Wata tankar mai ta fashe kuma ta yi sanadiyar mutuwar mutane 30 a hanyar Agaie-Bida a jihar Neja da safiyar Lahadi.
LEADERSHIP ta tattaro cewa, tankar ta yi karo ne da wata tirela dauke da shanu wacce ta nufi jihar Legas daga Wudil a jihar Kano.
Babban daraktan hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Neja, Mallam Arah, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Cikakken bayanai na tafe…
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp