ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cire Tallafin Fetur: Kano Za Ta Biya Ma’aikata Karin Albashin N20,000, ‘Yan Fansho N15,000.

by Sulaiman
2 years ago
Kano

Gwamnatin jihar Kano ta rattaba hannu da kungiyar kwadago ta Nijeriya (NLC da TUC) kan yarjejeniyar fara bayar da tallafin Naira 20,000 ga daukacin ma’aikatan jihar.

An amimce da kudirin ne da nufin rage kalubalen matsin tattalin arziki da ma’aikatan gwamnati ke fuskanta a jihar Kano bayan cire tallafin man fetur da gwamnatin tarayya ta yi.

  • Jerin Jami’o’i 18 Da NUC Ta Haramta Karatu Acikinsu
  • Hukumar Kashe Gobara Ta Kano Ta Ceto Rayuka 417 Da Dukiyoyin Nairori A Shekarar 2023

Shugaban kungiyar TUC reshen Kano, Kwamared Mubarak Buba Yarima ne ya tabbatar wa LEADERSHIP wannan rahoton, inda ya jaddada muhimmiyar rawar da kungiyoyin kwadago ke takawa wajen tattaunawa da gwamnati.

ADVERTISEMENT

Yarjejeniyar ta samu nasara ne biyo bayan rokon haɗin gwiwa da NLC da TUC suka gabatar wa gwamnatin jihar Kano a watan Oktoban 2023, inda suka nemi gwamnatin da tallafawa ma’aikata kan mawuyacin halin da suke ciki.

Gwamna Yusuf, nan take ya kafa kwamiti na musamman domin nemo mafita kan kudurin. Sakamakon binciken da kwamitin ya gabatar, an cimma matsaya kan cewa za a fara biyan tallafin Naira N20,000 daga watan Disambar 2023 ga daukacin ma’aikatan gwamnati a matakin jihohi da kananan hukumomi.

LABARAI MASU NASABA

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Yarima ya kara da cewa, za a ci gaba da bayar da tallafin kudi har sai an gudanar da cikakken nazari kan mafi karancin albashi a cikin watanni shida masu zuwa.

Bugu da kari, masu karbar fansho za su rika karbar N15,000 duk wata na tsawon watanni uku, tare da biyan bashin alawus din Disamba 2023 da ba a biya ba.

Yarima ya bayyana jin dadinsa ga gwamnatin jihar Kano, musamman ma mai baiwa gwamna shawara kan harkokin kwadago, Kwamared Baffa Sani Gaya, da sauran mambobin kwamitin bisa wannan gagarumin bincike da suka mika wa gwamnatin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi
Hotuna

HOTUNA: Yadda Tinubu Ya Kai Ziyara Don Ta’aziyyar Sheikh Dahiru Bauchi

December 20, 2025
Next Post
Nasarawa

Shugaban Karamar Hukumar Nasarawa Ya Shaki Iskar 'Yanci Bayan Biyan Kudin Fansa Miliyan N10

LABARAI MASU NASABA

‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

Kotu Ta Fara Sauraren Korafe-korafen Dalibai A Kan Jami’ar MAAUN

December 21, 2025
Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

Tinubu Ya Sauya Sunan Jami’ar Azare Don Karrama Sheikh Dahiru Usman Bauchi

December 20, 2025
Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

Wajibi Ne Tawagar MONUSCO Ta Wanzar Da Cin Gashin Kai In Ji Wakilin Kasar Sin

December 20, 2025
Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

Matasa Miliyan 80 Ne Ba Su Da Aikin Yi A Nijeriya

December 20, 2025
An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

An Nuna Jigo Da Tambarin Shagalin Murnar Bikin Bazara Na Shekarar 2026 A Moscow

December 20, 2025
Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

Auren Da Ya Fi Auren Gidan Daula Dadi Ga Mace

December 20, 2025
An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

An Fara Aiki Da Na’urar Fasahar Samar Da Lantarki Daga Iskar CO₂ Da Aka Sarrafa A Lardin Guizhou Na Kasar Sin

December 20, 2025
Shugaban Somaliya: Kara Fadada Bude Kofa Ga Kasashen Waje Da Sin Ke Yi Zai Inganta Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka

Shugaban Somaliya: Kara Fadada Bude Kofa Ga Kasashen Waje Da Sin Ke Yi Zai Inganta Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Afirka

December 20, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.