.

Kana maganar ba kudi gashi har ka ciyo bashi ka fara tunkarar matsalar ruwa, mutanen nan na Zamfara ma’aikata ga su kusan watansu uku ko hudu ba albashi, kana ganin bai da muhimmanci a samu su rage zafi musamman a wannan lokacin na janye tallafin mai?
Abin da zan iya tabbatar wa ma’aikatan Jihar Zamfara da ikon Allah za mu yi kokari mu biya albashin su kafin Sallah, duk yanda zan yi duk hanyar da zan bi in biya albashi in Allah ya yard azan biya su.

Na wata nawa?
To na farko zan ga nawa ne bashin da za a iya bani, idan zan iya biya fiye da wata daya zan biya in kuma ba zan iya ba, zan biya wanda na san wannan hakkina ne a wannan wata in basu kafin in ga wace hanya ce zan bi in samo wasu kudaden don in tabbatar da cewa wannan bashi da suke bin gwamnati na dauke shi daga kan gwamnati.

Yanzu baru mu je kan tsaro, bayan hawanka kusan kila ka shaida ganin kalubalen da ke gabanka, musamman an kai hare-hare a Maradun, an kai a yankin Maru, an kai kuma Jangebe har kashe wani likita, a Bakura ma an yi.
Kwarai da gaske

To yanzu ya ka ji kuma me za ka yi a kai?
Abu ne mara dadi, duk wani shugaba ba wanda zai so ya je cewa yau an zo an kashe wani mutumin jiharsa, na ji zafin wannan abu kuma na jajanta wa wannan al’umma, muna nan muna bakin kokarinmu na tabbatar da cewa an kawo tsaro a Jihar Zamfara. Na farko cikin satin nan da ni da sauran gwamnonin Arewa da Yamma mun zauna da shugaban kasa kuma mun gaya masa irin matsalolin da muke fuskanta ta wajen tsaro, wanda ya tabbatar mana da cewa yana sane da wadannan matsaloli kuma shima yana bakin kokari ya ga cewa an shawo kan wannan matsala. Bayan mun gama wannan tattaunawa, na je na zauna da shi shugaban sojojin na Nijeriya baki daya wato ‘Chief Of Army Staff’ kenan na kara tabbatar masa da irin matsalolin da muke fuskanta na rashin tsaro ya bani tabbacin cewa a shirye suke su taimaka wajen kawo tsaro a Zamfara.

To batun hanyoyi da ka yi magana akwai wasu hanyoyi, akwai batun sulhu ciki?
Wato abubuwan suna da yawa, abu nd sa za a tattauna a gani kan cewa shin maganar sulhu ta yaya za a yi in ma sulhun za a yi, ba zan iya gaya maka sauran abubuwan ba saboda abu ne na maganar tsaro amma dai in mun cimma iyaka na san su da kansu jami’an tsaron za su fito su yi wa al’umma bayani kan irin matakan da aka dauka.

Wane alkawari za ka yi ma ‘yan Zamfaran nan kan tsaron nan kila a cikin kwanakinka dari?
Abin da zan iya cewa maganar tsaro ita ce kan gaba a wannan mulki nawa, ba zan yi bacci b aba kuma zan daga kafa ba sai na tabbatar da cewa da ikon Allah mun ciyo kan matsalara tsaro.

To mu je batun ilimi ka ce yara ba su rubuta jarrabawa ba kuma an gaya maka a Saifuros an kori daliban Zamfara, batun ilimin nan kusan zamfara ita ce baya, me ka shirya yi a gaggauce wanda kila zai iya tunkarar wannan batu.?
Na farko abin gaggawa shi ne zan zauna da ‘yan NECO da ‘yan WAEC don mu shiga cikin wata yarjejeniya yadda zan iya biyan wadannan kudade da suke bin gwamnati, wanda idan mun biya dalibanmu za su iya komawa makaranta in lokacin jarrabawa ya yi kuma za su iya zauna wa wannan jarrabawa yadda za su amshi takardar shaidarsu.

Gwamnan Zamfara
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    NSCDC Ta Cafke Mutum 10 Da Ake Zargi Da Satar Kayan Gwamnati Da Kuma Fashi A Kano
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƴansanda Su Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 500 Daga Hannun Dillalin Miyagun Ƙwayoyi
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙasashen DR Congo Uganda Da Sudan Sun Haɗa Kai Domin Yaƙar Ibola
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Zafin Rana Ya Yi Ajalin Mutum 16 A Indiya

MASU ALAKA

Gwamnan Zamfara
Rahotonni

Ko Yakin Iran Zai Kawo Karshen Kawancen Amurka Da Kasashen Larabawa?

May 17, 2026
Gwamnan Zamfara
Rahotonni

Yadda Sauya Shekar ‘Yan Siyasa Ta Sauya Fasalin Majalisar Dokokin Kasa

May 16, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Rahotonni

Almajiranci:Matsala Ko Maslaha

May 10, 2026
Next Post
Tsayuwar Arfa

Hukuncin Talbiyya Da Falalar Tsayuwar Arfa

LABARAI MASU NASABA

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.