ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cikin Watanni 29 Mun Kama ‘Yan Kwaya 31,675 Da Kwace Miliyoyin Muggan Kwayoyi – Buba Marwa

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
marwa

Shugaban hukumar hana sha da fataucin muggan kwayoyi (NDLEA), Buba Marwa ya tabatar da cewa tsauraren matakan da suke dauka kan yaki da ta’ammuli da muggan kwayoyi ya haifar da mai ido, domin a cikin watani 29 kacal hukumar ta damke masu ta’ammuli da muyagun kwayoyi su 31,675.

Hukumar ta NDLEA ta kara da cewa cikin 31,675 da aka kama, 5,147 an tabbatar da laifinsu kuma an yanke masu hukunci, yayin da hukumar ta kwace muggan kwayoyi da suke da nauyin miliyan 6.3 a tsawon wannan lokaci.
Ya kara da cewa wannan kokarin yana cikin hobbasan da hukumar ke yi don hana jama’a ta’ammuli miyagun kwayoyi wanda a yanzu ya zama ruwan dare a tsakanin al’umma kuma yana barzana ga ci gaban tattalin arziki da su kansu masu amfani da kwayoyin da kuma iyalansu.

  • Kotu Ta Daure Insifektan ‘Yansanda Kan Dirka Wa Diyarsa Ciki Da Kashe Jaririn

Sakataren hukumar NDLEA, Mista Shadrach Haruna wanda shi ne ya wakilcin shugaban hukumar ya bayyana hakan a Abuja ranar Litinin a lokacin taron manema labarai na hadin gwiwa gami da karin haske ga wakilin ofishin Majalisar Dinkin Duniya da yaki da shan miyagun kwayoyi karkashin jagorancin, Mista Oliber Stolpe, don shirin aikace-aikace game da ranar yaki da miyagun kwayoyi ta Duniya ta shekarar 2023.

ADVERTISEMENT

A cewasa, “Babban taken bikin wannan shekarar shi ne, ‘mutane su daina nuna wariya ga masu ta’ammuli da muyagun kwayoyi tare da ba su kariya game da wannan yanayi da ake ciki a nan Nijeriya”.

“A cikin shekara 2 da rabi da suka gabata, mun yi kokari wajen tsaurara matakanmu wanda ya rage safarar miyagun kwayoyi a cikin al’umma. A cikin watanni 29 mun kama masu ta’ammuli da miyagun kwayoyi 31,675 da suka hada da manyan dilolin kwaya 35 tare da samun nasarar yanke wa 5,147 hukunci da kuma sama da mutum 11 da a yanzu haka ake ci gaba da gudanar da shari’arsu a kotu, a yayin da masu ta’ammuli da miyagun kwayoyi 23,725 aka shiryar da su tare da gyara dabi’unsu wanda mafi yawansu sun shiga cikin sana’o’i a cibiyoyinmu da muka kafa.

LABARAI MASU NASABA

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

“Akalla kilogiram miliyan 6.3 na muggan kwayoyin muka kwace, a cikin kokarinmu na hana safara da rarraba wadannan miyagun kwayoyin. Mun samu nasarar lalata gonakin tabar wiwi mai fadin hekta 852.142 da lalata manyan dakunan harhada magunguna da suke sanya maye guda 3. Zan iya tabbatar maku da cewa ko a yanzu da muke magana, jami’an hukumar NDLEA suna can suna aiki ba dare ba rana don ganin an kawo karshen ta’ammuli da miyagun kwayoyi”.

Ya kuma tabbatar da cewa a yanzu safarar miyagun kwayoyi ya ragu matuka, wanda an sami nasarar haka ne sakamakon namijin kokarin da hukumar take yi tare da wayar da kan masu ta’ammuli da miyagun kwayoyin don ganin sun bari kwata-kwata a harshe daban-daban a kafafen sadarwa a Nijeriya.

A nasa jawabin, Mista Stolpe ya kara jaddada alfanun hadin kai tsakanin kasa da kasa a ayyukan kawar da aikata ta’ammuli da muggan kwayoyi, musamman wajen kawar da duk hanyoyin yada wadannan muggan ayyuka.

“Yana da kyau al’umma da hukumomin kula da lafiya a matakin farko su yi dukkan mai yiwuwa wajen samar da bayanai na wayar da kai game da ta’ammuli da miyagun kwayoyi da nuna masu yadda illar da shan muggan kwayoyi ke yi wa mutane.

Mista Stolpe ya yaba wa ayyukan hukumar NDLEA wajen yaki da ta’ammuli da miyagun kwayoyi da kuma safarar kwayoyin a Nijeriya.

marwa
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: APC Na Fuskantar Matsin Lamba Kan Sake Fasalin Tawagar Yakin Neman Zabe
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin APC Da ‘Yan Adawa Kan Tallafin Gwamnatin Tarayya Ga Magidanta
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    INEC Ta Zayyano Kalubalen Da Ke Iya Shafar Sahihancin Zaben 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027:Kamun Ludayin Yakin Neman Zaben Manyan ‘Yan Takarar Shugaban Kasa

MASU ALAKA

marwa
Labarai

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato
Manyan Labarai

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu
Rahotonni

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Next Post
Gwamnan Zamfara

Da Ikon Allah Babu Bacci Ko Daga Kafa Sai Na Shawo Kan Matsalar Tsaro – Gwamnan Zamfara

LABARAI MASU NASABA

marwa

Uganda Za Ta Fara Fitar Da Man Fetur Zuwa Ƙasashen Waje

September 10, 2026
Cutar Mashaƙo Ta Ɓarke A Kano, Katsina Da Filato

Mashaƙo: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Sun Kai 27 A Filato

September 10, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

Wane Ne Dan Shagamu: Su Wane Ne Suka Kashe Shi A Kano?

September 10, 2026
Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

Al’umma Sun Yaba Wa Sojoji Kan Yaƙar ’Yan Bindiga A Zamfara

September 10, 2026
Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

Ambaliyar Ruwa Ta Tafi Da Ɗalibai 2 A Abuja Da Abia

September 10, 2026
’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.