• English
  • Business News
Saturday, June 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke

by Ra'ayinmu
3 weeks ago
in Kiwon Lafiya
0
Cutar Hawan Jini Na Ci Gaba Da Yi Wa ‘Yan Nijeriya Kisan Mummuke
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Nijeriya a kwanan baya tabi sahun sauran kasashen duniya, don tanawa da zagoyowar ranar masu fama da larurar hawan Jini da aka gudanar ta shekarar 2025.

A yayin taron, an tattuna kan wannan larurar mai yiwa wadanda suka kamu da ita, kisan mummuke.

Taken taron na bana shi ne, “Zuwa yin gwajin Jini yadda ya kamata, domin yin tsawo rayuwa”.

Tun dai a shekarar 2021, ake ci gaba da mai-maita wannan taken taron, wanda kuma ya mayar a hankali, kan mahimmancin zuwa yin gwajin Jini, yadda ya kamata.

Mahimmamcin taron na duniya shi ne, domin a wayar da kan alumma kan sanin kiwon lafiyarsu da kuma mayar da hankali, wajen ilimantar da su, game da hadarin da ciwon tare da kuma sanin irin abincin da ya kamata ya rinka ci.

Labarai Masu Nasaba

Me Ya Kamata Mai Yaron Ciki Ta Kula Da Shi?

Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su

  • Sulhu da ‘Yan Bindiga Ya Fi Zubar Da Jinin Ɗan Adam A Kaduna – Uba Sani
  • Gazawar Gwamnatin Tinubu Ce Ke Haddasa Zubar Da Jini A Filato – Ƙungiyar Dattawan Arewa

Kazalika, wasu kwararrun, sun ayyna larurar, a matsayin cieon da ke yiawa mutane, kisan mummuke, musamman duba da cewa, bata nuna wasu alamu, idan an kamu da ita, sai dai kawai, ta ci gaba da zama barzana ga lafiyar ‘yan Adam, kamar kamuwa da masu larorin da suka hada da; mutuwar barin Jiki, lalata Koda da kuma rashin iya gani.

An kiyasta cewa, a daukacin fadin duniya, sama da mutane, biliyan 1.3 ke fama da ciwon, wanda kuma rabin adadin wannan alkaluman ne kacal, aka yi masu gwaji aka kuma duba lafiyarsu, yadda ya kamata.

Ciwaon na karuwa, musamman saboda yawan shekarun wadanda suka manyanta kuma larurar, ta karade daukacin fannin tattalin arziki da shafar kudin shiga.

Wani rahoton wani bincike na kiwon lafiya na duniya, ya nuna cewa, za a iya samu karuwar ciwon daga kaso 15 zuwa 20, inda wannan adadin, zai iya kai wa zuwa biliyan 15, a 2025.

Kungiyar da ke wayar da kai kan Hawan Jini ta duniya wato, WHL, ta sanya ciwon a cikin jiren cututtukan da ba a iya yada su.

Hakazalika, Kungiyar Gudanar da Bincike da Tsare-Tsare ta duniya kan kula da kiwon lafiya ta duniya, ta sanar da cewa, ciwon na daga cikin larurorin da ke ci gaba da zama kalubale ga rayuwar wadanda suka kamu da shi wanda kuma Nijeriya na daya daga ciki.

Wani abin tausayarwa shi ne, aka shafe shekaru, kan yadda ciwon ke kara yaduwa, wanda  karuwar aka kiyasta ta kai daga kaso 22 zuwa kaso  44, wanda hakan karuwar ta sha ban ban da a yankunan da ke kasar.

Taken taron na bana, yazo ne tamkar kan gaba ga kasar nan, musamman duba irin yanayin abincin da ake ci a gidajen kasar, kusan a shekaru biyu da suka gabata zuwa yanzu.

Bugu da kari, gidaje da dama a kasar, musamman na talakawa, na ci gaba da fuskantan matsin rayuwa ciki har da aukuwar hauhawan farashin kayan abinci, wanda hakan ya kara zafafa talauci da kuma fuskantar matsalolin rashin lafiya.

An dai shafe shekaru, Nijeriya na ci gaba da fuskantar dimbin kalubale na samun kulawar kiwon lafiyar ‘yan kasar yadda ya kamata, da kuma wawagegen gibin da ya auku a tsakanin mazauna Birane da na Karkara, wajen samun ababen more rayuwa da yin inshorar kiwon lafiyar su.

Koda yake dai, an dan samu wasu nasarori, amma duk da haka, wasu kalubalen, na nan kamar yadda suke a wasu guraren, kamar na wahalar samun magunguna kan farashi mai sauki.

Duba da irin halin fatara a kasar, musamman a tsakanin talakawa, magungunan kula da ciwon, na da matukar tsada, hatta magunnan kula da wasu larorin kamar dai,  ciwon Suga, ba kasafai, masu wannan larurar za su iya sayen magungunan ba, har da, kanannan ma’aikatan a kasar, da ke karbar  sabon mafi karancin Albashin ma’aikatan kasar na Naira 70.

Kazalika, tsadar magungunan, wani babban nauyi ne, akasari ga masu larurar wanda hakan ke tilasata su, dai bin ka’idojin da aka gindaya masu, na ci gaba da kula da lafiyarsu.

Wani rahoto ya bayyana cewa, tsadar magungunan ciwon a kasar nan, ya sha ban ban a wasu sassan kasar, misali, ma’aunin da ke yin gwaji ciwon Suga, ya karu, inda farashinta a yanzu, ya kai kimanin daga Naira 30,000 zuwa Naira 6,000.

Hakazalika, Hukumar Inshorar Kiwon Lafiya ta Kasa, na fuskantar karancin masu shiga cikin tsarin Inshora, duba da cewa, kusan kashi biyar a cikin dari na ‘yan kasar ne, kacal, suka shiga cikin tsarin.

Bugu da kari, ana ci gaba da samun karancin wayar da kan alumma kan ciwon, duba da cewa wasu alkaluma a 2021 sun bayyana cewa, kaso 29 na mutanen da aka yiwa gwajin ciwon, inda kuma kaso 12, aka dora su, kan shan magani wanda kuma kaso uku ne kawai, aka ci nasara na dakile ciwon.

Muna goyon bayan tunawa da ranar ciwon na duniya wadda kuma aka mayar da hankali, mai-makon ayi mata magani kawai, hatta da yadda za a kare aukuwarta da kuma karfafawa jama’a Guiwa kan yadda za su kula da lafiyarsu da kuma zuwa yin gwaji, kan lokaci, domin a gano, ko sun kamu da ciwo tare da kuma yin dubi, ga irin nau’in abincin da suke ci.

Ya zama wajibi, a mayar da hankali, wajen wayar da kan alumma, musaman ta hanyar zuwa yin gwajin  kiwon lafiya game da larurar wanda ta hanak ne, kawai za a iya dakile yaduwarta.

Wasu kwararu, sun bayar da shawarar cewa, ya zama wajbi, mutane sun rinka sanin irin abincin da ya kamata su ci, rage yin amfani da Gishiri, motsa jiki rage shan Barasa da kuma daina shan Taba Sigari.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Hawan jiniHigh blood pressure
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gasar Wasanni Ta Kasa Wata Hanya Ce Ta Hada Kan Matasan Nijeriya– Obasanjo

Next Post

Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa

Related

Me Ya Kamata Mai Yaron Ciki Ta Kula Da Shi?
Kiwon Lafiya

Me Ya Kamata Mai Yaron Ciki Ta Kula Da Shi?

9 hours ago
Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su
Kiwon Lafiya

Amfanin ‘Ya’yan Gwanda Da Yadda Ake Sarrafa Su

7 days ago
Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa
Kiwon Lafiya

Yadda Man Bilicin Ke Yi Wa Fatar Mutum Illa

2 weeks ago
Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani
Kiwon Lafiya

Kwararraun Likitocin Tiyata 6 Ne Kacal Suka Rage A Kano – Farfesa Sani

3 weeks ago
Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu
Kiwon Lafiya

Cutar Cholera Ta Ɓarke A Filato, Mutane 4 Sun Mutu

1 month ago
Cutar Mashaƙo Ta Kashe Yara Biyu A Kaduna
Kiwon Lafiya

Cutar Mashaƙo Ta Kashe Yara Biyu A Kaduna

2 months ago
Next Post
Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa

Shekara Biyun Mulki Tinubu: Nasarori Da Matsaloli Da Inda Aka Dosa

LABARAI MASU NASABA

Rundunar PLA Ta Soki Birtaniya Bisa Zuzuta Abun Da Ya Wakana Yayin Da Jirgin Ruwan Sintirinta Ya Keta Ta Zirin Taiwan 

Rundunar PLA Ta Soki Birtaniya Bisa Zuzuta Abun Da Ya Wakana Yayin Da Jirgin Ruwan Sintirinta Ya Keta Ta Zirin Taiwan 

June 20, 2025
Hadin Gwiwa Da Sin Na Bunkasa Zaman Lafiya Da Daidaito A Yankin Kahon Afirka

Hadin Gwiwa Da Sin Na Bunkasa Zaman Lafiya Da Daidaito A Yankin Kahon Afirka

June 20, 2025
Me Ya Kamata Mai Yaron Ciki Ta Kula Da Shi?

Me Ya Kamata Mai Yaron Ciki Ta Kula Da Shi?

June 20, 2025
Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista

Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista

June 20, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)

June 20, 2025
Sin Ta Jadadda Wajibcin Daukar Jerin Matakan Magance Matsalar Talauci Da Karancin Ci Gaba Da Rikici

Sin Ta Jadadda Wajibcin Daukar Jerin Matakan Magance Matsalar Talauci Da Karancin Ci Gaba Da Rikici

June 20, 2025
Jakadan Sin Dake Amurka Ya Yi Jawabi A Gun Liyafar Da Kwamitin Kasa Mai Lura Da Kasuwancin Amurka Da Sin Ya Shirya

Jakadan Sin Dake Amurka Ya Yi Jawabi A Gun Liyafar Da Kwamitin Kasa Mai Lura Da Kasuwancin Amurka Da Sin Ya Shirya

June 20, 2025
Matsayin Sin Na Bude Kofar Tattalin Arzikinta Ga Duniya Ba Zai Canza Ba

Matsayin Sin Na Bude Kofar Tattalin Arzikinta Ga Duniya Ba Zai Canza Ba

June 20, 2025
Zamfara Ta Zama Jiha Ta Farko Da Ta Ƙaddamar da Tsarin Ilimin Fasahar Zamani

Zamfara Ta Zama Jiha Ta Farko Da Ta Ƙaddamar da Tsarin Ilimin Fasahar Zamani

June 20, 2025
An Kafa Fiye Da Kamfanonin Waje 24,000 A Sin Cikin Watanni 5 Na Farkon Bana

An Kafa Fiye Da Kamfanonin Waje 24,000 A Sin Cikin Watanni 5 Na Farkon Bana

June 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.